Rahoto

Jami’an tsaro sun hana ’yan majalisar dokoki shiga fadar Sarkin Dutse wajen naɗin Sardauna

Jami’an tsaro sun hana ’yan majalisar dokoki shiga fadar Sarkin Dutse wajen naɗin Sardauna

Daga UMAR AKILU MAJERI a Dutse Jami'an tsaron farin kaya sun hana Shugaban Masu Rinjaye a Majalisar Dokokin Jihar Jigawa, Alhaji Lawan Muhd Dansure, shiga fadar Mai Martabar Sarkin Dutse a lokacin bikin naɗin Sardaunan Dutse, Alhaji Nasiru Haladu Dano, wanda ya gaji kujerar Marigayi Alhaji Bello Maitama Yusuf, tsohon Sardaunan Dutse, wanda ya rasu a shekarar da ta gabata.  Jami'an tsaron sanye da baƙaƙen gilasai sun samu damar korar Shugaban Masu Rinjaye da tawagarsa ne a lokacin da su ka halarci fadar ta Mai martaba Sarkin na Dutse, Alhaji Hamim Muhd Sunusi, a lokacin da ya ƙaddamar da naxin…
Read More
Gwamnatin Nijeriya na biyan tallafin mai a yanzu fiye da a baya – El Rufa’i

Gwamnatin Nijeriya na biyan tallafin mai a yanzu fiye da a baya – El Rufa’i

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Tsohon gwamnan jihar Kaduna, Malam Nasir El Rufai ya yi zargin cewa gwamnatin Nijeriya na ci gaba da biyan tallafin mai wani abu da ya ce an Nijeriya da dama ba su sani ba. Da yake amsa tambayoyin manema labarai a Maiduguri, babban birnin jihar Borno, El Rufai ya ce a yanzu gwamnati na biyan fiye da abin da take biya a matsayin tallafin mai a baya. Ya bayyana cewa matakai da dama da aka tanada na rage raɗaɗin janye tallafin mai ba sa tasiri abin da a cewarsa ya sa aka maido da…
Read More
Bayan shekara 10 da sace ‘yan matan Chibok: Wani abu da ya kamata a sani

Bayan shekara 10 da sace ‘yan matan Chibok: Wani abu da ya kamata a sani

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Jaridar News Point Nigeria ta samu damar haɗuwa da Lisu a sirrance, yayin da ta ce wasu na ƙoƙarin hana ta magana da ‘yan jarida. Lisu na ɗaya daga cikin 'yan mata 276 da aka sace daga makarantar sakandare ta 'yan mata a garin Chibok shekaru goma da suka wuce - satar da ta girgiza duniya kuma ta haifar da zangar-zangar neman a dawo da 'yan matan mai taken: #BringBackOurGirls, wanda har ya haɗa da uwargidan tsohon Shugaban Ƙasar Amurka, Michelle Obama. Sama da 180 ne dai suka kuɓuto ko kuma aka sake su,…
Read More
Yadda yara uku ‘yan gida ɗaya suka riga mu gidan gaskiya rana guda a Nasarawa

Yadda yara uku ‘yan gida ɗaya suka riga mu gidan gaskiya rana guda a Nasarawa

Daga BASHIR ISAH Iyalan gidan Malam Sulaiman Ibrahim da ke garin Toto, cikin Ƙaramar Hukumar Toto, Jihar Nasarawa, sun tsinci kansu cikin halin jimami biyo bayan mutuwar wasu yaran gidan su uku wanda mota ta yi ajalinsu a lokaci guda da yammacin Juma'ar da ta gabata. Yaran da lamarin ya shafa wanda dukkansu mata ne, 'ya'yan mutum guda ne, kuma ajali ya cim musu ne a hanyarsu ta komawa gida bayan dawowa daga ziyarar gaisuwar sallah. Maihaifin yaran, Malam Sulaiman Ibrahim, ya yi wa MANHAJA ƙarin haske kan yadda lamarin ya faru inda ya ce, "Lamarin ya faru ne da…
Read More
Dara ta ci gida: An sace tsohon shugaban ’yan bindiga

Dara ta ci gida: An sace tsohon shugaban ’yan bindiga

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Wasu gungun mutane sanye da kayan sojoji sun yi garkuwa da wani shahararren tsohon shugaban tsagerun Ribas, High Chief Sobobo Jackrich, wanda aka fi sani da Egberipapa, daga gidansa na Usokun da ke Ƙaramar Hukumar Degema a Jihar Ribas. Majiyoyi na kusa da tsohon shugaban tsagerun sun ce 'yan bindigar sun kai farmaki gidansa ne da misalin ƙarfe 3:00 na safiyar ranar Litinin, inda suka kashe wasu hadimansa biyu tare da ɗauke shi zuwa wani wuri da ba a sani ba. Sai dai ɗaya daga cikin majiyar ta yi imanin cewa sojoji ne suka kai harin,…
Read More
Ƙarin kuɗin lantarki: Mataimakin Kakakin Majalisar Wakilai ya sha alwashin duba lamarin

