Babban Labari

Majalisar Wakilai ta amince da sabon ƙudirin haraji

Majalisar Wakilai ta amince da sabon ƙudirin haraji

Daga MAHDI MUSA MUHAMMAD Majalisar Wakilan Nijeriya ta amince da sabon ƙudirin dokar sake fasalin haraji a ƙasar guda huɗu da Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya gabatar a baya-bayan nan, yayin da ta yi nazari tare da amincewa da rahoton kwamitinta na musamman kan shawarwarin a ranar Alhamis 13 ga Maris, 2025. ƙudirorin sun haɗa da Dokar Samar da Kima, Tattarawa da kuma ƙididdigar Kuɗi don Tara Kuɗi ga Tarayya, Jihohi da ƙananan Hukumomi; Bayar da Iko da Ayyukan hukumomin haraji, da kuma abubuwan da ke da alaƙa da su, da kuma daftarin dokar da za ta soke Dokar Tattalin…
Read More
Ɗanjuma da Ɗanjummai? Rikicin Akpabio da Natasha ya janyo ayar tambaya

Ɗanjuma da Ɗanjummai? Rikicin Akpabio da Natasha ya janyo ayar tambaya

*Majalisar Dattawa ta dakatar da Sanata Natasha bayan da ta sake shigar da ƙorafinta Daga MAHDI MUSA MUHAMMAD Biyo bayan tashin saɓani tsakanin Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Godswill Akpabio, da Sanata Mai Wakiltar Kogi ta Tsakiya, Sanata Natasha Akpoti Uduaghan, inda suka zargi juna da aikata abubuwan da ba su dace ba, binciken tarihi ya nuna cewa, akwai ayar tambaya akansu bisa la’akari da abubuwan da suka gabata a baya. Ta zarge shi da neman yin lalata da ita, yayin da shi kuma ya zarge ta sharara ƙarya, zarge-zargen da dukkaninsu ba su da tabbas, idan aka yi la’akari da…
Read More
Tura ta kai bango: Fusatattun matasa sun kashe ’yan bindinga a Katsina

Tura ta kai bango: Fusatattun matasa sun kashe ’yan bindinga a Katsina

An ninka alawus ɗin sojojin da ke bakin daga Daga UMAR GARBA a Katsina da SANI AHMAD GIWA a Abuja Mazauna garin Tafoki da ke yankin ƙaramar Hukumar Faskari a Jihar Katsina sun yunƙura, inda suka kashe wasu ’yan bindiga da ke kai hare-hare a yankin. Da fari jami'an tsaron haɗin gwiwa da suke sintiri a yankin ne suka tunkari 'yan bindingar a ƙoƙarinsu na daƙile wani harin ɓarayin dajin. Bayan fafatawa tsakanin ɓangarorin biyu, jami'an tsaron sun samu nasarar daƙile harin 'yan bindingar a yayin da wasu daga cikin ɓarayin suka tsere zuwa daji, wasu kuma sun samu munanan raunukan…
Read More
Janar Oluyede ga sojoji:Ku gama da Bello Turji cikin kwana 30

Janar Oluyede ga sojoji:Ku gama da Bello Turji cikin kwana 30

Daga SANUSI MUHAMMAD a Gusau  Babban Hafsan Sojin ƙasan Nijeriya, Laftanar Janar Olufemi Oluyede, ya bayar da umarni mai ƙarfi ga dakarun haɗin gwiwa na Operations Fansan Yamma da ke yankin Arewa maso Yamma da su ƙara zage damtse da nufin kawo ƙarshen fitaccen jagoran ɗan bindigar nan, Bello Turji, a raye ko a mace nan da kwanaki 30 masu zuwa. Laftanar Janar Oluyede ya bayar da umarnin ne a lokacin da ya ke jawabi ga dakarun Operation Fansan Yamma a hedikwatar runduna ta ɗaya da ke Gusau a lokacin da ya ziyarci Jihar Zamfara jiya Alhamis. A cewarsa, umarnin…
Read More
Majalisar Wakilai ta tsaida ranar tunawa da Janar Murtala

Majalisar Wakilai ta tsaida ranar tunawa da Janar Murtala

Ta kafa sababbin kwamitoci da yin sauye-sauyen wasu Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Majalisar Wakilai ta Nijeriya a ranar Alhamis ta karrama tsohon shugaban mulkin soja na Nijeriya, Marigayi Janar Murtala Ramat Muhammed.  Shugaban Majalisar, Rt. Hon. Abbas Tajudeen, ya bayyana cewa, daga yanzu, majalisar za ta riƙa biki duk ranar 13 ga Fabrairu a matsayin Ranar Murtala Muhammed, don tunawa da marigayi tsohon shugaban ƙasar. A yayin zaman na jiya Alhamis, Majalisar wakilai ta yi shiru na minti guda, domin girmama shi, kamar yadda Blueprint Manhaja ta ruwaito.  Marigayi Murtala Muhammed ya shugabanci Nijeriya daga 1975 zuwa 1976,…
Read More
Majalisar Wakilai za ta ƙirƙiro sabbin jihohi 31

