Kasuwanci

Gidauniyar Sidiya Charity ta fara horar da mata sana’o’in dogaro da kai

Gidauniyar Sidiya Charity ta fara horar da mata sana’o’in dogaro da kai

Daga MAHDI MUSA MUHAMMAD A wani gagarumin yunƙuri na bunƙasa rayuwar mata da inganta walwalar al’umma, Gidauniyar Sidiya Charity Foundation ta ƙaddamar da wani shiri na musamman na horas da mata sana’o’i da dabarun dogaro da kai, domin ba su damar samun hanyoyin samun kuɗaɗen shiga da kuma ƙarfafa matsayinsu a fannin tattalin arziki. An ƙaddamar da shirin ne cikin yanayi na farin ciki da fatan alheri, inda manyan baƙi, shugabannin al’umma, masu ruwa da tsaki da sauran masu goyon bayan ayyukan ci gaba suka halarci taron domin nuna goyon bayansu ga wannan shiri. Da take jawabi a wajen taron,…
Read More
Kungiyar ’yan kasuwar Bichi ta nemi tallafin jari domin bunƙasa kasuwar Kabiru Abubakar

Kungiyar ’yan kasuwar Bichi ta nemi tallafin jari domin bunƙasa kasuwar Kabiru Abubakar

Daga WAKILINMU Kungiyar 'Yan Kasuwar Zamani ta Bichi, wato Traders Multi-Purpose Cooperative Society Limited, ta yi kira ga gwamnati, shugabanni, masu ruwa da tsaki, manyan 'yan kasuwa da masu zuba jari da su haɗa hannu wajen bunƙasa harkokin kasuwanci a ƙaramar Hukumar Bichi. Shugaban ƙungiyar 'Yan Kasuwar Zamani ta Bichin, Alhaji Abubakar Mazahimu Sale ne ya bayyana wannan kiran, bayan kammala gina kasuwar Kabiru Abubakar Ultra-Modern Market Bichi, ƙarƙashin jagorancin ɗan Majalisar Tarayya mai wakiltar Bichi, Alhaji Abubakar Kabir Abubakar. Ya ce, a wannan karon da ake shirin fara amfani da rukuni na biyu na shagunan da aka kammala, lokaci…
Read More
Ku kama sana’a mata

Ku kama sana’a mata

Daga AISHA ASAS  A cikin shekarun baya, ana kallon mace a matsayin mai kula da gida kawai; wadda aikinta ya tsaya ne kan girki, rainon yara da kula da miji. Amma sauyin zamani, tsadar rayuwa da kuma ƙalubalen tattalin arziki sun sauya wannan tunani a hankali, inda a yau dubban mata ke rungumar sana’o’i daban-daban domin tallafa wa kansu, iyalansu da ma al’umma baki ɗaya. A kasuwanni, cikin unguwanni, a kafafen sada zumunta har ma cikin gidaje, ana samun ƙarin mata masu gudanar da sana’o’in da suka haɗa da dinki, kayan kwalliya, girki, kayan miya, sayar da kaya ta yanar…
Read More
Tarihin kasuwanci a Kano (II)

Tarihin kasuwanci a Kano (II)

Daga MAHDI MUSA MUHAMMAD A farkon shekara ta 1496 miladiyya, Sarkin kano Muhammad Rumfa ya yi waɗansu baƙin fataken Turawa da suka ɓullo daga Kumasi ta ƙasar Gwanja (Ghana) can yamma da Ilorin. A harshen Hausa muna kiransu da suna Patoki, amma ainihin sunansu Portuguese, ma’ana mutanen ƙasar Portugal. Babban cinikin waɗannan Turawan shi ne fataucin bayi, sune Turawan farko da suka kawo gyaɗa garin Kano. Su kan sayi bayi maza da mata a kasuwa. Su kuma sukan sayarwa da Kanawa gyada. Yayin da suka kammala sayar da gyaɗar tasu, sai suka shirya bayin da suka saya, suka tashi suka…
Read More
Nijeriya ta dawo sahun gaba a taron tattalin arzikin duniya – Shettima

Nijeriya ta dawo sahun gaba a taron tattalin arzikin duniya – Shettima

Daga MAHDI MUSA MUHAMMAD Mataimakin Shugaban Nijeriya, Kashim Shettima, ya dawo Abuja bayan kammala wata ziyara ta mako guda zuwa Guinea-Conakry da kuma Switzerland, inda ya bayyana cewa Nijeriya ta sake komawa sahun gaba a tattaunawar tattalin arziki da manufofin duniya. A wata sanarwa da mai taimaka masa na musamman kan harkokin yaɗa labarai da sadarwa, Stanley Nkwocha, ya fitar, an ce Mataimakin Shugaban ƙasar ya iso Filin Jiragen Sama na Nnamdi Azikiwe da ke Abuja a ranar Asabar. Shettima ya wakilci Shugaba Bola Ahmed Tinubu a bikin rantsar da sabon shugaban ƙasar Guinea, Mamadi Doumbouya, kafin daga bisani ya…
Read More
Yadda iskar gas ta CNG ta samu karɓuwa duk da ƙalubalen tashoshin sayarwa da tsada

