Rahoto

SERAP ta buƙaci kotu ta dakatar da ƙarin kuɗin kiran waya zuwa kashi 50

SERAP ta buƙaci kotu ta dakatar da ƙarin kuɗin kiran waya zuwa kashi 50

Daga MAHDI MUSA MUHAMMAD Kungiyar da ke fafutukar yaƙi da cin hanci da rashawa da kare hakkin ɗan adam ta SERAP, ta maka Shugaba Bola Tinubu da Hukumar Sadarwa ta Nijeriya (NCC), a kotu kan karan kuɗin kiran waya, saƙon tes da data zuwa kashi 50. NCC ta amince da ƙarin, wanda ya sa kuɗin kiran waya ya tashi daga Naira takwas zuwa 16.5 a minti ɗaya, yayin da kudin sayen data 1GB ya tashi daga Naira 287.8 zuwa Naira 431.25. Shi kuwa kuɗin aika saƙon tes ya tashi zuwa Naira 6 daga na huɗu da ake biya a baya.…
Read More
KACRAN ta buƙaci Hukumar Raya Yankin Arewa Maso Gabas ta inganta harkar kiwon dabbobi

KACRAN ta buƙaci Hukumar Raya Yankin Arewa Maso Gabas ta inganta harkar kiwon dabbobi

Daga MAHDI MUSA MUHAMMAD Kungiyar Fulani Makiyaya a Nijeriya ta Kulen Allah (KACRAN) ta yi kira ga Hukumar Raya Yankin Arewa Maso Gabas da ta ci gaba da yin tsare-tsaren da take yi na ganin an inganta harkar kiwon dabbobi da kuma ɗabbaƙa cigaban yankin na Arewa maso Gabas. Wata sanarwa da ƙungiyar ta fitar wanda ya samu sa hannun shugabanta, Khalil Moh’d Bello, KACRAN ta yaba wa hukumar ta NEDC bisa ƙoƙari wajen ganin an samu zaman lafiya da sake ginda al'ummomi da kuma taimakawa makiyaya, inda ya kwatanta hukumar a matsayin abin koyi. "Hukumar raya yankin arewa maso…
Read More
An sake zaɓar Mai’adua a matsayin shugaban NULGE na Katsina 

An sake zaɓar Mai’adua a matsayin shugaban NULGE na Katsina 

Daga ABDULLAHI MUHAMMAD a Katsina Ƙungiyar Ma'aikatan ƙananan Hukumomi ta ƙasa (NULGE) reshen jihar Katsina ta sake zaɓen Nasiru Wada Mai'adua a matsayin shugabanta tare da wasu mutane 12 a karo na biyu da za su cigaba da jagorantar ƙungiyar nan da shekara 3. Zaɓen da ya gudana a hedkwatar ƙungiyar da ke Katsina an bi ta hanyar sasantawa a tsakanin yan takara kamar yadda tsarin mulkin ƙungiyar ya tanada. A jawabin sa bayan bayan kammala zaɓen gwamna Dikko Raɗɗa wanda ya sami wakilci na sakataren gwamnatin jihar Abdullahi Garba Faskari ya tabbatar da gwamnati za ta cigaba da aiki…
Read More
Muna fatan a ci gaba da samun sauƙin kayayyaki – Mataimakin Shugaban ƙungiyar Kasuwar Singa

Muna fatan a ci gaba da samun sauƙin kayayyaki – Mataimakin Shugaban ƙungiyar Kasuwar Singa

Daga IBRAHIM MUHAMMAD Ambasada Dakta Bashir Yusuf Abdullahi, Mataimakin Shugaban ƙungiyar Kasuwar Kwanar Singa da aka fi sani da 'SIMDA', ya bayyana cewa, a halin da ake ciki yanzu Allah na  kawo sauƙi na farashin kayan masarufi yana raguwa duba da duk shekara akwai yanayi ake samu, wannan shekara Allah ya kawo sauƙi tun daga yanzu akan kayan amfanin yau da kullum na al'umma. Ya bayyana haka ne da yake zantawa da ’yan jarida  ya  ce su  kansu yan kasuwa suna  kuka  da cewa kaya ba sa sayuwa sai ma faɗuwa da suke saboda tsada, sannan wani lokacin ma irin…
Read More
Yadda za a kawo ƙarshen cin zarafin mata

Yadda za a kawo ƙarshen cin zarafin mata

Daga ABBA ABUBAKAR YAKUBU Gwagwarmayar yaƙi da cin zarafin mata ta kwanaki 16 da aka saba gudanarwa duk shekara ta zo ta wuce, amma ba za a iya daina magana kan cin zarafi, cin zali da tauye haƙƙin da ake yi wa 'ya'ya mata ba. Har sai ranar da aka wayi gari aka ce yau mata suna rayuwa cikin 'yanci da kwanciyar hankali tare da maza abokan rayuwarsu, babu fargaba ko tsoron wani abu, ba a nan Nijeriya kaɗai ba har ma da duniya bakiɗaya. ƙungiyoyin mata daban-daban a ƙasar nan sun shiga cikin wannan gangami na kwanaki 16 da…
Read More
Zamfara: Ku kasance masu ɗa’a ga masu masaukinku, shugaban NYSC ga ‘yan hidimar ƙasa

