Babban Labari

‘Yan binga sun sace mutum 61 a wani sabon hari a Kaduna

‘Yan binga sun sace mutum 61 a wani sabon hari a Kaduna

Daga BASHIR ISAH Rahotanni daga jihar Kaduna sun ce aƙalla mutum 61 wasu da ake zargin 'yan fashin daji ne suka yi garkuwa da su a yankin Buda da ke cikin Ƙaramar Hukumar Kajuru a jihar. Duk da dai babu bayani a hukumance ka aukuwar harin, sai dai wani mazaunin yankin ya shaida wa majiyarmu ranar Talata cewar, maharan sun dira ƙauyen ne da misalin ƙarfe 11:45 na dare inda suka yi awon gaba da mutum 61. A cewar Dauda Kajuru wanda mazaunin yankin ne, 'yan bindigar shiga yankin da yawansu, kuma sun harba bindiga. Ta bakinsa, “abin da ya…
Read More
Yanzu-yanzu: Majalisar Dattawa ta dakatar da Ningi na wata uku kan zargin cushen kasafi

Yanzu-yanzu: Majalisar Dattawa ta dakatar da Ningi na wata uku kan zargin cushen kasafi

Majailisar Dattawa ƙarƙashin jagorancin Sanata Godswill Akpabio, ta dakatar da Sanata Abdul Ningi na tsawon wata uku daga majalisar. Manlisar ta ɗauki wannan mataki ne yayin zaman da ta yi ranar Talata, kuma ta dakatar da Ningi ne bayan da ya yi zargin an yi cushe na Naira tiriliyan 3.7 cikin Kasafin 2024. A wata hira da BBC Hausa ta yi da ɗan majalisar mai wakiltar Bauchi ta Tsakiya kwanan nan, aka ji shi ya ce haƙiƙanin kasadin 2024 da aka gabatar Tiriliyan 25 amma ba Tiriliyan 28 da ake amfani da shi a halin yanzu ba. Ya ce bayan…
Read More
Ku yi wa Allah ku tallafa wa talakawan ƙasa, roƙon Tinubu ga su Ɗangote

Ku yi wa Allah ku tallafa wa talakawan ƙasa, roƙon Tinubu ga su Ɗangote

Daga BASHIR ISAH Shugaban Ƙasar Nijeriya, Bola Ahmed Tinubu, ya roƙi hamshaƙan 'yan kasuwar ƙasar, wato Aliko Dangote, Abdulsamad Rabiu da sauran masu ƙumbar susa, da su dubi Allah sannan su taimaka wa marasa galihu musamman a wannan wata na Ramadan. Tinubu ya yi wannan kira ne ranar Lahadi a Kano a wajen ƙaddamar da shinkafar da Santa Abdullahi Yari ya tanada don tallafa wa jama'a don girmamawa ga Shugaba Tinubu. Tinubu ya bayyana hakan ne ta bakin wakilinsa kuma hadiminsa, Abdulaziz Abdulaziz, inda ya yaba da karamcin da sanatan ya nuna masa. Ya ce an ƙaddamar da tallafin ne…
Read More
Ku nemi watan Ramadan daga ranar Lahadi — Sarkin Musulmi

Ku nemi watan Ramadan daga ranar Lahadi — Sarkin Musulmi

Daga BASHIR ISAH Sarkin Musulmi kuma Shugaban Majalisar Ƙoli ta Harkokin Musulunci a Nijeriya (NSCIA), Sa’ad Abubakar, ya buƙaci al'ummar Musulmi da a nemi jinjirin watan Ramadan na shekarar 1445AH daga ranar Lahadi, 10 ga Maris, 2024. Umarnin hakan na ƙunshe ne a sanarwar da ke ɗauke da sa hannun Farfesa Sambo Janaidu wanda ya kasance Shugaban Kwamitin Shawara na Majalisar Masarautar Sakkwato wadda aka raba wa manema labarai a ranar Asabar. Sanarwar ta ce: “Ana sanar da Al'ummar Muslim kan cewa su fara neman jinjirin watan Ramadan daga ranar Lahadi, 10 ga Maris wanda ya yi daidai da 29…
Read More
Kuriga: Shettima ya gana da iyayen ɗaliban da aka yi garkuwa da su

