Rahoto

Asalin Fulani da shigarsu ƙasar Hausa

Asalin Fulani da shigarsu ƙasar Hausa

Daga MAHDI MUSA MUHAMMAD A ci gaba da kawo muku tarihin manyan ƙabilun Nijeriya, yau ma Jaridar Manhaja za ta yi duba kan ƙabilar Fulani, wadda ɗaya ce daga cikin manyan ƙabilu mafi yawan jama'a a Nijeriya. Tushen Fulani: Fulani dai ƙabila ce da tarihi ke turke asalinta tun ƙarni na 15 daga wasu manyan ’yankuna biyu da ke ƙasashen Senegal da kuma Guinea Conakry, wato Futa Toro da kuma Futa Jalloh. Daga nan ne suka ci gaba da bazuwa cikin ƙasashen duniya musamman yammaci da kuma tsakiyar nahiyar Afirka domin nema wa dabbobinsu abinci da kuma ingantacciyar rayuwa. Ko…
Read More
Gyaran wurin kiwo don ya daina wari a lokacin damina

Gyaran wurin kiwo don ya daina wari a lokacin damina

Tare da BILKISU YUSUF ALI, Ph’D Gabatarwa Kiwon dabbobi yana da muhimmanci ƙwarai da gaske kuma ana iya yin sa a wajen da ya dace a ko’ina amma rashin tsafta yana haifar da wari da cututtuka musamman lokacin damina. Don haka duk wanda yake kiwon dabbobi yana ruɓanya ƙoƙarinsa na tsafta ne don samun muhallin kiwo mai tsafta wanda ba zai cutar da kansa ba sannan ya cutar da makwabtansa ba da ma su dabbobin kansu. Ma'anar wurin kiwo Wurin kiwo shi ne wurin da ake renon dabbobi. Ya kamata ya kasance mai tsafta a bushe, da magudanar ruwa. Sannan…
Read More
Wacce wainar aka toya a taron ’yan midiya na Arewa?

Wacce wainar aka toya a taron ’yan midiya na Arewa?

Daga ABBA ABUBAKAR YAKUBU Ba da jimawa ba ne aka gudanar da wani taron matasa ’yan Arewa masu rubuce-rubuce a zaurukan sada zumunta, a wani yunƙuri na haɗa kan matasan maza da mata, ƙarfafa musu gwiwa, da kuma samar musu da wata alƙibla ta yadda rubuce-rubucen da suke yi za su riƙa samar musu da natija mai kyau. Ofishin babban mai bai wa shugaban ƙasa shawara kan harkokin watsa labarai da wayar da kai, Abdul'Aziz Abdul'Aziz ne ya shirya wannan taro, wanda aka gudanar a babban ɗakin taro na fadar gwamnatin Kano, a ranar Litinin 6 ga watan Yuli, 2026.…
Read More
Buhari ya bar Nijeriya cikin kyakkyawan yanayi – Hadi Sirika

Buhari ya bar Nijeriya cikin kyakkyawan yanayi – Hadi Sirika

Daga UMAR GARBA a Katsina Tsohon ministan sufurin jiragen sama, Sanata Hadi Sirika, ya bayyana cewa marigayi tsohon Shugaban ƙasa, Muhammadu Buhari, ya bar Nijeriya cikin yanayi na ci gaba, tare da ingantaccen tattalin arziki da tsaro mai kyau. Da yake magana a tashar ARISE TV, Sirika ya ce gwamnatin Buhari ta gaji matsaloli masu yawa, amma ta samu nasarori wajen yaƙi da Boko Haram, inda ta ƙwato ƙananan hukumomi 17 da 'yan ta'adda suka mamaye tare da ceto wasu daga cikin ɗaliban Chibok da aka sace. Ya kuma ce inganta tsaro ya bai wa al'umma damar komawa noma, zuwa…
Read More
Kotu ta bada belin Dr Bishir Kurfi don sauraron shari’a 13 ga Yuli

Kotu ta bada belin Dr Bishir Kurfi don sauraron shari’a 13 ga Yuli

Daga ABDULLAHI MUHAMMAD a Katsina Kotun majistare a Katsina ta bada belin Dr Bishir Kurfi zuwa 13 ga watan Yuli ranar da za ta cigaba da sauraran ƙarar da gwamnatin Jihar Katsina ta shigar tana zargin sa da ƙarya da ɓata su. A wata hira da gidan talabijin na Trust TV Dr Kurfi ya yi zargin cewa gwamnatin Jihar Katsina ta ɗauki nauyin 'yan bindiga zuwa aikin hajji wanda gwamnatin ta ƙaryata ta kuma buƙaci Dr Kurfi ya janye ƙazafin da ya yi. Lauyan wanda ake ƙara Barista AD umar ya bayyana wa manema labarai bayan da aka fito daga…
Read More
Karamar Hukumar Dandi ta nuna damuwa kan rashin waƙilci nagari