Ƙarin kuɗin lantarki: Mataimakin Kakakin Majalisar Wakilai ya sha alwashin duba lamarin

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Mataimakin Kakakin Majalisar Wakilai, Benjamin Kalu, ya kwantarwa da ’yan Nijeriya hankali kan batun ƙarin farashin wutar lantarki da Gwamnatin Tarayya ta yi. Ben Kalu ya ce 'yan majalisar sun ƙudiri aniyar tafka muhawara kan ko ya kamata a yi ƙarin kuɗin wutar ko a'a. A cewar mai magana da yawun Kalu, Levinus Nwabughiogi, ɗan majalisar na amsa tambayar wani mai sauraro da ya yi kiran waya cikin shirin yana tambayar matsayar majalisa kan ƙarin kuxin wutar. Kalu ya ce, "Gama-garin matsala ce. Ina cikin hutu, amma daga abin da ke damu na akwai takardar da…
Read More
Kuɗin lantarki: Ma’aikatan lantarki sun yi barazana shiga yajin aiki a Zamfara

Kuɗin lantarki: Ma’aikatan lantarki sun yi barazana shiga yajin aiki a Zamfara

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Ƙungiyar Ma’aikatan Wutar Lantarki ta Ƙasa ta yi kira da a sake nazari a kan ƙarin kuɗin wutar lantarkin da aka yi a baya-bayan nan, inda ta yi barazanar shiga yajin aiki. A cikin wata sanarwa, shugaban ƙungiyar, Adebiyi Adeyeye, ya yi gargaɗin yiwuwar shiga yajin aikin matuƙar ba a sauya ba. Hukumar da ke sa ido kan wutar lantarki ta Nijeriya ta kara haraji ga kwastomomin da ke samun wutar lantarki na sa’o’i 20 a kullum, lamarin da ya haifar da ƙarin farashin.  Adeyeye ya bayyana rashin daidaiton tsarin a matsayin hanyar da ke kashe…
Read More
Gwamna Abba Kabir ya biya wa ɗalibai 6,500 kuɗin JAMB ‘yan asalin Jihar Kano

Gwamna Abba Kabir ya biya wa ɗalibai 6,500 kuɗin JAMB ‘yan asalin Jihar Kano

Daga RABIU SANUSI a Kano Gwamna Abba Kabir Yusuf na jihar Kano ya biya wa ɗalibai maza da mata da suka gama sakandire 'yan asalin Jihar Kano kuɗin jarrabawar share fagen shiga jami'a kimanin 6,500 don ci gaba da karatun su a kwalejoji da jami'o'i a ƙasar nan dama duniya gaba ɗaya. Gwamnan wanda ya fara da godiya ga iyayen yara bisa jajircewarsu wajen bai wa yaransu tarbiyya da tsayawa don ci gaban su ta hanyar ilimi. Maigirma Gwamna ya ce daga lokacin da aka zaɓi wannan gwamnati sun gudanar da ayyuka da dama ya zuwa yanzu, inda ya ce…
Read More
An kama matashi kan zargin kashe yayansa a Bauchi

An kama matashi kan zargin kashe yayansa a Bauchi

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Rundunar 'yan sanda jihar Bauchi ta kama wani matashi mai suna Isyaku Babale, bisa zargin daɓa wa yayansa wuƙa har lahira. Wata sanarwa da mai magana da yawun 'yan sandan jihar SP Ahmed Wakili ya fitar, ta ce binciken farko da suka gudanar, ya nuna cewa wanda ake zargin ya yi amfani da wuƙa wajen daɓa wa babban wansa mai suna Abubakar Ɓalewa ranar Lahadi, 31 ga watan Maris bayan cacar-baki da ta ɓarke tsakaninsu. Wakili ya ce bayan samun rahoton abin da ya faru ne, sai suka tura jami’ansu zuwa wurin, abin da…
Read More
Hajjin 2024: Gwamnatin Kebbi ta fitar da Naira biliyan 3.34 don tallafa wa maniyyatan jihar 3,344

Hajjin 2024: Gwamnatin Kebbi ta fitar da Naira biliyan 3.34 don tallafa wa maniyyatan jihar 3,344

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Gwamnatin jihar Kebbi ta ce ta amince da bayar da tallafin Naira biliyan 3.34 ga maniyyata 3,344 da ke son zuwa aikin Hajjin bana daga jihar. MANHAJA ta rawaito cewa an fitar da kuɗin ne don kammala biyan ƙarin kuɗin aikin Hajjin bana da ya kai kimanin Naira miliyan 1.9 da hukumar alhazai ta ƙasa NAHCON ta sanar. An cimma wannan matsayar ne a wani taron gaggawa na Majalisar Zartaswa da Mataimakin Gwamna, Umar Abubakar Tafida ya jagoranta, a Birnin Kebbi a ranar Litinin. Da ya ke jawabi ga manema labarai kan sakamakon taron,…
Read More