Babban Labari

Rufe asusun gwamnatin Osun: Tinubu ya kare dimukraɗiyya a Osun

Rufe asusun gwamnatin Osun: Tinubu ya kare dimukraɗiyya a Osun

*Matakin da kotu da EFCC suka ɗauka gabanin zaɓe ya kunyata ni, cewarsa Daga MAHDI MUSA MUHAMMAD Shugaban Nijeriya, Bola Ahmed Tinubu, ya bayyana cewa, ba komai ake aikatawa a Gwamnatin Tarayya da shi shugaban yake da masaniya kafin yi ba. Don haka ya umarci Hukumar Yaƙi da Masu Yi wa Tattalin Arziki Ta'annati (EFCC) da ta garzaya kotu, domin janye umarnin da ya bai wa hukumar damar rufe asusun bankunan Gwamnatin Jihar Osun tare da dakatar da duk wani matakin shari'a da ta ɗauka kan lamarin. A cikin wata sanarwa da Shugaban ƙasar ya sanya wa hannu da kansa…
Read More
Yilwatda ne Gwarzon Blueprint na 2025

Yilwatda ne Gwarzon Blueprint na 2025

Daga MAHDI MUSA MUHAMMAD Kamfanin jaridun Blueprint da Mahana ya zaɓi Shugaban Jam’iyyar APC na ƙasa, Farfesa Nentawe Goshwe Yilwatda, a matsayin Gwarzon Shekara ta 2025 bisa irin jagorancinsa, gudunmawar da ya bayar wajen bunƙasa dimokuraɗiyya da kuma ƙoƙarinsa na ƙarfafa cibiyoyin siyasa a Nijeriya. Lambar yabon, wadda ita ce mafi girma da kamfanin ke bayarwa a duk shekara, na karrama mutanen da suka taka muhimmiyar rawa wajen ci gaban ƙasa ta fuskar shugabanci, hidimar jama'a da kuma ayyukan raya ƙasa a shekarar da ake dubawa. Daraktan Gudanarwa na Kamfanin Jaridun Blueprint, Salisu Umar, ya ce an zaɓi Farfesa Yilwatda…
Read More
Nijeriya na iya zaɓen tikitin Kirista-Kirista – Gwamna Sule

Nijeriya na iya zaɓen tikitin Kirista-Kirista – Gwamna Sule

Daga MAHDI MUSA MUHAMMAD Gwamnan Jihar Nasarawa, Injiniya Abdullahi Sule, ya bayyana cewa, yana da yaƙinin cewa, wata rana Nijeriya za ta zaɓi shugaban ƙasa da mataimakinsa, waɗanda dukkansu Kiristoci ne, duk da ci gaba da muhawarar da ta biyo bayan matakin Jam’iyyar APC na ci gaba da tsayar da tikitin Musulmi-Musulmi a zaɓen shugaban ƙasa na shekarar 2027. Da yake magana a shirin Politics Today na gidan talbijin na Channels, Sule ya ce Kundin Tsarin Mulkin Nijeriya na 1999 bai tanadi wajabcin daidaita addini a tikitin takarar shugaban ƙasa ba, yana mai jaddada cewa ƙwarewa da kuma bin ƙa’idar…
Read More
’Yan sandan jihohi: An makara wajen sukar shirin – Sulaiman Abba

’Yan sandan jihohi: An makara wajen sukar shirin – Sulaiman Abba

*Tsohon Sufeto Janar ya ce, amma Legas ce kaɗai yake da tabbacin shirya *Har ’yan sandan ƙananan hukumomi ma Nijeriya tana buƙata, inji shi Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Tsohon Sufeto Janar na ’Yan Sandan Nijeriya, Alhaji Suleiman Abba, ya bayyana cewa, a cikin jihohin Nijeriya bakiɗaya, Jihar Legas ce kaɗai yake da tabbacin ta shirya riƙe rundunar ’yan sandan jiha, sai dai ya ƙara da cewa, lokaci ya ƙure da za a ci gaba da bayyana wani ra’ayi na daban kan samar da rundunonin ’yan sandan jihohi a ƙasar, illa dai kawai masu ruwa da tsaki su taimaka…
Read More
Gwamnatin Tinubu ta sauya salon yaƙi da ta’addanci

Gwamnatin Tinubu ta sauya salon yaƙi da ta’addanci

*Ku harbi ’yan ta’adda babu jiran umarninmu – Musa ga dakaru *Ya ce, za a ɗauki sojan da ya jira umarnin harbi tamkar ɗan ta’adda *Majalisa ta nemi dakatar da shirin gyaran halin ’yan ta’adda *Kwamandojin ISWAP shida da iyalansu sun miƙa wuya a Borno Daga MAHDI MUSA MUHAMMAD Ministan Tsaro, Janar Christopher Musa (mai ritaya), ya umarci dakarun Rundunar Sojin Nijeriya da sauran hukumomin tsaro su riƙa ɗaukar mataki kai tsaye kan duk wani ɗan bindiga ko ɗan ta’adda da suka ci karo da shi, yana mai gargaɗin cewa duk jami’in da ya ƙi buɗe wuta saboda jiran umarni…
Read More
Babbar badaƙala: Gwamnati ta fallasa hukumar bogi

