06
Jul
Daga JAMIL GULMA a Kebbi Babbar kotun tarayya da ke zama a birnin Abuja ta amince da ɗage ranar yanke hukunci na ƙarshe dangane da ƙarar da hukumar yaƙi da yi wa tattalin arzikin ƙasa ta'annati (EFCC) ta shigar, tana neman a ba ta damar ƙwace wasu manyan ƙadarori guda hamsin da bakwai (57) na tsohon ministan shari’a kuma babban lauyan ƙasa (AGF), Abubakar Chika Malami (SAN).Alƙalin kotun, mai shari’a Emeka Nwite, ne ya sanar da ɗage zaman bayan da lauyoyin ɓangarorin biyu suka kammala gabatar da hujjojinsu na ƙarshe a gaban kotun. Hukumar EFCC tana neman babban hukunci na…
