29
Sep
Daga JAMIL GULMA a Kebbi Haɗaɗɗiyar ƙungiyar masu bayar da maganin gargajiya ta ƙasa ta zaɓi Yusuf Abubakar a matsayin Garkuwan masu maganin gargajiya na ƙasa. Tawagar ta masu maganin gargajiya ta ƙasa da ta reshen jihar Kebbi ta iso fadar Mai Martaba Sarkin Kabin Argungu Alhaji Sama'ila Muhammadu Mera a ƙarƙashin jagoranacin Malam Bala Hassan inda suka tabbatar wa Masarautar Sarkin Kabin Argungu da cewa wannan zaɓen Allah ne, sun zaɓe shi ne tun daga mataki na ƙasa ba tare da wata jayayya ba saboda la'akari da irin rawar da ya ke takawa a wannan ɓangaren. Da ya ke…