Rahoto

Abokan Mujaddadi allo da tawada

Abokan Mujaddadi allo da tawada

Daga NASIRU ADAMU EL-HIKAYA Har Shehu Usmanu Danfodiyo ya koma ga Allah a shekaru 63 bai samu zarafin yin hajji ba don sadaukar da kansa kakaf ga koyarwa. Kama daga ƙofar gidansa, masallaci har duk inda ya nufa a cikin jama’arsa. Hatta kaninsa Sheikh Abdullahi Gwandu ya yi yunƙurin tafiya aikin hajji amma kanawa su ka dakatar da shi don ya koya mu su addini. Gaba ɗaya rayuwar Shehu Mujaddadi a hidimar karatu, karantarwa da wayar da kan al’umma ne kan dokokin addinin Musulunci na ƙarfafa gaskiya da amana da tarbiyya. Wannan ya sa ba a samun ko rabin sa’a…
Read More
An kama mai aski bisa zargin amfani da gashin mutane don yin tsafi

An kama mai aski bisa zargin amfani da gashin mutane don yin tsafi

An kama wani mai aski mai suna Emeka a garin Umuahia, babban birnin Jihar Abia, bayan da jami'an Rundunar 'Yan Sandan Jihar Abia suka gano wata tukunya da ke cike da gashin mutane a cikin ɗakinsa. Rahotanni sun ce Emeka ya yi suna a Umuahia saboda ƙwarewarsa wajen aski, sai dai an cafke shi ne a ranar Talata bayan maƙwabcinsa, Johnson Ikenga, ya kai ƙorafi ga 'yan sanda yana zargin mai askin da yi masa barazana. A yayin da jami'an 'yan sanda suka kai samame gidan wanda ake zargin domin bincike, sun gano wata tukunya mai ɗauke da gashin mutane…
Read More
Me ya sa ‘yan Kannywood suka mamaye harkar siyasa?

Me ya sa ‘yan Kannywood suka mamaye harkar siyasa?

Daga AISHA ASAS  *Shin suna shiga domin wakiltar muradun jama'a ko kansu? A shekarun baya, sunayen fitattun jaruman Kannywood sun fi yawan bayyana ne a fagen fina-finai, waƙoƙi da nishaɗantar da jama'a. Kyamarori, hasken fage da kuɗin shirya fina-finai ne suka fi zama abubuwan da ake danganta su da wannan masana'anta. Amma a yau, wannan hoton ya fara sauyawa. Wasu daga cikin fitattun jarumai, mawaƙa da masu shirya fina-finai sun koma wani babban dandali da za mu iya cewa saɓa wa sanannen abubuwan da suke fassara masana'antar, wato fagen siyasa. Daga halartar gangamin jam'iyyu, zama masu taimaka wa 'yan takara,…
Read More
Zaɓen Osun: Zan yi nasara idan aka yi sahihin zabe — Adeleke

Zaɓen Osun: Zan yi nasara idan aka yi sahihin zabe — Adeleke

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Gwamnan Jihar Osun kuma ɗan takarar Jam'iyyar PDP a zaɓen gwamna na ranar 15 ga Agusta, Ademola Adeleke, ya bayyana ƙwarin gwiwar cewa zai sake lashe zaɓe idan aka gudanar da shi cikin sahihanci da adalci. Adeleke ya bayyana hakan ne a ranar Litinin yayin wani gangamin neman zaɓen tazarce da aka gudanar a Osogbo. "Da taimakon Allah, ina da cikakken yaƙinin samun nasara. Idan aka gudanar da zaɓe cikin gaskiya da adalci, zan yi nasara," inji shi. Gwamnan ya kuma yi zargin cewa ana kashe mambobin jam'iyyarsa, lamarin da ya sa ya roƙi…
Read More
Gwamnatin Tarayya ta ƙara ƙarfafa haɗin gwiwa da Cocin Katolika domin magance ƙalubalen Nijeriya – Akume

Gwamnatin Tarayya ta ƙara ƙarfafa haɗin gwiwa da Cocin Katolika domin magance ƙalubalen Nijeriya – Akume

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Sakataren Gwamnatin Tarayya (SGF), Sanata George Akume, ya tabbatar da aniyar gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu na ƙara ƙarfafa haɗin gwiwa da Taron Limaman Cocin Katolika na Nijeriya (CBCN), sauran ƙungiyoyin addinai, cibiyoyin gargajiya, ƙungiyoyin fararen hula da kuma kamfanoni masu zaman kansu domin magance manyan ƙalubalen da ƙasar ke fuskanta. Sanarwar da Mai Ba SGF Shawara kan Yaɗa Labarai da Hulɗa da Jama'a, Yomi Odunuga, ya sanya wa hannu ta bayyana cewa Akume ya yi wannan bayani ne bayan wata ganawa da Shugaba Tinubu ya yi da shugabannin CBCN. Akume ya ce, magance…
Read More
Masu ciwon sukari sun fi buƙatar kula da ƙafa

