Rahoto

Shin ko kasan saka takalma marasa kyau na lalata ƙafa?

Shin ko kasan saka takalma marasa kyau na lalata ƙafa?

Daga AISHA ASAS  Mai karatu barkanmu da sake kasancewa a shafin Kwalliya na jaridar Blueprint Manhaja. Sannunku da jimirin bibiyar mu.  Na san mai karatu zai iya ɗan saka alamar tambaya kan darasin namu, wato kalamar 'takalma mai kyau'. Idan tunaninka ya tafi kan tsari na kyau da ake gani a zahiri ne, to ka dawo baya, hakan zai sa ka fahimci inda darasin namu ya dosa. Takalma masu kyau da muka ambata na magana ne kan takalma masu bada lafiya, ba masu wahalar da ƙafa ba. Akwai takalma da muke wa laƙabi da 'orthopedic shoes' su musamman an gina…
Read More
Yadda cutar damuwa ta iyaye ke shafar ‘ya’yansu 

Yadda cutar damuwa ta iyaye ke shafar ‘ya’yansu 

Daga AISHA ASAS Mai karatu, barkanmu da sake saduwa a shafin Iyali na jaridar Blueprint Manhaja. A wannan mako za mu tattauna wani muhimmin batu da duk da girman tasirinsa ga rayuwar iyali, ba kasafai ake ba shi kulawar da ta dace ba, musamman a Arewacin Najeriya. Batu ne da ya shafi lafiyar ƙwaƙwalwa, musamman cutar damuwa (anɗiety) da kuma baƙin ciki mai tsanani (depression). A gidaje da dama, akwai matsalolin da ba sa bayyana a ido, amma suna girgiza zaman lafiyar iyali. Cutar damuwa da baƙin ciki na daga cikin irin waɗannan matsaloli. Mutane da yawa na rayuwa da…
Read More
Tarihin Muhammadu Kanta, wanda ya assasa Daular Kabi (II)

Tarihin Muhammadu Kanta, wanda ya assasa Daular Kabi (II)

Daga JAMIL GULMA a Kebbi Bayan da Muhammadu Kanta ya samu nasarar tabbatar da 'yancin Daular Kabi, ya mayar da hankali wajen faɗaɗa mulkinsa. A cewar masana tarihi, mulkinsa ya bazu zuwa manyan yankuna na ƙasar Hausa da wasu sassan Yammacin Afirka. A gabas, iyakar mulkinsa ta kai har yankin Nguru, a masarautar Borno ta tsohon lokaci. A yamma kuma ya miƙa ikonsa zuwa yankunan da suka yi iyaka da tsohuwar Daular Oyo. A arewa kuwa, ya mamaye yankunan Arewa, Zabarma da wasu sassan da yanzu suke cikin Jamhuriyar Nijar. Haka kuma ya shimfiɗa ikonsa zuwa wasu yankunan da yanzu…
Read More
Majalisar Dokokin Katsina ta buƙaci gwamnati ta gyara muhimman hanyoyi

Majalisar Dokokin Katsina ta buƙaci gwamnati ta gyara muhimman hanyoyi

Daga ABDULLAHI MUHAMMAD a Katsina A zaman majalisar dokokin na ranar ƙarƙashin jagoranci mataimakin kakakin majalisar Rt Hon. Abduljalal Haruna Runka, majalisar ta gabatar da ƙuduri na tunatar da ɓangaren zartarwa na gwamnatin jihar, kan buƙatar sake gina wasu muhimman hanyoyi da suka lalace domin sauƙaƙa zirga-zirga da bunƙasa tattalin arziƙin al'ummomin da abin ya shafa. A ƙudurin da Hon. Umar Ali Bindawa, ɗan majalisa mai wakiltar ƙaramar hukumar Bindawa, ya gabatar, inda ya buƙaci majalisa ta turawa ɓangaren zartarwa da ta sake gina hanyar Bindawa, Dallaje, Doro Geremawa zuwa Kwanar Duwan. Hanyar wadda ta ratsa ƙananan hukumomin Bindawa da…
Read More
Zaɓen gwaji na hukumar INEC

Zaɓen gwaji na hukumar INEC

Hukumar Zaɓe ta ƙasa Mai Zaman Kanta (INEC) ta sanar da cewa za ta gudanar da zaɓen gwaji gabanin babban zaɓen ƙasa. Wannan mataki ya haifar da muhawara, inda wasu ke ganin tamkar wata alama ce da za ta iya bayyana ko za a samu gaskiya da adalci a zaɓe ko akasin haka. Akwai kuma masu nuna rashin amincewa da shugabancin shugaban INEC, bisa wasu kalaman da ake zargin ya taɓa furtawa tun kafin ya hau kan wannan muƙami. Wasu na fargabar cewa hakan na iya sa a yi duk mai yiwuwa wajen bai wa gwamnati mai ci goyon baya…
Read More
Waƙa:Ta’aziyyar Hauwa Ƙamshi