Majalisar Wakilai za ta ƙirƙiro sabbin jihohi 31

Kudu maso Yamma ya samu kaso mafi yawa Daga MAHDI MUSA MUHAMMAD Kwamitin Sake Nazarin Kundin Tsarin Mulkin Nijeriya na amajalisar Wakilai ya bayar da shawarar ƙirƙirar ƙarin sababbin jihohi 31 a ƙasar. Mataimakin kakakin majalisar wakilan aasar, Hon.Benjamin Kalu ne ya bayyana haka lokacin da ya karanto wasiƙar kwamitin, a zaman majalisar da ya jagoranta a ranar Alhamis. Idan aka amince da buƙatar adadin jihohin Nijeriya zai kai 67. Ga jerin sabbin jihohin da kwamitin ya bayar da shawarar ƙirƙira daga wasu jihohin ƙasar na yanzu: Arewa ta Tsakiya – Benue Ala daga jihar Benuwai, Okun daga jihar Kogi,…
Read More
Dala Biliyan 29: Mata za su jagoranci farfaɗo da Afrika – Shettima

Dala Biliyan 29: Mata za su jagoranci farfaɗo da Afrika – Shettima

Ya ƙaddamar da shirin #SheIsIncluded don cike giɓin jinsi a fannin kuɗi da tattali Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja A wani mataki na inganta daidaito tsakanin jinsi da ƙarfafa tattalin arzikin mata, Mataimakin Shugaban Nijeriya, Kashim Shettima, ya bayyana cewa, mata za su kasance a sahun gaba wajen sauye-sauyen bunƙasa tattalin arzikin Afirka da aka yi hasashen za a kashe Dalar Amurka tiriliyan 29. Ya bayyana ƙwaƙƙwaran yaƙinin cewa, haɗa jinsi ba wai alfarma ba ce kawai, amma ginshiƙi ne na ajandar ci gaban Nijeriya. Sanata Shettima ya bayyana hakan ne jiya Alhamis a Abuja lokacin da ya buɗe…
Read More
Yadda gobarar tankokin fetur suka ci rayuka

Yadda gobarar tankokin fetur suka ci rayuka

Yadda gobarar Dikko Junction ta maimaita tarihi a Nijeriya Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Hatsarin wata motar tankar dakon man fetur akan hanyar Abuja, Babban Birnin Nijeriya, zuwa Kaduna ya haifar da asarar rayuka sama da 80, yayin da wasu da dama suka samu rauni. Wannan na zuwa ne ƙasa da shekara ɗaya bayan samun irin wannan hatsari a Jihar Jigawa da ke yankin Arewa maso Yammacin ƙasar, wanda shi kuma ya kashe kusan mutum 200. Irin waɗannan haɗurra na neman zama ruwan dare a Nijeriya duk kuwa da gargaɗin da hukumomi da ɗaiɗaikun mutane ke ta yi. Ana…
Read More
Dalilin ƙaruwar hare-hare a Nijeriya – Hedikwatar tsaro

Dalilin ƙaruwar hare-hare a Nijeriya – Hedikwatar tsaro

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja  Hedikwatar Tsaro ta Nijeriya ta bayyana dalilan da suka saka aka samu ƙarin hare-hare a Nijeriya. Cikin makonnin da suka gabata dai a Nijeriya, an ga yadda Boko Haram da kuma 'yan fashin daji suka ƙara ƙaimi wajen kai hare-hare a wasu sassan ƙasar. Lamarin da ya bar al'ummar ƙasar cikin taraddadi kan dalilin faruwar hakan. Mayaƙan Boko Haram sun kai hare-hare a jihar Borno, waɗanda ya zuwa yanzu ba a kammala tantance ɓarnar da hakan ya haifar ba. Duk kuwa da cewa rundunar sojin Nijeriya ta bayyana cewa jami'anta shida ne aka kashe…
Read More
Cutar HMPV: Yanzu Nijeriya ba ta fuskantar mummunar barazana – NCDC

Cutar HMPV: Yanzu Nijeriya ba ta fuskantar mummunar barazana – NCDC

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Cibiyar Kula da Cututtuka Masu Yaɗuwa ta Nijeriya (NCDC) ta ce, ƙasar ba ta cikin yanayi na fuskantar “mummunar barazana a yanzu” na vullar sabuwar cutar nan ta ‘Human Metapneumovirus’ (HMPV). Yayin da ake nuna damuwa kan vullar cutar a wasu sassan duniya, Hukumar NCDC ta tabbatar wa ’yan Nijeriya cewa, ƙasar na cikin ƙoshin lafiya kuma babu wani abin fargaba. “Bari na ce, babu wata babbar barazana a yanzu. ɗaya kenan. Na biyu, wannan cutar ta HMPV, ba sabuwar cuta ba ce. Kawai dai ba a san ta ba. "Amma yana da tasiri…
Read More