Babban Labari

An shiga ruɗani game da hukuncin kotu kan shari’ar zaɓen Gwamnan Kaduna

An shiga ruɗani game da hukuncin kotu kan shari’ar zaɓen Gwamnan Kaduna

Jama'a sun shiga halin ruɗani game da shari'ar zaɓen gwamna a jihar Kaduna. Hakan ya faru ne bayan da wani rahoto ya nuna Kotun Sauraren Ƙararrakin Zaɓe na Gwamnan Jihar ta ayyana zaɓen a matsayin wanda bai kammala ba. Bayan kimanin awa guda da fitan rahoton, sai aka sake ganin wani rahoto na daban na cewa, kotun ta tabbatar da nasarar da Gwamna Uba Sani ya samu a zaɓen wanda hakan ke nuni da shi ne zaɓaɓɓen gwamnan jihar. Da yake yi wa Jaridar News Point Nigeria ƙarin haske game da hukuncin ta waya, lauyan Gwamna Sani, Ibrahim H O…
Read More
Da Ɗumi-ɗumi: Kotu ta ayyana zaɓen gwamnan Kaduna ‘Inconclusive’

Da Ɗumi-ɗumi: Kotu ta ayyana zaɓen gwamnan Kaduna ‘Inconclusive’

Kotun Sauraren Ƙararrakin Zaɓen Gwamnan Jihar Kaduna, ta ayyana zaɓen gwamnan jihar da ya gudana ran 18 ga Maris a matsayin wanda bai kammala ba, wato 'inconclusive.' Kotun ta ayyana hakan ne a zaman yanke hukunci kan shari'ar da ta yi a ranar Alhamis. Kotun, ƙarƙashin jagorancin Mai Shari'a Victor Oviawe ta bai wa Hukumar Zaɓe ta Ƙasa INEC, da ta gudanar da zaɓen cike giɓi a cikin kwana 90. Da wannan hukuncin, ana sa ran INEC ta sake shirya zaɓe a gundumomi bakwai a tsakanin ƙananan hukumomi huɗu kuma a rumfunan zaɓe 24 masu ɗauke da masu kaɗa ƙuri'a…
Read More
Masu garkuwa sun ɗauki salon ɗauki-ɗaiɗai a Kebbi 

Masu garkuwa sun ɗauki salon ɗauki-ɗaiɗai a Kebbi 

Daga JAMIL GULMA a Kebbi  Masu garkuwa da mutane sun ɗauki sabon salo a waɗansu sassan Jihar Kebbi, inda yanzu a maimakon kai hari da suke yi a baya a cikin ayarin babura masu yawa, sun ɗauki salon ɗauki-ɗaiɗai, inda suke shiga cikin gari da tsakar dare su ɗauki mutum ɗaya ko biyu zuwa biyar maimakon ayarin mutane. Yankin ƙananan hukumomin Koko/Besse, Bagudo da Maiyama dai yanzu a nan ne waɗannan mutanen ke cin karensu ba babbaka duk da irin ƙoƙarin da hukumomin tsaro da ’yan sa-kai ke yi. A cikin daren ranar Larabar da ta gabata waɗannan mutanen sun…
Read More
Da Ɗumi-ɗumi: Kotu ta ce Yusuf Gawuna ne zaɓaɓɓen Gwamnan Kano

Da Ɗumi-ɗumi: Kotu ta ce Yusuf Gawuna ne zaɓaɓɓen Gwamnan Kano

Kotun Sauraren Ƙararrakin Zaɓen Gwamna a Kano, ta tsige Gwamna Abba Kabir Yusuf na Jam'iyyar NNPP sannan ta ayyana Yusuf Gawuna na Jam'iyyar APC a matsayin wanda ya lashe zaɓen gwamnan jihar da aka guda a ranar 18 ga Maris. Bayan kammala zaɓe Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC) ta ayyana Yusuf Kabir a matsayin wanda ya lashe zaɓen. Yayin da ɗan takarar APC, Nasir Gawuna, ya taya Kabir ɗin murnar lashe zaɓen ita kuwa jam'iyyarsa ta APC garzayawa kotu ta yi don ƙalubalantar sakamakon zaɓen. Yayin zaman yanke hukuncin da kotun ta yi a ranar Laraba, alƙalan kotun sun ba…
Read More
Yadda babban layin lantarki ya jefa Nijeriya duhu

Yadda babban layin lantarki ya jefa Nijeriya duhu

*Minista ya yi ƙarin haske*Wannan ne duhun-duhununa na farko a mulkin Tinubu Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Ministan Wutar Lantarki na Tarayyar Nijeriya, Adebayo Adelabu ya ce an samu fashewar wani abu da ya kai ga ɓarkewar gobara a tashar wuta ta Kainji/Jebba da ke yankin Arewa ta Tsakiyar Nijeriya. Adelabu a cikin jerin saƙon a dandalin sadarwa na X a jiya Alhamis ya ce, da ƙarfe 04:35 na asubahin Alhamis an ji tashin gobara tare da ƙarar fashewar abubuwa a layin Kainji/Jebba mai qarfin 330KV Line 2 (Cct K2J) Blue Phase CVT da Blue Phase Line Isolator na…
Read More
Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu ya naɗa Yemi Cardoso Gwamnan CBN

