03
Jul
Daga MAHDI M. MUHAMMAD Majalisar Gudanarwar Jami’ar NOUN ta Nijeriya, ta amince da naɗin sabon magatakarda, shugaban kula da shige da ficen kuɗaɗe da kuma shugaban ɗakin karatu, na wa’adi guda na shekaru biyar. Sabbin waɗanda aka naɗa sune, Oladipo Adetayo Ajayi a matsayin magatakarda, Malam Nasir Gusau Marafa a matsayin shugaban kula da shige da ficen kuɗaɗe da Dakta Angela Ebele Okpala a matsayin shugaban ɗakin karatu na jami’ar. An miƙa naɗin ga waɗanda aka naɗa a wasiƙu daban-daban na ranar 27 ga watan Yuni, 2022, kuma magatakarda mai barin gado, Felix I. Edoka ya sanya wa hannu. Edoka…