Babbar badaƙala: Gwamnati ta fallasa hukumar bogi

*Har an saka ta a kasafin kuɗin Gwamnatin Tarayya Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja  Fadar Shugaban ƙasar Nijeriya ta bayyana cikakken bayani kan yadda wani mutum mai suna Adeniyi Adeyemi Matthew ya ƙirƙiri wata hukumar gwamnatin tarayya ta bogi, ya buɗe ofis a Sakatariyar Tarayya da ke Abuja, tare da gabatar da kansa a matsayin Darakta Janar domin gudanar da ayyukan da ba su da sahalewar gwamnati. A cikin wata sanarwa da Mai Bai wa Shugaban ƙasa Shawara kan Yaɗa Labarai da Dabarun Aiki, Mista Bayo Onanuga, ya fitar, ya ce babu wata hukuma mai suna Presidential Foreign Intervention…
Read More
Ƙudirin dokar ’yan sandan jihohi: Muhimman abubuwan da Majalisar Dattawa ta amincewa

Ƙudirin dokar ’yan sandan jihohi: Muhimman abubuwan da Majalisar Dattawa ta amincewa

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Majalisar Dattawan Nijeriya ta amince da ƙudirin dokar kafa Rundunar ’Yan Sandan Jihohi bayan karatu na uku a wani gagarumin mataki da ake ganin zai sauya tsarin tsaron ƙasa tare da ba wa jihohi damar taka rawar gani wajen kare rayuka da dukiyoyin al’umma. ƙudirin dokar, wanda Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya aike wa Majalisar Dattawa ranar Talata, ya samu amincewa ne a zaman majalisar na ranar Laraba bayan doguwar muhawara da nazari kan gyaran Kundin Tsarin Mulkin Nijeriya da ake buƙata domin tabbatar da aiwatar da sabon tsarin. Amincewar da majalisar ta bayar…
Read More
Fetur da sadarwa: Gwamnatin Tinubu ta yi alƙawarin ƙin ƙara haraji

Fetur da sadarwa: Gwamnatin Tinubu ta yi alƙawarin ƙin ƙara haraji

A daina biye wa jita-jita, inji Ma’aikatar Kuɗi Daga MAHDI MUSA MUHAMMAD Gwamnatin Tarayyar Nijeriya ta yi watsi da rahotannin da ke iƙirarin cewa, tana shirin ƙaƙaba sabbin haraji kan harkokin sadarwa da kayayyakin man fetur, bayan fitar da sabon rahoton tuntuɓar tattalin arziki na Asusun Lamuni na Duniya (IMF) kan Nijeriya. Gwamnatin ta bayyana irin waɗannan rahotanni a matsayin kuskuren fassara abubuwan da ke cikin rahoton, tana mai jaddada cewa ba sa wakiltar manufofinta ko alƙiblarta ta fuskar tattalin arziki. Ta kuma tabbatar wa da ’yan ƙasaR cewa, duk wani matakin haraji da za a ɗauka nan gaba za…
Read More
Hausawan Jos ’yan ƙasa ne, inji kotu

Hausawan Jos ’yan ƙasa ne, inji kotu

Daga MAHDI MUSA MUHAMMAD Babbar Kotun Jihar Filato mai lamba ta 17 ta yanke hukuncin cewa, duk wani Bahaushe da aka haifa kuma ya taso a ƙaramar Hukumar Jos ta Arewa yana da cikakken haƙƙin a ɗauke shi a matsayin ɗan asalin yankin. Alƙali C. Donglong ne ya yanke hukuncin yayin da yake yanke hukunci a ƙarar da Fatima Baba Akawu da Baba Alhaji Akawu suka shigar a gaban kotun kan ƙin ba Fatima takardar shaidar asali (Certificate of Indigene) daga ƙaramar Hukumar Jos ta Arewa. Masu ƙarar sun nemi kotun ta tantance ko Fatima Baba Akawu, wadda aka haifa…
Read More
Faɗan daba ya zama ‘gida-gida’ a Kano

Faɗan daba ya zama ‘gida-gida’ a Kano

Yadda al'amura suka dagule a unguwar Nasarawa Daga MAHDI MUSA MUHAMMAD A baya-bayan nan, ayyuykan daba sun sun mamaye lungu da saƙo na birnin Kano, Babban Birnin Jihar Kano, inda aka fara jin al’ummar jihar, musamman malamai, suna hawa munbari suna kiraye-kiraye kan batun. A baya an fi samun rikicin a unguwannin talakawan birin kamar ɗorayi, Rijiyar Lemo, Birged, Fagge, ƙofar Nasarawa da dai makamantansu sun yi ƙaurin suna wajen guje-guje, saboda yadda ’yan daba kan faɗa wa mutane babu gaira babu dalili baya ga kashe mutane ta hanyar ƙwacen waya da ya yi ƙaurin suna. Bugu da ƙari, al’ummar…
Read More