Yadda iskar gas ta CNG ta samu karɓuwa duk da ƙalubalen tashoshin sayarwa da tsada

Daga MAHDI MUSA MUHAMMAD Shirin amfani da iskar gas ta CNG da Gwamnatin Tarayya ta ƙaddamar a matsayin madadin fetur ya fara samun karɓuwa a wurin ’yan Nijeriya, duk da cewa masu ruwa da tsaki na ci gaba da roƙon gwamnati ta magance matsalolin samuwar sa, ƙarancin ababen more rayuwa da kuma tsadar sauya injin mota zuwa inji mai amfani da CNG. Wannan tsari na daga cikin muhimman sauye-sauyen da gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu ta ɓullo da su a fannin makamashi, inda ake ƙoƙarin rage dogaro da fetur tare da bunƙasa amfani da ɗimbin arzikin iskar gas da ƙasar…
Read More
Yadda ƙaruwar kuɗaɗen Asusun Tarayya ya taimaka wa jihohi rage dogaro da rancen banki

Yadda ƙaruwar kuɗaɗen Asusun Tarayya ya taimaka wa jihohi rage dogaro da rancen banki

Daga MAHDI MUSA MUHAMMAD Jihohi da ƙananan hukumomi a Nijeriya sun samu gagarumin sauƙi a nauyin bashin bankuna, bayan sun biya kusan Naira Biliyan 547.5 cikin shekara guda, sakamakon ƙaruwar kuɗaɗen da suke samu daga Asusun Tarayya (FAAC).  Wannan ci gaban na nuni da wani sabon salo a tafiyar kuɗin gwamnatocin ƙananan matakai, inda aka fara fifita rage bashi maimakon dogaro da tsadar rance daga bankuna. Bayanai daga sabon rahoton ƙididdigar Babban Bankin Nijeriya (CBN) sun nuna cewa jimillar bashin da bankuna ke bin jihohi da ƙananan hukumomi ya ragu daga naira tiriliyan 2.68 a watan Yunin 2024 zuwa naira…
Read More
’Yan Nijeriya sun yi amfani da terabayit miliyan 1.236 na data a Nuwambar 2025 – NCC

’Yan Nijeriya sun yi amfani da terabayit miliyan 1.236 na data a Nuwambar 2025 – NCC

Daga MAHDI MUSA MUHAMMAD Amfani da data a Nijeriya ya kai sabon matsayi mafi girma a tarihin ƙasar a watan Nuwamba na shekarar 2025, inda mutane suka kashe kusan terabayt miliyan 1.236 na data, wato kusan petabayt 1.24, a cewar alƙaluman Hukumar Sadarwa ta Nijeriya (NCC). Wannan shi ne adadin wata guda mafi girma da aka taɓa samu tun bayan fara tattara irin waɗannan bayanai. Rahotanni sun nuna cewa wannan adadi ya ɗan zarce na watan Oktoba, wanda aka kiyasta ya kai terabayt miliyan 1.235, alamar da ke nuna ci gaba mai ƙarfi duk da matsin tattalin arziki da aka…
Read More
Yara marasa zuwa makaranta barazana ne ga ƙasa — Shettima

Yara marasa zuwa makaranta barazana ne ga ƙasa — Shettima

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja  Mataimakin Shugaban ƙasa, Kashim Shettima ya ce yawan yara marasa zuwa makaranta a Nijeriya a barazana ce da ke buƙatar haɗin gwiwa daga dukkan matakan gwamnati da masu ruwa da tsaki. Shettima ya yi wannan bayani a taron Zauren Ilimin Nijeriya na 2025 da aka gudanar a Abuja, wanda ƙungiyar Gwamnonin Nijeriya tare da Ma’aikatar Ilimi ta Tarayya da abokan hulɗa suka shirya. Ya ce matsalar ilimi ba za ta iya warwarewa da ƙoƙarin gwamnati kaɗai ba, yana mai jaddada cewa: “Yawan yaran da ba sa zuwa makaranta buƙatar gaggawa ce ta ƙasa da…
Read More
Sama da miliyan 100 za a raba wa ‘yan kasuwar Masaka da gobara ta shafa

Sama da miliyan 100 za a raba wa ‘yan kasuwar Masaka da gobara ta shafa

Daga JOHN D. WADA, a Lafiya Kwamitin da shugaban ƙaramar hukumar Karu a jihar Nasarawa barista Abubakar Aliyu Madaki ya kafa domin tantance lalacewa da kuma asarar dukiyoyi da aka yi sakamakon wata mummunar gobarar wuta da ta auku a kasuwar Masaka ta garin Karu din a bara ya gabatar da rahoton sa. Kwamitin wadda ke ƙarƙashin jagorancin shugabanta wato Cif Mark Auta a yayin zaman ya kuma ba da wasu shawarwari na musamman dangane da yadda za a aiwatar da matakan hana wuta a kasuwannin domin hana irin wannan abin gaggawa sake faruwa nan gaba da tabbatar da tsaro…
Read More