12
Mar
Daga BASHIR ISAH Rahotanni daga jihar Kaduna sun ce aƙalla mutum 61 wasu da ake zargin 'yan fashin daji ne suka yi garkuwa da su a yankin Buda da ke cikin Ƙaramar Hukumar Kajuru a jihar. Duk da dai babu bayani a hukumance ka aukuwar harin, sai dai wani mazaunin yankin ya shaida wa majiyarmu ranar Talata cewar, maharan sun dira ƙauyen ne da misalin ƙarfe 11:45 na dare inda suka yi awon gaba da mutum 61. A cewar Dauda Kajuru wanda mazaunin yankin ne, 'yan bindigar shiga yankin da yawansu, kuma sun harba bindiga. Ta bakinsa, “abin da ya…