Masu ciwon sukari sun fi buƙatar kula da ƙafa

Daga AISHA ASAS Masu karatu, barkanku da sake saduwa a wannan makon cikin shafinmu na Kwalliya. Muna fatan darussan da muke tattaunawa suna ƙara wayar muku da kai kan yadda za a kare ƙafa da kuma kauce wa matsalolin da za a iya hana faruwarsu. A makonnin da suka gabata mun mayar da hankali kan muhimmancin kula da ƙafa, inda muka yi bayani kan matsalolin da rashin kula da ita kan haifar, tare da hanyoyin da za su taimaka wajen tabbatar da lafiyarta. A yau kuma za mu ci gaba da wannan darasi ne ta fuskar da ta fi shafar…
Read More
Kasuwar Kurmi: Kasuwar da ta gina Jihar Kano ta kuma sauya tarihin kasuwancin Afirka ta Yamma

Kasuwar Kurmi: Kasuwar da ta gina Jihar Kano ta kuma sauya tarihin kasuwancin Afirka ta Yamma

Daga MAHDI MUSA MUHAMMAD Blueprint Manhaja na ci gaba da kawo wa masu karatu shafinta na tarihi domin tunatar da al'umma muhimman abubuwan da suka taka rawa wajen gina tarihin Nijeriya, musamman waɗanda ba kasafai ake ba su kulawar da ta dace ba. A wannan makon, mun waiwayi tarihin Kasuwar Kurmi ta Kano, ɗaya daga cikin tsofaffin kasuwannin Afirka da ta yi fice wajen bunƙasa kasuwanci, sana'o'i da tattalin arziki tun sama da ƙarni biyar da suka gabata. Wannan nazari zai bayyana yadda kasuwar ta kasance ginshiƙin ci gaban Kano da kuma rawar da ta taka wajen haɗa Afirka Ta…
Read More
Koya wa matasa kamun kifi

Koya wa matasa kamun kifi

A ƙasar mu Nijeriya, musamman yankin Arewa, zaman kashe wando da matasa ke yi na ci wa gwamnati da duk wani mai kishin cigaban matasa tuwo a ƙwarya. Mun wayi gari mafi yawan matasanmu basu da ayyukan yi. Yayin da wasu da dama sun gama karatun su na digiri a jami'o'i a fannoni daban-daban amma babu aikin yi.  Sai dai a maimakon waɗannan matasa su nemi ananan sana'o'i da za su yi, sai dai ka ga mafi yawan su sun raina ƙananan sana'o'i da ayyukansu, suna ganin in ba aikin gwamnati da za a biya su kuɗaɗe masu yawa ba,…
Read More
Ta’addanci a Arewa: Ina mafita ta ke?

Ta’addanci a Arewa: Ina mafita ta ke?

A halin yanzu, babu shakka Arewa na matuƙar buƙatar mafita daga matsalolin rashin tsaro, musamman ta'addanci, garkuwa da mutane domin neman kuɗin fansa da kuma hare-haren 'yan bindiga. A cikin wannan makon ne muka samu rahoton yadda wasu da ake zargin 'yan ta'adda ne suka yi garkuwa da wani Alƙalin Babbar Kotu a Jihar Kebbi. Haka kuma, an kuma yi garkuwa da wani ɗan siyasa a Jihar Zamfara. Waɗannan al'amura abin takaici ne matuƙa. Sai dai, a wani ɓangaren kuma, an kama wasu da ake zargi da hannu wajen sace ɗalibai a Jihar Oyo, inda ake cewa alamu sun nuna…
Read More
Mu koyi hana juna ɓarna da yin ba daidai ba

Mu koyi hana juna ɓarna da yin ba daidai ba

Daga ABBA ABUBAKAR YAKUBU  Mai karatu yau za ka ji rubutuna na wannan makon ya ɗauki wani salo kamar na mai wa'azi to, ba wa'azi ba ne, faɗakarwa ce da tunatarwa daga almajiri mai neman ilimi. Domin shi wa'azi malamai masu tawali'u da tsoron Allah ne ke yin sa, da baki ko a cikin ayyukansu. Na ce haka ne don mu fahimci shi wa'azi ba kawai sai a wajen aikin addini ko a wurin ibada ake yin sa ba. Muna ganin abubuwan wa'azi da dama daga ayyukan malamai da koyarwar su, da kuma abubuwan da ke faruwa a kewayen mu.…
Read More