Kuriga: Shettima ya gana da iyayen ɗaliban da aka yi garkuwa da su

*Ya ba da tabbacin ceto yaran cikin ƙoshin lafiya Daga BASHIR ISAH Mataimakin Shugaban Ƙasa Kashim Shettima ya gana da shugabannin ƙauyen Kuriga, Jihar Kaduna da kuma iyayen ɗaliban firamaren da ɓarayin daji suka yi garkuwa da su kwanan nan a yankin. Kusan ɗalibai 300 daga makarantar firamare da GSS da ke Kuriga cikin Ƙaramar Hukumar Chikun a jihar, 'yan bindiga suna yi awon gaba da su a farkon makon jiya. Sai dai a tattaunawar da suka yi a Fadar Gwamnatin Jihar a ranar Asabar, Shettima ya bada tabbacin gwamnati ta yanke shawarar ceto ɗaliban da lamarin ya shafa baki…
Read More
An sace ’yan firamare sama da 100 a Kaduna

An sace ’yan firamare sama da 100 a Kaduna

…Sojoji sun yi wa ’yan ta'adda ruwan wuta a Katsina da Zamfara Daga MAHDI M. MUHAMMAD An sace ɗaliban firamare da na sakandare sama da 100 a makarantarsu da ke ƙauyen Kuriga a Ƙaramar Hukumar Chikun ta Jihar Kaduna. Kawo yanzu ba a iya tantance adadin mutanen da aka sace, amma mazauna yankin sun ce kusan 100 ne. Rahotanni sun ce shugaban makarantar da wasu ma’aikatan makarantar na cikin waɗanda abin ya shafa. An tattaro cewa lamarin ya faru ne da misalin ƙarfe 8:20 na safe a lokacin da ɗaliban ke taro (assembly) na ranar Alhamis. Ɗaliban sakandare sun koma…
Read More
Ba jami’an CPG suka kashe Sheikh Abubakar Hassan Mada ba – Gwamnatin Zamfara

Ba jami’an CPG suka kashe Sheikh Abubakar Hassan Mada ba – Gwamnatin Zamfara

*An kama waɗanda ake zargi Daga BASHIR ISAH Aƙalla 'yan banga 10 ne aka tsare bisa zargin kisan malamin addini a Jihar Zamfara. MANHAJA ta rawaito an kashe Sheikh Abubakar Hassan Mada ne a ranar Talata a garin Mada da ke cikin yankin Ƙaramar Hukumar Gusau a jihar. Kakakin Gwamnan Zamfara, Sulaiman Bala Idris, ya ce waɗanda hukuma ta kama 'yan banga ne ba jami'an bai wa al'umma kariya (CPG) ba. MANHAJA ta rawaito ana zargin jami'an CPG da yi wa Sheikh Abubakar Hassan Mada kisan gilla, lamarin da ya jefa al'ummar jihar cikin ruɗani. Sai dai sanarwar da Sulaiman…
Read More
Tsadar Rayuwa: ‘Abin da muka shuka muke girba’ – Shettima

Tsadar Rayuwa: ‘Abin da muka shuka muke girba’ – Shettima

Daga BASHIR ISAH Matamakin shugaban Ƙasa Kashim Shettima, ya bayyana cewa abin da aka shuka a baya shi ake girba a yanzu dangane da tsadar rayuwar da ake fuskanta a ƙasa. Shettima ya buƙaci ‘yan Nijeriya da a kula da yadda suke bayyana fushinsu game da matsalolin tattalin arzikin da ƙasa ke fama da su a wannan hali. Ya ce dukkanin abubuwan da ake gani a yanzu sakamakon abubuwan da aka aikata a gwamnatocin a baya ne wanda ƙasar ke ƙoƙarin daidaita komai don inganta tattalin arzikin ƙasa. Ya ci gaba da cewa, kamar kowace gwamnati, ita gwamnatin Shugaba Bola…
Read More
Tinubu ga ’yan Nijeriya: Wahalarku ba za ta tashi a banza ba

Tinubu ga ’yan Nijeriya: Wahalarku ba za ta tashi a banza ba

*Shugaban ya ɗora alhakin taɓarɓarewar tattalin arziki a kansa Daga MAHDI M. MUHAMMAD Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya ɗauki cikakken alhakin taɓarɓarewar tattalin arzikin da 'yan Nijeriya ke fuskanta tare da tabbatar wa 'yan ƙasar cewa, wahalhalun da suke fama da shi ba zai faɗi wasa banza ba. Tinubu ya bayyana haka ne a lokacin da yake jawabi ga shugabannin ƙungiyar Afenifere a gidan Pa Reuben Fasoranti da ke Akure, Jihar Ondo, a ranar Laraba, 28 ga Fabrairu, 2024. A cewar wata sanarwa da mai ba shi shawara na musamman kan harkokin yaɗa labarai, Ajuri Ngelale ya fitar, shugaban…
Read More