Rahoto

Dalilin da ke sa mutum saurin jin fitsari bayan sahur

Dalilin da ke sa mutum saurin jin fitsari bayan sahur

Tare da CHIROMA AMINU ASID Sau da dama mutane na iya fuskanta wani yanayi na saurin jin fitsari bayan sahur. Hakan yana faruwa ne, saboda wasu dalilai na halitta da ɗabi’a, kamar haka:- Shan ruwa da yawa lokaci guda: Idan mutum ya sha ruwa da yawa a lokaci guda, ƙodojinsa za su riƙa tace ruwan da wuri. Hakan na sa yawan fitsari. Shan kayan sha masu ‘caffeine’: Shan abubuwan sha masu ƙarfafa fitsari (Diuretics), wasu nau’in abinci ko abin sha na iya sa fitsari ya ƙaru. Wannan ya haɗa kayan sha masu ‘caffeine MM’, kamar a shayi da kofi, kayan…
Read More
’Yan uwan juna sun yi wa almajiri yankan rago a Adamawa

’Yan uwan juna sun yi wa almajiri yankan rago a Adamawa

Rundunar ’yan sandan Adamawa ta cafke wasu wa da ƙani, Aliyu Abdulmalik da Ibrahim Abdulmalik, kan zargin yanke kan wani almajiri ɗan shekara 10, Abdallah Lawali. Bayanai sun ce ’yan uwan junan biyu sun aikata wannan ta’asa ce a ranar 7 ga watan Maris a unguwar Sarkin Yamma da ke ƙaramar Hukumar Jada. Sanarwar da rundunar ’yan sandan ta fitar ta ce an kama ababen zargin ne da gangar jikin almajirin a cikin wani buhu, yayin da aka ƙwaƙulo kansa a cikin wani rami da suka binne a harabar gidansu. Rundunar wadda ta ce yanzu haka bincike ya kankama a…
Read More
Wani abu da ya kamata a sani game da cutar hawan jini

Wani abu da ya kamata a sani game da cutar hawan jini

Tare da CHIROMA AMINU ASID Bayani kan cutar hawan Jini: Mene ne hawan jini? Cutar hawan jini ita ce buguwar zuciya ya wuce adadin da ake buƙata. Ciwon hawan jini yana ɗaya daga cikin cutuka masu haifar da illoli a jiki daga ciki har da rasa rai, domin ya na kashewa nan take. A ƙa'ida fa, hawan jini kashi 85 ba asan abunda ke haddasa shi ba. Alamomin da za a fahimci akwai alamun hawan jini sun sha bamban da illolin da yake haifarwa. Hawan jini yana zubar da ciki, ya tsotse jini, ya haddasa tsinkau tsinkau, ya sa ciwon…
Read More
’Yan fansho a Kaduna, Kano da Katsina sun koka kan jinkirin biyan su kuɗaɗen ritaya

’Yan fansho a Kaduna, Kano da Katsina sun koka kan jinkirin biyan su kuɗaɗen ritaya

Daga MAHDI MUSA MUHAMMAD Ma’aikatan Gwamnatin Tarayya da suka yi ritaya a Kaduna, Kano, da Katsina, sun bayyana matuƙar ɓacin ransu kan jinkirin da aka samu wajen biyansu hakkokinsu na ritaya, wanda ke ƙara dagula musu rayuwa sakamakon ƙalubalen tattalin arzikin Nijeriya. Yawancin masu ritaya, waɗanda wasu daga cikinsu sun bar aiki har zuwa Maris 2023, sun ba da rahoton cewa har yanzu suna jiran a fara buyansu kuɗin fansho. A Kaduna, Ahmad Kawure, wanda tsohon ma’aikaci ne a hukumar kula da ayyukan yi ta ƙasa, ya bayyana rashin jin daɗinsa bayan ya shafe kusan shekara guda yana jiran kuɗin…
Read More
Hukumar lafiya matakin farko ta inganta harkokinta a Nasarawa – Dakta Usman Saleh

Hukumar lafiya matakin farko ta inganta harkokinta a Nasarawa – Dakta Usman Saleh

Daga JOHN D WADA a Lafiya Hukumar kiwon lafiya ta matakin farko ta gwamnatin Jihar Nasarawa ta ce a yanzu haka tana aiki tuƙuru ne tare da haɗin gwiwar babban bankin duniya da sauran abokan hulɗa wajen inganta harkokin ta na kiwon lafiya a faɗin jihar baki ɗaya. Shugaban hukumar Dakta Usman Iskilu Saleh ne ya sanar da hakan a lokacin da yake karɓar baƙuncin ƙungiyar masu aiko da rahotanni, wato correspondents chapel a turance, ta ƙasa reshen Jihar Nasarawa a hukumar da ke Lafiya babban birnin jihar a makon da ake ciki. Ya ce, a yanzu haka hukumar ta…
Read More
Mutum miliyan 30 za su fuskanci ƙarancin abinci tsakanin Yuni zuwa Agusta