Waƙa:Ta’aziyyar Hauwa Ƙamshi

Dags MUHAMMED BALA GARBA  1. Rabbana Sarki Ilahu,       Rabbi mai tayar da ruhu,    Rabbi ga baiwarka Hauwa. 2. Babu mai tsarki ya naka,  Babu mai rahama kamarka, Rabbi kai rahama ga Hauwa.  3. Babu mai jin ƙai kamarka,          Babu mai tausai irinka,   Don Rasulu ka dubi Hauwa. 4. Duk Karamci na wurinka,         Ragwame ita ce sifarka,   Rabbi rangwantawa Hauwa. 5. Yadda duk kayi babu mita,        Ba mu jayayya da yin ka, Rabbi kai rahama ga Hauwa. 6. Hauwa Ƙamshi jaruma ce,       Babu shakka malama ce,     Mai rubuce-rubuce Hauwa. 7. Rabbi duk an mata shaida,               Kamila ce mai ibada,      Sayyada laƙabi…
Read More
Cikakken jerin sunayen waɗanda suka yi nasara a zaɓen Kungiyar Lauyoyin Nijeriya na 2026

Cikakken jerin sunayen waɗanda suka yi nasara a zaɓen Kungiyar Lauyoyin Nijeriya na 2026

Daga MAHDI MUSA MUHAMMAD An bayyana cikakken sakamakon zaɓen shugabannin ƙasa na ƙungiyar Lauyoyin Nijeriya (NBA) na shekarar 2026, bayan kammala zaɓe da kuma sanar da sakamakon da Kwamitin Gudanar da Zaɓen NBA (ECNBA) ya yi a ranar Lahadi. Kamar yadda aka ruwaito a baya, Babbar Lauya mai Matsayin SAN, Misis Oyinkansola Badejo-Okusanya, ta zama shugabar NBA ta 33 bayan ta doke sauran manyan lauyoyi biyu da suka fafata da ita a zaɓen shugaban ƙungiyar. Shugaban Kwamitin Gudanar da Zaɓen NBA (ECNBA), Aham Ejelam (SAN), ne ya sanar da sakamakon a hedikwatar ƙungiyar da ke Abuja. Badejo-Okusanya ta samu ƙuri'u…
Read More
Shehu bai ƙwace ƙasar kowa ba!

Shehu bai ƙwace ƙasar kowa ba!

Daga NASIRU ADAMU EL-HIKAYA Sam Shehu Mujaddadi bai ƙwace ƙasar kowa ba, hasalima waɗanda su ka karɓi tuta ‘yan asalin yankin da su ke sarauta ne. Shehu Mujaddadi Bagobiri ne ko ɗan Gobir a matsayin mahaifarsa a ƙasarsa ta gado Wallahi akwai takaici da ban mamaki wani dan kwangilar AIFOB ko na makiya Arewa wanda ba shi ma da alaƙa ta kusa ko nesa da Hausawa; ya rubuta wai Shehu Mujaddadi ya ƙwace ƙasar Hausa ko ya yaƙi wani Sarki da sauran shirmen makirci da sai a soshiyal midiya dandalin bulus na Bello Badum a ke gani. In ka deɓe…
Read More
Duk da saukar hauhawar farashi, jihohi 19 da Abuja sun ci gaba da fuskantar tsaiko – NBS

Duk da saukar hauhawar farashi, jihohi 19 da Abuja sun ci gaba da fuskantar tsaiko – NBS

Daga MAHDI MUSA MUHAMMAD Duk da cewa adadin hauhawar farashin kayayyaki a matakin ƙasa ya ɗan ragu a watan Yunin 2026, rahoton Hukumar ƙididdiga ta ƙasa (NBS) ya nuna cewa mazauna fiye da rabin jihohin Nijeriya na ci gaba da fama da matsanancin tashin farashi, inda jihohi 19 tare da Babban Birnin Tarayya Abuja, suka yi rajistar hauhawar farashi da ta zarce kashi 30 cikin ɗari. Sabon rahoton Ma’aunin Farashin Mabuƙaci (CPI) da hukumar ta fitar ya nuna cewa hauhawar farashin kayayyaki ta sauka kaɗan daga kashi 15.93 cikin ɗari da aka samu a watan Mayu zuwa kashi 15.91 cikin…
Read More
Trump ya jinjina wa Tinubu kan yaƙi da ta’addanci

Trump ya jinjina wa Tinubu kan yaƙi da ta’addanci

* Ya yi alƙawarin ƙarfafa haɗin gwiwa da Nijeriya Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Shugaban ƙasar Amurka, Donald Trump, ya yaba wa Shugaba Bola Ahmed Tinubu kan abin da ya bayyana a matsayin jajircewarsa wajen yaƙi da ta'addanci da magance matsalolin tsaro a Nijeriya, musamman hare-haren da ake kai wa al'ummomin Kiristoci. Yabon na ƙunshe ne cikin wata wasiƙa mai ɗauke da kwanan watan 6 ga Yulin 2026, wadda Trump ya aikewa Tinubu, kuma Fadar Shugaban ƙasa ta fitar da ita ga manema labarai ranar Laraba ta bakin Mai Bai wa Shugaban ƙasa Shawara na Musamman kan Yaɗa Labarai…
Read More