Babban Labari

Gwamnatin Tinubu ta sauya salon yaƙi da ta’addanci

Gwamnatin Tinubu ta sauya salon yaƙi da ta’addanci

*Ku harbi ’yan ta’adda babu jiran umarninmu – Musa ga dakaru *Ya ce, za a ɗauki sojan da ya jira umarnin harbi tamkar ɗan ta’adda *Majalisa ta nemi dakatar da shirin gyaran halin ’yan ta’adda *Kwamandojin ISWAP shida da iyalansu sun miƙa wuya a Borno Daga MAHDI MUSA MUHAMMAD Ministan Tsaro, Janar Christopher Musa (mai ritaya), ya umarci dakarun Rundunar Sojin Nijeriya da sauran hukumomin tsaro su riƙa ɗaukar mataki kai tsaye kan duk wani ɗan bindiga ko ɗan ta’adda da suka ci karo da shi, yana mai gargaɗin cewa duk jami’in da ya ƙi buɗe wuta saboda jiran umarni…
Read More
Babbar badaƙala: Gwamnati ta fallasa hukumar bogi

Babbar badaƙala: Gwamnati ta fallasa hukumar bogi

*Har an saka ta a kasafin kuɗin Gwamnatin Tarayya Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja  Fadar Shugaban ƙasar Nijeriya ta bayyana cikakken bayani kan yadda wani mutum mai suna Adeniyi Adeyemi Matthew ya ƙirƙiri wata hukumar gwamnatin tarayya ta bogi, ya buɗe ofis a Sakatariyar Tarayya da ke Abuja, tare da gabatar da kansa a matsayin Darakta Janar domin gudanar da ayyukan da ba su da sahalewar gwamnati. A cikin wata sanarwa da Mai Bai wa Shugaban ƙasa Shawara kan Yaɗa Labarai da Dabarun Aiki, Mista Bayo Onanuga, ya fitar, ya ce babu wata hukuma mai suna Presidential Foreign Intervention…
Read More
Ƙudirin dokar ’yan sandan jihohi: Muhimman abubuwan da Majalisar Dattawa ta amincewa

Ƙudirin dokar ’yan sandan jihohi: Muhimman abubuwan da Majalisar Dattawa ta amincewa

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Majalisar Dattawan Nijeriya ta amince da ƙudirin dokar kafa Rundunar ’Yan Sandan Jihohi bayan karatu na uku a wani gagarumin mataki da ake ganin zai sauya tsarin tsaron ƙasa tare da ba wa jihohi damar taka rawar gani wajen kare rayuka da dukiyoyin al’umma. ƙudirin dokar, wanda Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya aike wa Majalisar Dattawa ranar Talata, ya samu amincewa ne a zaman majalisar na ranar Laraba bayan doguwar muhawara da nazari kan gyaran Kundin Tsarin Mulkin Nijeriya da ake buƙata domin tabbatar da aiwatar da sabon tsarin. Amincewar da majalisar ta bayar…
Read More
Fetur da sadarwa: Gwamnatin Tinubu ta yi alƙawarin ƙin ƙara haraji

Fetur da sadarwa: Gwamnatin Tinubu ta yi alƙawarin ƙin ƙara haraji

A daina biye wa jita-jita, inji Ma’aikatar Kuɗi Daga MAHDI MUSA MUHAMMAD Gwamnatin Tarayyar Nijeriya ta yi watsi da rahotannin da ke iƙirarin cewa, tana shirin ƙaƙaba sabbin haraji kan harkokin sadarwa da kayayyakin man fetur, bayan fitar da sabon rahoton tuntuɓar tattalin arziki na Asusun Lamuni na Duniya (IMF) kan Nijeriya. Gwamnatin ta bayyana irin waɗannan rahotanni a matsayin kuskuren fassara abubuwan da ke cikin rahoton, tana mai jaddada cewa ba sa wakiltar manufofinta ko alƙiblarta ta fuskar tattalin arziki. Ta kuma tabbatar wa da ’yan ƙasaR cewa, duk wani matakin haraji da za a ɗauka nan gaba za…
Read More
Hausawan Jos ’yan ƙasa ne, inji kotu

Hausawan Jos ’yan ƙasa ne, inji kotu

Daga MAHDI MUSA MUHAMMAD Babbar Kotun Jihar Filato mai lamba ta 17 ta yanke hukuncin cewa, duk wani Bahaushe da aka haifa kuma ya taso a ƙaramar Hukumar Jos ta Arewa yana da cikakken haƙƙin a ɗauke shi a matsayin ɗan asalin yankin. Alƙali C. Donglong ne ya yanke hukuncin yayin da yake yanke hukunci a ƙarar da Fatima Baba Akawu da Baba Alhaji Akawu suka shigar a gaban kotun kan ƙin ba Fatima takardar shaidar asali (Certificate of Indigene) daga ƙaramar Hukumar Jos ta Arewa. Masu ƙarar sun nemi kotun ta tantance ko Fatima Baba Akawu, wadda aka haifa…
Read More
Faɗan daba ya zama ‘gida-gida’ a Kano