Zamfara: Ku kasance masu ɗa’a ga masu masaukinku, shugaban NYSC ga ‘yan hidimar ƙasa

Daga SANUSI MUHAMMAD Gusau An shawarci masu yiwa Ƙasa hidima a Jihar Zamfara da su mutunta al’adun al’ummar da suke zaune tare su da yin amfani da lokacin hidimar Ƙasar wajen samar da wani tsaro mai ma’ana ga rayuwar al’ummar jihar. Darakta-Janar na NYSC, Birgediya Janar YD Ahmed, ya ba da wannan shawarar a ranar Asabar a lokacin da yake jawabi ga mambobin Batch C Stream II na 2024 dake karɓar horo yiwa ƙasa hidima a Gusau . Shugaban masu yi wa kasa hidima na ya bayyana cewa ɗaya daga cikin manyan maƙasudin shirin shi ne ƙarfafa haɗin kai a…
Read More
Farfesa Usman Yusuf zai zauna hannun EFCC bayan ɗage shari’a

Farfesa Usman Yusuf zai zauna hannun EFCC bayan ɗage shari’a

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Babbar kotun birnin tarayya, Kuje, ta ɗage gurfanar da tsohon babban sakataren hukumar inshorar lafiya ta ƙasa, Farfesa Usman Yusuf zuwa ranar Litinin 3 ga watan Fabrairu, 2025. Yusuf wanda hukumar yaƙi da masu yi wa tattalin arzikin ƙasa zagon ƙasa ta kama a ranar Laraba 29 ga watan Junairu, 2025, an gurfanar da shi a gaban mai shari’a Chinyere E. Nwecheonwu a ranar Alhamis domin gurfanar da shi a gaban kuliya bisa zargin zamba. Sai dai kotun ta ɗage ci gaba da sauraren ƙarar don ba da damar yin kwaskwarima ga tuhume-tuhumen. Sanarwar…
Read More
‘Yan siyasa na yin ko-a-mutu-ko-a-yi-rai don nasara – Amaechi

‘Yan siyasa na yin ko-a-mutu-ko-a-yi-rai don nasara – Amaechi

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Rotimi Amaechi, tsohon ministan sufuri, ya ce Shugaba Bola Tinubu ba zai ba matasan Najeriya mulki salin-alin  ba sai an kai ruwa rana. Ya ƙara da cewa ‘yan siyasa su na amfani da hanyoyin ko a mutu ko a yi rai don cin zabe. Tsohon gwamnan Jihar Ribas ɗin ya bayyana hakan ne a Abuja yayin wani taro kan ƙarfafa dimokuraɗiyya a Nijeriya, wanda Cibiyar 'African Centre for Leadership, Strategy and Deɓelopment' ta shirya. Amaechi ya jaddada buƙatar kula da harkokin siyasa, yana gargaɗin cewa dole ne a yi gwagwarmaya don samun mulki, tare…
Read More
Nijeriya ta kori baƙin haure 828, ta ƙarfafa tsaron iyakokinta

Nijeriya ta kori baƙin haure 828, ta ƙarfafa tsaron iyakokinta

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Gwamnatin Tarayya ta ce ta kori baƙin haure 828 daga ƙasar a shekarar 2024 a wani ɓangare na ƙoƙarin da ta ke na yaƙi da ‘yan ci-rani da inganta tsaron ƙasa. Ministan harkokin cikin gida Olubunmi Tunji-Ojo ne ya bayyana hakan a wani taron manema labarai a Abuja ranar Talata. Da yake ƙarin haske kan nasarorin da gwamnati ta samu, Ministan ya bayyana cewa, “A cikin shekara ɗaya da ta gabata, an kama mutane 137 da aka yi safarar su, kuma a shekarar 2024 kaɗai, Hukumar Kula da Shige da Fice ta Nijeriya ta…
Read More
Yadda taƙaddama ta kaure tsakanin Gwamnan Bauchi da Yusuf Tuggar

Yadda taƙaddama ta kaure tsakanin Gwamnan Bauchi da Yusuf Tuggar

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Ministan harkokin wajen Nijeriya, Yusuf Maitama Tuggar ya mayar wa gwamnan jihar Bauchi, Bala Mohammed martani bisa wasu kalamai da gwamnan ya yi a kan shi. Hakan na zuwa ne kwana ɗaya bayan BBC ta sanya tattaunawar da ta yi da gwamnan na jihar Bauchi, inda ya kare manufofinsa tare da mayar da martani kan sukar da ministan ya yi wa gwamnatin jihar. 'yan siyasan biyu dukkaninsu sun fito ne daga jiha ɗaya - Bauchi - da ke arewa maso gabashin Nijeriya, kuma sun daɗe suna jan zarensu a harkar siyasa. A wata tattaunawa…
Read More