Rahoto

Yadda aka yi maulidin Sheikh Ahmadu Tijjani na 2026 ƙarƙashin Khalifa Ibrahim Dahiru Bauchi a Kano

Yadda aka yi maulidin Sheikh Ahmadu Tijjani na 2026 ƙarƙashin Khalifa Ibrahim Dahiru Bauchi a Kano

Daga BILKISU YUSUF ALI a Kano An gudanar da babban taron maulidin Sheikh Ahmad Tijjani a birnin Kano, wanda gidauniyar Sheikh Dahiru Usman Bauchi Foundation ta saba shiryawa duk shekara don tunawa da ranar haihuwar Shehi Ahmadu Tijjani da irin gudummawar da ya bayar wajen yaɗa addinin Musulunci da ɗariƙar Tijjaniyya a duniya. Taron ya kasance babban taro na addini mai ɗauke da tarihi da muhimmanci ga al’ummar Musulmi, musamman mabiya ɗariƙar Tijjaniyya.  Taron, wata muhimmiyar dama ta tunatarwa da ilimintarwa da ƙarfafa zumunci tsakanin al’ummar Musulmi. Haka kuma, ya sake tabbatar da matsayi da muhimmancin birnin Kano a matsayin…
Read More
Bankin Lotus ya shiga tsaka-mai-wuya da hukumar NDPC kan zargin ɗaukar bayanan ɗalibai

Bankin Lotus ya shiga tsaka-mai-wuya da hukumar NDPC kan zargin ɗaukar bayanan ɗalibai

Daga MAHDI MUSA MUHAMAMD Bankin Lotus ya shiga tsaka mai wuya bisa fuskantar binciken ƙwararru daga Hukumar Kare Bayanai ta Nijeriya (NDPC) bisa zargin cewa an yi amfani da bayanan sirri na wasu ɗalibai ba bisa ƙa’ida ba wajen buɗe musu asusun banki ba tare da ingantaccen tushe na doka ba. Hukumar ta kuma fara bincike kan Jami’ar Legas (UNILAG) da kamfanin Hackerbella Ltd, domin gano irin rawar da kowannensu ya taka wajen tattarawa, amfani da su, bayyana wa wasu ko sarrafa bayanan sirrin ɗaliban da lamarin ya shafa. Shugaban Sashen Shari’a, Tilasta Bin Doka da ƙa’idoji na NDPC, Babatunde…
Read More
Dangote na burin samun Dala biliyan 100 duk shekara nan da 2030

Dangote na burin samun Dala biliyan 100 duk shekara nan da 2030

Daga MAHDI MUSA MUHAMMAD Shugaban Rukunin Kamfanonin Dangote, Alhaji Aliko Dangote, ya bayyana ƙwarin gwiwar cewa, kamfanin zai iya cimma burinsa na samun Dala biliyan 100 a matsayin kuɗaɗen shiga a duk shekara nan da shekarar 2030. Dangote ya ce, cikakken nazari da ƙididdigar cikin gida da mahukuntan kamfanin suka gudanar ya ƙara musu tabbacin wannan buri na samun Dala biliyan 100 a shekara cikin shekaru huɗu masu zuwa abu ne da za a iya cimmawa. Ya bayyana hakan ne yayin da manyan jami’an Goldman Sachs, ɗaya daga cikin fitattun bankunan zuba jari da kamfanonin hidimomin kuɗi na duniya, suka…
Read More
Annobar karuwanci a ƙasar Hausa

Annobar karuwanci a ƙasar Hausa

(Ci gaba daga makon jiya) Daga MUKHTAR YAKUBU  "Shekara ta takwas kenen ina sana'ar karuwanci amma ba abinda na amfana da shi," in ji wata karuwa Da yake ba wannan ne ya fi damu na na sani ba, nan take sai na katse ta da tambayarta, duk tsawon shekarunta da take wannan sa'ar, wacce riba ta taɓa samu kuma wacce wahala ta taɓa fuskanta, kuma ko tana tunanin barin sana'ar nan gaba idan ta samu kudi ko mijin aure?  Sai ta ce, "Ni dai yanzu ina jin ina cikin shekaruna na takwas kenen a cikin wannan sana'ar ta karuwanci, kuma…
Read More
Abokan Mujaddadi allo da tawada

Abokan Mujaddadi allo da tawada

Daga NASIRU ADAMU EL-HIKAYA Har Shehu Usmanu Danfodiyo ya koma ga Allah a shekaru 63 bai samu zarafin yin hajji ba don sadaukar da kansa kakaf ga koyarwa. Kama daga ƙofar gidansa, masallaci har duk inda ya nufa a cikin jama’arsa. Hatta kaninsa Sheikh Abdullahi Gwandu ya yi yunƙurin tafiya aikin hajji amma kanawa su ka dakatar da shi don ya koya mu su addini. Gaba ɗaya rayuwar Shehu Mujaddadi a hidimar karatu, karantarwa da wayar da kan al’umma ne kan dokokin addinin Musulunci na ƙarfafa gaskiya da amana da tarbiyya. Wannan ya sa ba a samun ko rabin sa’a…
Read More
An kama mai aski bisa zargin amfani da gashin mutane don yin tsafi

