14
Mar
Daga MAHDI MUSA MUHAMMAD Majalisar Wakilan Nijeriya ta amince da sabon ƙudirin dokar sake fasalin haraji a ƙasar guda huɗu da Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya gabatar a baya-bayan nan, yayin da ta yi nazari tare da amincewa da rahoton kwamitinta na musamman kan shawarwarin a ranar Alhamis 13 ga Maris, 2025. ƙudirorin sun haɗa da Dokar Samar da Kima, Tattarawa da kuma ƙididdigar Kuɗi don Tara Kuɗi ga Tarayya, Jihohi da ƙananan Hukumomi; Bayar da Iko da Ayyukan hukumomin haraji, da kuma abubuwan da ke da alaƙa da su, da kuma daftarin dokar da za ta soke Dokar Tattalin…