10
Feb
Tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Atiku Abubakar, ya jagoranci wata tawaga don ganawa da tsohon shugaban kasa, Olusegun Obasanjo, a gidansa da ke Hilltop, Abeokuta, babban birnin Jihar Ogun, a ranar Litinin. Atiku ya samu rakiyar tsohon gwamnan Jihar Cross River, Liyel Imoke, da kuma tsohon gwamnan Jihar Sakkwato, Sanata Aminu Tambuwal. Har zuwa lokacin da aka kammala taron, ba a bayyana takamammen dalilin ganawar ba, amma ana raɗe-raɗin cewa hakan na da nasaba da shirye-shiryen ‘yan adawa na fitar da dabarun da za su taimaka wajen kayar da jam’iyyar APC mai mulki a zaɓen shugaban ƙasa na 2027. Atiku Abubakar…