Rahoto

Sarkin Borin Kabi ya zama Garkuwan masu maganin gargajiya na ƙasa

Sarkin Borin Kabi ya zama Garkuwan masu maganin gargajiya na ƙasa

Daga JAMIL GULMA a Kebbi Haɗaɗɗiyar ƙungiyar masu bayar da maganin gargajiya ta ƙasa ta zaɓi Yusuf Abubakar a matsayin Garkuwan masu maganin gargajiya na ƙasa. Tawagar ta masu maganin gargajiya ta ƙasa da ta reshen jihar Kebbi ta iso fadar Mai Martaba Sarkin Kabin Argungu Alhaji Sama'ila Muhammadu Mera a ƙarƙashin jagoranacin Malam Bala Hassan inda suka tabbatar wa Masarautar Sarkin Kabin Argungu da cewa wannan zaɓen Allah ne, sun zaɓe shi ne tun daga mataki na ƙasa ba tare da wata jayayya ba saboda la'akari da irin rawar da ya ke takawa a wannan ɓangaren. Da ya ke…
Read More
Masu zanga-zanga sun garƙame Ministan Ayyuka a ofishinsa

Masu zanga-zanga sun garƙame Ministan Ayyuka a ofishinsa

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Wasu ma’aikatan da suka yi zanga-zanga sun kulle Ministan Ayyuka da Gidaje na Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu, Mista Dave Umahi, a cikin ofishinsa da ke Abuja. An ce ministan ya hana ma’aikatan da suka zo aiki a makare samun damar shiga ma’aikatar. ’Yan ƙungiyar da suka hada da ma’aikatar gidaje da ayyuka sun yanke shawarar kulle ma’aikatar, tare da hana shiga da fita da kuma hana ministan fita daga ofishin. Sun kuma yi ikirarin cewa ya hana injiniyoyi da daraktoci yin aikinsu, kuma tun bayan naɗa shi ya ke karya ƙa’idojin aikin gwamnati, ta hanyar…
Read More
Sanatocin Kebbi sun gana da shugabannin sojoji

Sanatocin Kebbi sun gana da shugabannin sojoji

Daga JAMIL GULMA a Kebbi  Sanatoci daga jihar Kebbi da suka haɗa da Sanata Yahaya Abubakar Abddullahi na gundumar mazaɓar Kebbi ta Arewa da Sanata Garba Musa Maidoki na mazaɓar Kebbi ta Kudu sun gana da shugabannin sojoji dangane da matsalar tsaro da ke addabar waɗansu sassan jihar. Sanata mai wakiltar mazaɓar Kebbi ta Arewa Dr Yahaya Abdullahi ya jagoranci sanatocin jihar Kebbi a ofishin shugaban samar da tsaro na ƙasa Manjo Janar Christopher. Sanata Yahaya Abdullahi ya ce wannan ziyarar tana da alaƙa da rashin tsaro da ke addabar jihar Kebbi musamman yankin gundumar mazaɓar Kebbi ta Kudu don…
Read More
Yadda Nijeriya ta ɗau saiti gadan-gadan a cikin gida da waje ƙarƙashin mulkin Tinubu

Yadda Nijeriya ta ɗau saiti gadan-gadan a cikin gida da waje ƙarƙashin mulkin Tinubu

Daga MOHAMMED IDRIS Nan a cikin gida, Shugaba Bola Tinubu ya kama aiki ka'in-da-na'in, ba tare da wani jinkiri ba, musamman manyan tsare-tsaren saita fasalin tattalin arzikin ƙasa. Baya ga wannan kuma, Shugaba Tinubu ya yi amfani da damar da ya samu a cikin watan Satumba, ya yi wa duniya shiga-da-ƙafar-dama. Satumba ne ya fi zama watan da ayyuka da sha'anin tafiyar da mulki su ka fi kacame masa a cikin duniya, tun bayan rantsar da shi. Shugaba Tinubu ya tafi Indiya inda ya halarci Taron Ƙasashe Masu Ƙarfin Tattalin Arziki na Duniya, wato G20. Shugaban Indiya, Modi, shi ne…
Read More
Rana ko iska a matsayin makamashi

Rana ko iska a matsayin makamashi

Tare da BASHIR MUDI YAKASAI Batunmu na wannan makon shine, hasken rana da kuma iska a matsayin sinadiran da za su samar da makamashi da zai samar da wutar lantarki ga gidajenmu da ofisoshinmu da guraren gudanar da sana’oi da suke buƙatar wutar lantarki har da masana’antu da suke buƙatar wutar lantarki har da masana’antu da kamfanoni da gonaki, kai da duk wuni guri da ake buƙatar wutar lantarki. Kimiya, wato Ilimin ƙwaƙwa da na ci da kuma zurfafa tunani kan al’amari mai tafiya da kuma komowa, sai kuma ilimin fasaha wato, ilimin sarrafa abubuwa zuwa wani abun. Ɗan Adam…
Read More
Tarihin yaƙin duniya na biyu

