Rahoto

An kama mai sayar da yalo kan zargin yi wa yaro fyaɗe a Bauchi

An kama mai sayar da yalo kan zargin yi wa yaro fyaɗe a Bauchi

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Jami'an 'yan sandan jihar Bauchi da ke aiki ƙarƙashin rundunar maido da zaman lafiya sun kama matashi mai shekara 23 da ake zargin ya yi wa wani yaro ɗan shekara goma fyaɗe. Matashin da ake zargi ya yaudari yaron da naira 30 da alawa inda ya nemi yaron ya raka shi wani kango da ke bayan wani gidan mai a kan titin Kofar Ran domin ya yi bahaya. Sanarwar da kakakin rundunar 'yan sandan Bauchi, SP Ahmed Mohammed Wakil ya fitar ta ce bayan ya yi bahayar ne kuma, matashin ya bukaci yaron da…
Read More
Hajjin 2024: Gwamnan Jigawa ya bada tallafin Naira miliyan ɗaya ga kowane maniyyacin jihar

Hajjin 2024: Gwamnan Jigawa ya bada tallafin Naira miliyan ɗaya ga kowane maniyyacin jihar

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Gwamnan Jihar Jigawa Umar Namadi ya sanar da bayar da tallafin Naira miliyan ɗaya ga maniyyata aikin Hajji daga jihar. Kakakin hukumar jin daɗin alhazai ta jihar Jigawa Murtala Usman ne ya sanar da hakan ga manema labarai a ranar Litinin. Usman ya ce an bayar da tallafin ne ga maniyyatan Jigawa da suka fara ajiyar kuɗaɗen aikin Hajjin su na 2024 tun a baya. “Kowane maniyyaci yanzu zai biya cikon Naira 900,000 kawai saɓanin Naira miliyan 1.9 da Hukumar Alhazai ta Nijeriya (NAHCON) ta sanar. “Tun da farko hukumar ta NAHCON ta ware…
Read More
Sama da shanu 300 aka sace mana cikin makonni uku a Jihar Filato – Makiyaya

Sama da shanu 300 aka sace mana cikin makonni uku a Jihar Filato – Makiyaya

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Makiyaya a Ƙaramar Hukumar Bokkos da ke Jihar Filato, sun koka cewa ɓarayin shanu sun arce musu shanu sama da 390 da kudin su ya kai aƙalla Naira miliyan 300. Makiyayan sun ce an yi awon gaba da shanun a lokacin da suke kiwo a Bot, Faranti, Anguwan Abuja, Makada da Wumat. Manhaja ta buga cewa shugaban ƙungiyar ci gaban Fulani na ‘Gan Allah’ dake qaramar hukumar Bokkos Saleh Adamu ya ce sun kai ƙarar abinda aka yi musu zuwa ga kwamandan sashin ‘Operation Safe Haven’ da ke yankin. “A ranar 4 ga Maris,…
Read More
Sabuwar manhajar KIPPIS za ta bada cikakkun bayanai akan ma’aikatan Kano – AG Abdulkadir

Sabuwar manhajar KIPPIS za ta bada cikakkun bayanai akan ma’aikatan Kano – AG Abdulkadir

Daga MUHAMMADU MUJITABA a Kano Akanta Janar na Jihar Kano, Abdulqadir Abdulsalam ya bayyana cewa ƙirƙiro da manhaja KIPPIS da gwamnatin Jihar Kano ta yi zai taimaka wajen samun cikakkun bayanan ma'aikatan jihar. Abdulsalam ya bayyana hakan ne ranar Talata lokacin da yake yi wa manema labarai ƙarin haske bayan kammala taron kwana biyu kan yadda sabuwar manhajar tattara bayanai na ma'aikatan Kano da ake kira KIPPIS da aka yi a jihar Kano wanda ya ƙunshi ofishin Akanta Janar da Ofishin kula da ma'aikatan Kano da ofishin binciken kuɗi na Kano da ofishin kula da biyan albashi da gwamnan Jihar…
Read More
Yadda sabbin gwamnoni 13 suka kinkimi bashin N226.8bn a cikin wata shida – DMO

Yadda sabbin gwamnoni 13 suka kinkimi bashin N226.8bn a cikin wata shida – DMO

Daga BASHIR ISAH Bayabnan da Manhaja ta tattaron sun ce, a jimilIance wasu sabbin gwamnoni su 13 sun ci bashi da ya kai Naira Biliyan 226.8 a cikin watanni shida da suka yi a ofis. Wannan bashin kuwa ya shafi wanda gwamnonin suka ci a gida da kuma ƙetare. Binciken News Point Nigeria ya gano cewa, wasu gwamnonin jihohi 16 kuma, basussukan da suka ciyo ya ƙaruwa da Naira Biliyan 509.3. An yi lissafin basussukan ƙetaren ne kan lissafin N889 kan $1 kamar yadda Ofishin Kula da Basussuka (DMO) ya nuna. Rahoton DMO ya ce an tattaro bayanan basussukan ne…
Read More
Cikakken bayanin yadda Tinubu ya kafa Majalisar Havaka Tattalin Arzikin Nijeriya