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu ya naɗa Yemi Cardoso Gwamnan CBN

Shugaban Ƙasa Bola Tinubu ya amince da a naɗa Dr. Olayemi Michael Cardoso a matsayin sabon Gwamnan Babban Bankin Nijeriya (CBN), na wa'adin shekara biyar ya zuwa lokacin Majalisar Dattawa za ta tabbatar da naɗin nasa. Bayanin haka na ƙunshe ne cikin sanarwar da ta fito ta bakin mai magana da yawun Shugaban Ƙasa, Ajuri Ngelale, a ranar Juma'a. Sanarwar ta ce naɗin ya yi daidai da Sashe na 8 (1) na Dokar Babban Bankin Nijeriya na 2007, wanda ya sahale wa Shugaban Ƙasa ikon naɗa Gwamnan CBN da mataimaka huɗu gabanin Majalisar Tarayya ta tabbatar da naɗinsu. Kazalika, Bola…
Read More
Bayan kotu ta tabbatar da nasarar zaɓen Tinubu…

Bayan kotu ta tabbatar da nasarar zaɓen Tinubu…

*Atiku da Obi za su cigaba da yaƙin*Tinubu ya yi maraba da hukuncin*Buhari ya tsomo baki*Tinubu ya nuna gwanintar mulki a kwana 100 – Ministan Labarai Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Kotun Sauraron Ƙararrakin Zaɓen Shugaban Ƙasa ta tabbatar da nasarar Zaɓen Shugaba Bola Ahmed Tinubu. Shugaban kotun, Mai shari'a Haruna Tsammani ya ce matakin hukumar Zaɓe na ayyana Bola Tinubu, a matsayin wanda ya lashe zaɓen 25 ga watan Fabrairu, ya dace. Matakin na zuwa ne bayan kotun ta kori ƙarar ɗan takarar shugaban ƙasa na babbar jam'iyyar adawar Nijeriya, Atiku Abubakar da maraicen Laraba. Shi, da Peter…
Read More
Kotu ta kori ƙarar su Atiku kan Tinubu

Kotu ta kori ƙarar su Atiku kan Tinubu

Kotun Sauraren Ƙararrakin Zaɓe mai zamanta a Abuja ta kori ƙarar da Jam'iyyar PDP da ɗan takararta na shugabancin ƙasa, Atiku Abubakar suka shigar inda suke ƙalubalantar nasarar da Shugaba Bola Tinubu ya samu a babban zaɓen da ya gabata. Kotu ta yi watsi da ƙarar ne a zaman shari'a da ta yi ranar Laraba. Yayin zamanta, kotun ta soke wasu sakin layi a ƙorafin da aka shigar da suke nuni da Shugaba Bola Tinubu bai cancanci shiga zaɓen da ya gudana ranar 25 ga Fabrairun da ya gabata ba. Ta ce masu ƙarar sun gagara gabatar wa kotun cancantar…
Read More
Kotu ta tsayar da ranar yanke hukunci kan shari’ar zaɓen shugaban ƙasa

Kotu ta tsayar da ranar yanke hukunci kan shari’ar zaɓen shugaban ƙasa

Ya zuwa ranar 6 ga Satumban 2023 idan Allah Ya kai mu, Kotun Sauraron Ƙararrakin Zaɓen Shugaban Ƙasa (PEPT) za ta yanke hukunci game da ƙararrakin zaɓen shugabancin ƙasa da ke gabanta. Rajistaran Kotun Ɗaukaka Ƙara, Umar Bangari ne ya tabbatar da hakan a wani shiri da tashar Channels Television ta yi da shi ranar Litinin. Ya ce, “Kotun Ɗaukaka Ƙara na sanar da al'umma cewar za ta yanke hukunci a kan ƙararrrakin zaɓen Shugaban Ƙasa ya zuwa ranar Laraba, 6 ga Satumba 2023." Ƙararrakin sun haɗa ƙara mai lamba "CA/PEPC/03/2023 tsakanin Mr. Peter Gregory Obi & Anor da Hukumar…
Read More
Juyin mulkin Gabon ya kaɗa hantar shugabannin Afrika

Juyin mulkin Gabon ya kaɗa hantar shugabannin Afrika

•Ba za mu amince da halayyar sojoji ba, inji Shugaban Nijeriya*Shugabannin Kamaru da Rwanda sun sauke manyan hafsoshinsu*Ka daure ka koma Nijar – Tinubu ya roqi Sarkin Musulmi*Hamɓararren Shugaban Gabon ya nemi agaji Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Daga dukkan alamu hamvarar da gwamnatin Ƙasar Gabon ya ɗaga hankalin wasu shugabannin Afrika bisa la’akari da yadda suke ɗaukar matakai daban-daban wajen ganin sun daƙile afkuwar hakan a ƙasashensu, inda ake ganin lamarin a matsayin kaɗuwar hanta. A shekaranjiya Laraba, 30 ga Agusta, 2023, ne sojoji suka hamɓarar da gwamnatin Ƙasar Gabon, makonni bayan kiki-kakar da ake yi da sojojin…
Read More