Faɗan daba ya zama ‘gida-gida’ a Kano

Yadda al'amura suka dagule a unguwar Nasarawa Daga MAHDI MUSA MUHAMMAD A baya-bayan nan, ayyuykan daba sun sun mamaye lungu da saƙo na birnin Kano, Babban Birnin Jihar Kano, inda aka fara jin al’ummar jihar, musamman malamai, suna hawa munbari suna kiraye-kiraye kan batun. A baya an fi samun rikicin a unguwannin talakawan birin kamar ɗorayi, Rijiyar Lemo, Birged, Fagge, ƙofar Nasarawa da dai makamantansu sun yi ƙaurin suna wajen guje-guje, saboda yadda ’yan daba kan faɗa wa mutane babu gaira babu dalili baya ga kashe mutane ta hanyar ƙwacen waya da ya yi ƙaurin suna. Bugu da ƙari, al’ummar…
Read More
Zaɓen fidda gwanin ADC: Magoya bayan El-Rufai na zargin an yaudare su

Zaɓen fidda gwanin ADC: Magoya bayan El-Rufai na zargin an yaudare su

Daga MAHDI MUSA MUHAMMAD Rikicin cikin gida na ci gaba da ƙamari a jam’iyyar ADC reshen Jihar Kaduna, yayin da wasu daga cikin magoya bayan tsohon gwamnan jihar, Nasir El-Rufai, ke zargin sa da yin watsi da tsarin siyasar da ya tsaya masa tsayin daka tsawon shekaru. Abin da ya fara a matsayin saɓani kan zaɓen fidda gwani na kujerar gwamna da na ’yan majalisa yanzu ya rikiɗe zuwa babbar ɓaraka a cikin jam’iyyar, inda masu biyayya ga El-Rufai ke zargin cewa an yi watsi da biyayyarsu da sadaukarwar da suka yi ta hanyar yarjejeniyoyin sirri da kuma amfani da…
Read More
Zaɓukan APC: Wasu sun dara, wasu sun koka

Zaɓukan APC: Wasu sun dara, wasu sun koka

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Zaɓukan fidda gwani na Jam’iyyar ‘All Progressiɓes Congress’ (APC) da aka gudanar a sassa daban-daban na Niijeriya sun bar baya da ƙura, rikice-rikice, koke-koke, zarge-zargen maguɗi da murnar nasara daga ɓangarori mabambanta, yayin da jam’iyyar ke ƙoƙarin tsara dabarun tunkarar babban zaɓen shekarar 2027. Yayin da wasu manyan jiga-jigan jam’iyyar suka samu tikitin takara cikin farin ciki da gagarumar nasara, wasu kuwa sun bayyana zaɓukan a matsayin “wasan kwaikwayo” da aka shirya domin fifita wasu ‘yan takara, lamarin da ya haddasa zanga-zanga da kuma barazanar ɗaukaka ƙorafe-ƙorafe zuwa matakin ƙasa. A wasu jihohi, an…
Read More
ACI: Rikicin ACF abin kunya ne ga Arewa

ACI: Rikicin ACF abin kunya ne ga Arewa

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja  Kungiyar haɗin kan arewacin Nijeriya da zaman lafiya da bunƙasa, wato Arewa Cohesion for Peace, Unity and Development Initiative (ACI) ta nuna rashin jin daɗinta kan rikicin shugabanci da ke addabar ƙungiyar Tuntuba ta Arewa (ACF), tana mai bayyana lamarin a matsayin abin kunya da ya jefa Arewacin Nijeriya cikin ba’a da raini a idon jama’a. A cikin wata sanarwa da Darakta Janar na ƙungiyar, Dr. Abdullahi Idris, ya aikewa da manema labarai, ACI ta bayyana damuwarta kan yadda rikice-rikice, zarge-zarge da rarrabuwar kai suka yi ƙamari a cikin ACF. Kungiyar ta ce rikicin…
Read More
ACF ta afka rikici kan biliyoyin Naira

ACF ta afka rikici kan biliyoyin Naira

*An dakatar da Shugaban Kwamitin Amintattu Daga MAHDI MUSA MUHAMMAD Kwamitin Zartarwa na ƙasa na ƙungiyar Tuntuɓa ta Arewa (ACF) ya dakatar da Shugaban Kwamitin Amintattu na ƙungiyar, Alhaji Bashir M. Dalhatu, bisa zargin almundahanar kuɗi da take ƙa’idojin kundin tsarin mulki, a wani mataki mai tsauri da ya ƙara ruruta rikicin shugabanci a cikin ƙungiyar. An yanke wannan hukunci ne a wani taron gaggawa na NEC da aka gudanar a Kaduna a ranar Laraba, a daidai lokacin da ake taƙaddama kan rahotannin hana shiga hedikwatar ACF da ‘yan sanda suka yi gabanin tarurrukan da aka shirya gudanarwa. Yayin da…
Read More