Tarihin yaƙin duniya na biyu

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Yaƙin duniya na biyu da a Turanci ake kira ‘World War II’ a kan kintse rubutun kamar haka ‘WWII’ ko ‘WW2’, kuma a kan kira shi da Turanci ‘Second World War’. Yaqin dai wani yaqi ne da duniya baki ɗaya suka afka a ciki, wanda ya kwashi tsawon shekaru shida ana gwabzawa, tun daga shekarar 1939 har zuwa shekara ta 1945. Mafi yawan ƙasashen duniya tare da ƙasashe masu qarfi su ne suka ja daga a tsakaninsu, inda suke yaƙan juna. Hakane ya haifar da gagarumin gumurzu tsakaninsu wanda aƙalla mutane sama da miliyan ɗari ne…
Read More
Ma’aikatan lafiya 400,000 sun yi kaɗan a Nijeriya, inji minista

Ma’aikatan lafiya 400,000 sun yi kaɗan a Nijeriya, inji minista

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Ministan Lafiya da Walwalar Al'umma, Ali Pate, ya ce ma'aikatan kiwon lafiya 400,000 a Nijeriya ba su isa ba wajen biyan buƙatun kiwon lafiyar 'yan Nijeriya. Pate ya bayyana hakan ne a lokacin da yake zantawa da manema labarai a ranar Asabar a Abuja, bayan ganawar kwanaki uku da ya yi da sassa da hukumomin da ke ƙarƙashin ma’aikatar. Ma'aikatar ta shirya taron ne domin fitar da wani tsari na tsarin kiwon lafiya a Nijeriya. A cewar Pate, ma’aikatan fannin lafiya dubu 400,000 sun haɗa da ma’aikatan kiwon lafiya na al’umma, ma’aikatan jinya, ungozoma,…
Read More
Za mu magance matsalar cin zarafin mata a hidimar ƙasa – Daraktan NYSC

Za mu magance matsalar cin zarafin mata a hidimar ƙasa – Daraktan NYSC

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Babban Darakta Janar na masu yi wa ƙasa hidima (NYSC) Brig Gen. Yushau Ahmed, ya ce za su magance matsalar cin zarafin mata a NYSC. Babban daraktan wanda ya bayyana hakan a ranar Talata a yayin gangamin wayar da kan al’ummar karkara a Bauchi, ya ce shirin ya dade yana yaqi da GBV ta hannun ƙungiyar ta Corps Gender Vanguards. Darakta Janar na hukumar ta NYSC a Jihar Bauchi, Misis Rifkatu Yakubu, ta wakilce shi, ta bayyana cewa, an samar wa Vanguards kayayyakin aikin da suka dace don gudanar da gangamin wayar da kan…
Read More
INEC ta karrama Sa’idu Bappah da mutum biyar a Gombe

INEC ta karrama Sa’idu Bappah da mutum biyar a Gombe

Daga ABUBAKAR A. BOLARI a Gombe Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Ƙasa INEC a Jihar Gombe ta karrama Shugaban Sashin Injiniyoyi na hukumar Injiniya Sa'idu Bappa Yaya da wasu ma'aikata mutum 5 bisa jajircewar su a aiki a Jihar Gombe. INEC ta karrama ma'aikatan na ta ne bisa hazaƙar a aiki kafin zaɓe da bayan babban zaven shekarar 2023 da ya gabata. A jawabinsa a wajen taron karramawar da ya gudana a helkwatar hukumar Kwamishinan Zaɓen na Jihar Gombe Alhaji Ibrahim Umar, yaba wa ma'aikatan ya yi bisa ƙwazon da suka nuna a aikin su wanda hakan ne sanadiyyar…
Read More
Tallafi: Gwamnan Neja ya bai wa NLC tirelar shinkafa biyu

Tallafi: Gwamnan Neja ya bai wa NLC tirelar shinkafa biyu

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Gwamnan Jihar Neja, Umaru Bago ya amince da tireloli biyu na buhunan shinkafa mai nauyin kilogiram 50 ga ƙungiyar ƙwadago ta ƙasa, NLC, a matsayin tallafin rage raɗaɗin cire tallafn man fetur. Mista Bago ya sanar da amincewar ne a lokacin liyafar murnar sabon ginin ofishin mataimakin gwamna, Yakubu Garba da aka gina a Minna. Ya bayyana cewa Naira miliyan 110 da aka amince wa ƙungiyar ta NLC tun da fari, an ba su ne don samar da kayan aiki don sanya ido kan yadda ake raba kayan agajin a mazaɓu 274 na jihar.…
Read More