Cikakken bayanin yadda Tinubu ya kafa Majalisar Havaka Tattalin Arzikin Nijeriya

Daga MAHDI M. MUHAMMAD A wani muhimmin mataki na ƙarfafa tsarin tafiyar da tattalin arzikin qasa da tabbatar da tsayayyen tsare-tsare da aiwatar da tattalin arzikin ƙasa cikin aminci, Shugaban Nijeriya, Bola Ahmed Tinubu, ya amince da ya kafa Kwamitin Kula da Tattalin Arzikin Ƙasa na Shugaban Ƙasa (PECC) da kuma samar da Ƙungiyar Kula da Tattalin Arziki ta Gaggawa (EET). A cewar wata sanarwa mai ɗauke da sa hannun Ajuri Ngelale, mai ba shugaban ƙasa shawara na musamman kan kafafen yaɗa labarai da wayar da kan jama'a, kwamitin kula da tattalin arzikin shugaban ƙasa (PECC) ya ƙunshi fitattun shugabanni…
Read More
Gidauniyar Ɗangote ta ƙaddamar da tallafin kayan abinci a Kano

Gidauniyar Ɗangote ta ƙaddamar da tallafin kayan abinci a Kano

Daga IBRAHIM HAMISU a Kano Gwamnan jihar Kano Injiniya Abba Kabir Yusuf, ya jagoranci ƙaddamar da rabon tallafin kayan abinci da Gidauniniyar Dangote za ta raba wa al’ummar Nijeriya domin rage musu raɗaɗin rayuwa da suke fuskanta. Da yake ƙaddamar da rabon tallafin a gidan Gwamnatin Kano a ranar Asabar, Gwamna Abba Kabir Yusuf, ya yi kira ga kwamitin da za su gudanar da rabon kayan abincin su zamo masu gaskiya da riƙon amana, tare da tabbatar da tallafin ya isa ga mabuƙatan da aka tanadi abincin domin su. Yusuf ya kuma ce tuni tallafin kayan abincin ya isa ga…
Read More
Ɗaliban Kuriga sun shaƙi iskar ‘yanci

Ɗaliban Kuriga sun shaƙi iskar ‘yanci

Daga BASHIR ISAH Bayanai daga Jihar Kaduna na nuni da cewa, ɗaliban firamaren da aka yi garkuwa da su kwanan baya a yankin Kuriga a jihar, sun shaƙi iskar 'yanci. Gwamnan Jihar, Sanata Uba Sani, shi ne ya ba da sanarwar hakan a shafinsa na Facebook ranar Asabar da tsakar dare Idan za a iya tunawa, MANHAJA ta rawaito a ranar 8 ga Maris wasu 'yan bindiga suka kai hari yankin Kuriga, cikin Ƙaramar Hukumar Chilun a jihar Kaduna, inda suka yi awon gaba da yara sama da 200. Sai dai Gwamnan bai yi wani cikakken bayani kan sako yaran…
Read More
Kayan miliyoyin Naira sun kone a gobarar kasuwar Legas

Kayan miliyoyin Naira sun kone a gobarar kasuwar Legas

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Kayayyaki da darajarsu ta kai na miliyoyin Naira sun kone kurmus a ranar Larabar da ta gabata, yayin da wata gobara ta tashi a wasu shaguna a sashen Nnamdi Azikiwe da Docemo na Kasuwar Idumota a Jihar Legas. Gobarar ta shafi gine-gine guda uku da suka haɗa da benaye biyu da wani gini mai hawa uku a kasuwar waɗanda suka shahara  wajen sayar tufafi da jaka da takalma. Hukumar kashe gobara ta jihar Legas da sauran masu bada agajin gaggawa sun isa wurin, inda suka yi ta koƙarin aikin kashe gobarar. "Hukumomin kashe gobara a Ebute…
Read More
Tinubu zai tsige ministocin da suka gaza kataɓus

Tinubu zai tsige ministocin da suka gaza kataɓus

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Shugaban Nijeriya Bola Tinubu yana shirin fara wani tsari mai matakai uku domin tantance ƙoƙarin ministoci, shugabannin ma’aikatu da hukumomin gwamnati. Manufar ita ce samar da wani shafi da zai ba jama'a damar yin bayanai game da koƙarin ministocin da ba da shawarar waɗanda za a riƙe da waxanda za a kora. Wannan yunkuri na zuwa ne yayin da Gwamnatin Tinubu ke tunkarar bikin cika shekara gyda a kan madafun iko a ranar 29 ga Mayu, 2024. Wasu majiyoyi masu ƙarfi a fadar shugaban kasa sun ce Shugaban kasar Tinubu zai ƙaddamar da wannan shafi ne…
Read More