Rahoto

Tamuwa: Red Cross ta tallafa wa gwamnatin Katsina da katan 700 na ƙwamaso

Tamuwa: Red Cross ta tallafa wa gwamnatin Katsina da katan 700 na ƙwamaso

Daga ABDULLAHI MUHAMMAD a Katsina Jihar Katsina ta karɓi katan 700 na ɗan ƙwamaso (RUTF) daga Ƙungiyar Red Cross ta Najeriya, domin tallafa wa ƙoƙarin gwamnati na yaƙi da tamowa, a tsakanin yara. An miƙa kayan ta hannun Kungiyar reshen Jihar Katsina. Za a rarraba ga yaran da ke fama da tamowa a faɗin jihar, tare da tabbatar da cewa kayan sun isa ga waɗanda aka tanada kuma an yi amfani da su yadda ya kamata. Wannan ba shi ne karon farko da Red Cross ke tallafa wa Katsina wajen yaƙi da tamowa ba. A irin wannan lokaci a shekarar…
Read More
Yadda ake amfani da kafafen sadarwa na zamani: Tasirinsu, damarmaki da ƙalubale kashi na biyu

Yadda ake amfani da kafafen sadarwa na zamani: Tasirinsu, damarmaki da ƙalubale kashi na biyu

Daga BILKISU YUSUF ALI, Ph’D Gabatarwa: Kamar yadda muka faro bayani a makon da ya gabata. Kafafen sadarwa na zamani sun zama ginshiƙin sadarwa a ƙarni na 21. Sun sauƙaƙa yaɗa bayanai da ilimi da  kasuwanci da  siyasa da hulɗar jama'a cikin sauri. Duk da haka, rashin amfani da su yadda ya kamata na iya haifar da yaɗuwar labaran ƙarya da zamba ta yanar gizo da cin zarafi da rashin tsaro. Wannan takarda ta yi bayani kan ma'anar kafafen sadarwa na zamani, nau'o'insu, yadda ake amfani da su cikin hikima, fa'idodinsu, ƙalubalen da suke tattare da su, da hanyoyin inganta…
Read More
Yaƙin Basasar Kano (1894–1895)

Yaƙin Basasar Kano (1894–1895)

Shekaru 131 kenan tun bayan da al'ummar Kano suka tsinci kansu cikin mummunan yaƙin basasa sakamakon rikicin sarauta tsakanin gidan Sarkin Kano Abdullahi Maje Karofi da gidan Sarkin Kano Muhammadu Bello, waɗanda dukkansu 'ya'yan Sarkin Kano Ibrahim Dabo ne. Masana tarihi sun bayyana wannan yaƙi a matsayin mafi muni da birnin Kano ya taɓa fuskanta. An rawaito cewa wani Bature da ya ziyarci Kano a lokacin ya ce, "Kano ta zama ƙasar jini saboda irin yawan jinin da aka zubar." Wannan yaƙi ya haifar da babbar asara ga rayuka, dukiyoyi da kuma tattalin arzikin birnin. Asalin rikicin: Bayan rasuwar Sarkin…
Read More
2027: Abin da ya sa zan dawo da tallafin fetur idan na ci zaɓe – Atiku

2027: Abin da ya sa zan dawo da tallafin fetur idan na ci zaɓe – Atiku

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Tsohon Mataimakin Shugaban Majalisar ƙasa kuma ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar African Democratic Congress (ADC), Alhaji Atiku Abubakar, ya yi alƙawarin dawo da tallafin man fetur idan aka zaɓe shi a matsayin shugaban ƙasa a zaɓen 2027. Atiku Abubakar ya bayyana hakan ne a wata hira da aka yi da shi ranar Laraba, inda ya ce bai yi adawa da cire tallafin man fetur a farko ba, amma matsalar ita ce yadda gwamnati ta yi amfani da kuɗin da aka samu bayan cire tallafin. Ya ce ya kamata kuɗin da aka samu daga…
Read More
Mambayya sai mai nazari

Mambayya sai mai nazari

Daga NASIRU ADAMU EL-HIKAYA Malam Aminu Kano bai gina gidansa “Mambayya” a 1968 don taron ranar zallawa ba. Wallahi ko sunan gidan ba su iya rubutawa daidai ba! maimakon Mam-bayya sai su ka maka Man-bayya. ƙarshe na ga Zallawa sun bayyana inda za su yi taron ranarsu ta zallanci da fakewa da wai ranar Hausa a gidan MAMBAYYA inda su ka rubuta MANBAYYA da “N” maimakon “M” don dama ’yan arufta ne ba sa iya rubutu ko magana da Hausa tiryan-tiryan sai sun wurga Turanci. Hausa ba layinsu ba ne sam. MAMBAYYA gidan marigayi Malam Aminu Kano ne da ya…
Read More
Gwamnan Kano Ahmed Daku