An kama mai aski bisa zargin amfani da gashin mutane don yin tsafi

An kama wani mai aski mai suna Emeka a garin Umuahia, babban birnin Jihar Abia, bayan da jami'an Rundunar 'Yan Sandan Jihar Abia suka gano wata tukunya da ke cike da gashin mutane a cikin ɗakinsa. Rahotanni sun ce Emeka ya yi suna a Umuahia saboda ƙwarewarsa wajen aski, sai dai an cafke shi ne a ranar Talata bayan maƙwabcinsa, Johnson Ikenga, ya kai ƙorafi ga 'yan sanda yana zargin mai askin da yi masa barazana. A yayin da jami'an 'yan sanda suka kai samame gidan wanda ake zargin domin bincike, sun gano wata tukunya mai ɗauke da gashin mutane…
Read More
Me ya sa ‘yan Kannywood suka mamaye harkar siyasa?

Me ya sa ‘yan Kannywood suka mamaye harkar siyasa?

Daga AISHA ASAS  *Shin suna shiga domin wakiltar muradun jama'a ko kansu? A shekarun baya, sunayen fitattun jaruman Kannywood sun fi yawan bayyana ne a fagen fina-finai, waƙoƙi da nishaɗantar da jama'a. Kyamarori, hasken fage da kuɗin shirya fina-finai ne suka fi zama abubuwan da ake danganta su da wannan masana'anta. Amma a yau, wannan hoton ya fara sauyawa. Wasu daga cikin fitattun jarumai, mawaƙa da masu shirya fina-finai sun koma wani babban dandali da za mu iya cewa saɓa wa sanannen abubuwan da suke fassara masana'antar, wato fagen siyasa. Daga halartar gangamin jam'iyyu, zama masu taimaka wa 'yan takara,…
Read More
Zaɓen Osun: Zan yi nasara idan aka yi sahihin zabe — Adeleke

Zaɓen Osun: Zan yi nasara idan aka yi sahihin zabe — Adeleke

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Gwamnan Jihar Osun kuma ɗan takarar Jam'iyyar PDP a zaɓen gwamna na ranar 15 ga Agusta, Ademola Adeleke, ya bayyana ƙwarin gwiwar cewa zai sake lashe zaɓe idan aka gudanar da shi cikin sahihanci da adalci. Adeleke ya bayyana hakan ne a ranar Litinin yayin wani gangamin neman zaɓen tazarce da aka gudanar a Osogbo. "Da taimakon Allah, ina da cikakken yaƙinin samun nasara. Idan aka gudanar da zaɓe cikin gaskiya da adalci, zan yi nasara," inji shi. Gwamnan ya kuma yi zargin cewa ana kashe mambobin jam'iyyarsa, lamarin da ya sa ya roƙi…
Read More
Gwamnatin Tarayya ta ƙara ƙarfafa haɗin gwiwa da Cocin Katolika domin magance ƙalubalen Nijeriya – Akume

Gwamnatin Tarayya ta ƙara ƙarfafa haɗin gwiwa da Cocin Katolika domin magance ƙalubalen Nijeriya – Akume

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Sakataren Gwamnatin Tarayya (SGF), Sanata George Akume, ya tabbatar da aniyar gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu na ƙara ƙarfafa haɗin gwiwa da Taron Limaman Cocin Katolika na Nijeriya (CBCN), sauran ƙungiyoyin addinai, cibiyoyin gargajiya, ƙungiyoyin fararen hula da kuma kamfanoni masu zaman kansu domin magance manyan ƙalubalen da ƙasar ke fuskanta. Sanarwar da Mai Ba SGF Shawara kan Yaɗa Labarai da Hulɗa da Jama'a, Yomi Odunuga, ya sanya wa hannu ta bayyana cewa Akume ya yi wannan bayani ne bayan wata ganawa da Shugaba Tinubu ya yi da shugabannin CBCN. Akume ya ce, magance…
Read More
Masu ciwon sukari sun fi buƙatar kula da ƙafa

Masu ciwon sukari sun fi buƙatar kula da ƙafa

Daga AISHA ASAS Masu karatu, barkanku da sake saduwa a wannan makon cikin shafinmu na Kwalliya. Muna fatan darussan da muke tattaunawa suna ƙara wayar muku da kai kan yadda za a kare ƙafa da kuma kauce wa matsalolin da za a iya hana faruwarsu. A makonnin da suka gabata mun mayar da hankali kan muhimmancin kula da ƙafa, inda muka yi bayani kan matsalolin da rashin kula da ita kan haifar, tare da hanyoyin da za su taimaka wajen tabbatar da lafiyarta. A yau kuma za mu ci gaba da wannan darasi ne ta fuskar da ta fi shafar…
Read More