Mutum miliyan 30 za su fuskanci ƙarancin abinci tsakanin Yuni zuwa Agusta

Daga MAHDI MUSA MUHAMMAD Wani rahoton na Cadre Harmonise game da mummunan matsalar abinci a Nijeriya ya yi hasashen cewa, mutane miliyan 30.6 a faɗin Jihohi 26 da Babban Birnin Tarayya za su kasance cikin wani yanayi na ƙarancin abinci tsakanin watan Yuni da Agusta. Rahoton wanda gwamnatin tarayya da gwamnatocin Jihohi tare da tallafin Hukumar Abinci da Aikin Noma ta FAO da sauran ƙungiyoyin raya ƙasa suka gudanar, ya nuna cewa adadin ya haɗa da ‘yan gudun hijira 150,978. Ta bayyana cewa, duk da raguwar farashin abinci da kayayyakin masarufi a faɗin ƙasar, kimanin mutane miliyan 24.9, da suka…
Read More
Ya yi kuskuren liƙe bakinsa yayin wasan barkwanci

Ya yi kuskuren liƙe bakinsa yayin wasan barkwanci

Kwanan nan ne wani bidiyo na wani mutum ɗan ƙasar Philippines ya ɗauki hankalin jama’a a intanet. A cikin bidiyon, mutumin ya shafa sufa-gilu a laɓɓansa a matsayin wani ɓangaren na wasan barkwanci, amma lamarin ya sauya zuwa wani abun daban. Mai wasan barkwanci ya liƙe laɓɓansa bayan da ya shafa musu gam ɗin sufa-gilu a yayin da yake yin bidiyo kai-tsaye domin ƙayatar da masu bibiyarsa. Mutumin ya shafa gilu ne, inda ya manne laɓɓansa, wanda cikin dakika kaɗan, mannewar ta kama fatar laɓɓan kamar yadda ya so, inda hakan ya sa yabar laɓɓansa a rufe sosai. A zamanin…
Read More
Tarihin Bawa Jangwarzo

Tarihin Bawa Jangwarzo

Daga MAHDI MUSA MUHAMMAD Bawa Jan Gwarzo wanda sunansa na gaskiya Umaru Dogo, shi kaɗai mahaifiyarsa ta haifa, yana da ’yan uwa guda goma sha ɗaya, kuma Allah shi ya zaɓa a cikinsu ya bai wa sarauta. Sunan mahaifinsa Amadu, wanda ake kiran sa da Almada, bayan rasuwarsa ne jama’a daga cikin ma su mulki su ka nuna cewa sun fi ƙaunar a ba wa Bawa Jan Gwarzo sarauta. Dalilin wannan suna na Bawa Jan Gwarzo kuwa shi ne, ya kasance mutum ne shi mai yawan Bautawa Allah da roƙon Allah akan ya bashi sarautar da zai zamana ya fi…
Read More
Ƙabilar Abzinawa

Ƙabilar Abzinawa

Daga MAHDI MUSA MUHAMMAD Abzinawa ƙabila ce da ke a yankunan Kudancin Afrika, musamman ma a ƙasashen kamar Nijar, inda yawansu ya kai kimanin 2,116,988, ƙasar Mali yawansu ya kai 536,557, Burkina Faso yawansu ya kai 370,738, sai ƙasar Aljeriya yawansu ya kai 25,000 sai kuma ƙasar Tunusiya inda yawansu ya kai kimanin 2,000. Hakanan kuma ana samun wasu ’yan kaɗan a Faransa da koma Nijeriya. Abzinawa Bororo (Masu Yawo) ne kuma masu arziki. Akasarin Abzinawa sun kasance Musulmai ne. Al’ummar Abzinawa na daga cikin ƙabilu da dama kamar Soninke, Mende, Bambara, Songhai, Madinka, Mossi da dai sauransu waɗanda suka…
Read More
Ƙungiyar Rayuwar Mata ta tallafa wa mutum dubu 20 da abinci a Nijar da Nijeriya

Ƙungiyar Rayuwar Mata ta tallafa wa mutum dubu 20 da abinci a Nijar da Nijeriya

Daga MUKHTAR A. HALLIRU TAMBUWAL a Sakkwato Kowacce shekara ƙungiyar Rayuwar Mata, da ke tallafawa cigaban mata, wacce Malama Khadija Abubakar ke jagoranci, tana raba wa mabuƙata abincin buɗe-baki, a lokacin azumin Ramadan, kamar yadda take gudanarwa a wannan shekarar. Kawo yanzu ƙungiyar ta baba abinci ga jama'a da dama da suka haɗa da ’yan gudun Hijira, waɗanda ambaliyar ruwa ta rutsa da su, akwai masu lalura ta musamman, akwai zawarawa, uwayen marayu, da almajirrai da sauransu. An tsara gudanar da aikin rabon abincin a wasu sassan garin Maraɗi a Jamhuriyar Nijar, da wasu yankuna na jihohin Zamfara, Sakkwato, Katsina…
Read More