Gwamnan Kano Ahmed Daku

Ahmed Mohammad Daku an haife shi kuma ya yi karatunsa a Katsina. Ya halarci Barewa College daga shekarar 1958 zuwa 1962, sannan ya ci gaba da karatu a Okene Secondary School daga 1962 zuwa 1965. Aikin Soja: A shekarar 1967, Ahmed Daku ya shiga Nigerian Defence Academy, inda aka ba shi muƙamin Second Lieutenant shekara guda bayan haka. Ya shiga yakin basasar Nijeriya a matsayin jagoran dakaru da kwamanda, sannan daga shekarar 1969 zuwa 1972 ya kasance kwamandan batir. An horar da shi a fannin makaman harbo-harbo (Artillery). Ya halarci Royal School of Artillery da ke Larkhill sau biyu, daga…
Read More
Me ya sa wasu ‘ya’ya ke bijire wa iyayensu?

Me ya sa wasu ‘ya’ya ke bijire wa iyayensu?

Daga MUKHTAR YAKUBU  Tasirin rikicin iyaye ga ƙwaƙwalwar yara Allah maɗaukakin Sarki ya ce:"Ya ku waɗanda suka yi imani! Ku tsare kanku da iyalanku daga wuta." (Suratut-Taḥrīm: 6) Iyaye da yawa suna tambaya: "Me ya sa ɗana ko 'yata ba sa jin magana?"  Ko kuma: "Me ya sa yaro yake da taurin kai?" Sau da yawa ana kallon yaro ne kawai. Amma ilimin halayyar ɗan adam yana nuna cewa dole ne a kalli gidan da yaron ya taso kafin a yanke hukunci a kansa. ƙwaƙwalwar yaro tana gina kanta ne daga abin da take gani. Lokacin da yaro yake ƙarami,…
Read More
Me ya sa ake yawan mantawa da ƙafa a kwalliya?

Me ya sa ake yawan mantawa da ƙafa a kwalliya?

Daga AISHA ASAS  Akwai abubuwan da mutum kan yi wa kansa ba tare da ya ɗauke su a matsayin wani nau'in kulawa ta musamman ba. Wanke fuska, shafa mai, gyaran gashi, tsaftace farce da neman kayan kwalliya masu kyau duk suna daga cikin abubuwan da mutane da dama suka saba yi domin su kasance cikin tsari. Amma idan aka tambayi mutum yadda yake kula da ƙafafunsa, akwai yiwuwar amsar ta zama daban. Wataƙila ya tuna da lokacin da zai yi pedicure, ya shafa mai ko ya gyara farcen ƙafa. Amma kulawar kafa ta fi haka nisa. Domin kafin takalmi ya…
Read More
Sakataren Gwamnatin Yobe ya cancanci sarautar Jigon Fika – Fatima Paga

Sakataren Gwamnatin Yobe ya cancanci sarautar Jigon Fika – Fatima Paga

Daga ABUBAKAR A BOLARI Jami’ar kula da harkokin mata ta Majalisar Ɗinkin Duniya (UN Women) a jihar Yobe ga gwamna Mai Mala Buni, Hajiya Fatima Muhammad Paga, ta bayyana naɗa Sakataren Gwamnatin Jihar (SSG), Dakta Muhammad Goje, a matsayin Jigon Fika da Sarkin Fika, Alhaji (Dakta) Muhammadu Abali Ibn Muhammadu Idrissa, CON, ya yi, a matsayin abin da ya dace. A cikin saƙon taya murna da ta fitar, Paga ta ce karramawar ta nuna irin shekaru na sadaukarwar da Goje ya yi wajen hidimar jama’a da kuma gudunmawar da ya bayar wajen ci gaban jihar Yobe da jin daɗin al’ummarta.…
Read More
Gwamnatin Tarayya ta saki biliyan N11.58 ga shirin tallafa wa mutane 178,342 a Jigawa

Gwamnatin Tarayya ta saki biliyan N11.58 ga shirin tallafa wa mutane 178,342 a Jigawa

Daga MAHDI MUSA MUHAMMAD Gwamnatin Tarayya ta fitar da sama da Naira biliyan 11.58 domin aiwatar da shirin Tallafin Tsaron Rayuwar Jama’a na Sabunta Fata, wato Renewed Hope Social Security Grant, a Jihar Jigawa, inda ake sa ran mutane 178,342 za su amfana da tallafin a faɗin ƙananan hukumomin jihar 27. Kwamishinan Ayyuka na Musamman da Harkokin Agaji na Jihar Jigawa, Hon. Auwal Sankara, ne ya bayyana hakan yayin da yake yi wa ’yan jarida bayani kan yadda shirin ke gudana. Ya ce, an tsara shirin ne domin tallafa wa iyalai masu ƙaramin ƙarfi ta fuskar kuɗi tare da haɓaka…
Read More