Karamar Hukumar Dandi ta nuna damuwa kan rashin waƙilci nagari

Daga JAMIL GULMA a Kebbi Wasu al’ummar ƙaramar Hukumar Mulki ta Dandi da ke Jihar Kebbi sun bayyana damuwarsu kan abin da suka bayyana a matsayin rashin ingantaccen wakilci daga ɗan majalisar da ke wakiltar mazabar Arewa/Dandi a Majalisar Wakilai ta Tarayya. Daya daga cikin shugabannin matasa a yankin, Malam Hashimu Musa Buma, ya bayyana cewa akwai buƙatar sake nazari kan wakilcin Hon. Garba Rabi’u Kamba, wanda ke wakiltar ƙananan hukumomin Arewa da Dandi, yana mai zargin cewa wakilcin bai kai yadda al’umma ke tsammani ba. Ya ce ya kamata a yi la’akari da ra’ayin jama’a da kuma ƙarfafa shugabanci…
Read More
Gwamnatin Tinubu ta samu rancen Dala biliyan 11.4 daga Bankin Duniya a shekaru uku

Gwamnatin Tinubu ta samu rancen Dala biliyan 11.4 daga Bankin Duniya a shekaru uku

Daga MAHDI MUSA MUHAMMAD Wani rahoto ya nuna cewa Gwamnatin Tarayya ƙarƙashin jagorancin Shugaba Bola Ahmed Tinubu ta samu amincewar ciyo rancen da ya kai dala biliyan 11.4 daga Bankin Duniya cikin shekaru uku na farko da ta yi kan mulki, lamarin da ya kusantar da ita ga zarce adadin dala biliyan 14.59 da aka amince wa Nijeriya a zamanin tsohon shugaban ƙasa, Muhammadu Buhari, na tsawon shekaru takwas. Binciken bayanan Bankin Duniya ya nuna cewa daga watan Yunin 2023 zuwa Yunin 2026, Nijeriya ta samu amincewar rancen da ya kai dala biliyan 11.4, wanda ya kai kusan kashi 78…
Read More
Ba takardar digiri kaɗai ake buƙata a jami’a ba – Shettima

Ba takardar digiri kaɗai ake buƙata a jami’a ba – Shettima

Daga MAHDI MUSA MUHAMMAD Mataimakin Shugaban ƙasa, Sanata Kashim Shettima, ya ce lokaci ya yi da jami'o'in Nijeriya za su sauya salon aikinsu ta hanyar zama cibiyoyin ƙirƙire-ƙirƙire, kasuwanci da bunƙasa masana'antu, maimakon mayar da hankali kan fitar da masu takardun shaida kawai. Shettima ya bayyana hakan ne yayin ƙaddamar da cibiyar Manufacturing Technology Uniɓersity Innoɓation Pod (Manu-Tech UniPod) a Jami'ar Noma ta Michael Okpara da ke Umudike, ƙaramar hukumar Ikwuano a Jihar Abia. An kafa cibiyar ne domin haɓaka ƙirƙire-ƙirƙire a fannin fasaha da kuma bunƙasa harkokin kasuwanci. Shirin haɗin gwiwa ne tsakanin Shirin Raya ƙasashe na Majalisar ɗinkin…
Read More
Dangote zai gina babbar matatar mai a Kenya

Dangote zai gina babbar matatar mai a Kenya

Daga MAHDI MUSA MUHAMMAD Rukunin Kamfanonin Dangote ya bayyana shirinsa na samar da kuɗaɗen gina sabuwar matatar mai mai ƙarfin tace ganga 700,000 a kowace rana a ƙasar Kenya, ta hanyar haɗa kuɗaɗen shiga na cikin gida, fitar da takardun bashin gwamnati da kuma kuɗaɗen da ake sa ran samu daga sayar da hannayen jari ga jama'a (IPO). Sabuwar matatar, wadda za a gina a Tsibirin Lamu da ke gabar tekun Kenya, ana sa ran za ta kasance mafi girma a Gabashin Afirka, tare da taimakawa wajen ƙarfafa tsaron makamashi a yankin ta hanyar rage dogaro da shigo da tataccen…
Read More
Akanza ya yabi Tinubu da Gwamna Sule kan ayyukan hanyoyi

Akanza ya yabi Tinubu da Gwamna Sule kan ayyukan hanyoyi

Daga JOHN D WADA a Lafia Shugaban yankin raya Lafia ta Arewa Hon. Nasiru Kasimu Akanza ya yaba wa shugaba Bola Ahmed Tinubu da gwamna Abdullahi Sule na jihar Nasarawa bisa ayyukan hanyoyi da ake cigaba da yi, yana mai cewa ayyuka ne na tarihi da za su inganta cigaban tattalin arziki da sauƙaƙe zirga-zirga a faɗin ƙasa. Da yake tattaunawa da manema labarai a ofishinsa da ke Shabu na ƙaramar hukumar Lafia, Akanza ya yaba da ƙaddamar da aikin babbar hanyar Akwanga zuwa Jos da Gombe da Maiduguri da kuma buɗe hanyar kilomita 3 mai layi biyu da aka…
Read More