Kasuwanci

Atiku, Tambuwal da Imoke sun shiga ganawar sirri da Obasanjo

Atiku, Tambuwal da Imoke sun shiga ganawar sirri da Obasanjo

Tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Atiku Abubakar, ya jagoranci wata tawaga don ganawa da tsohon shugaban kasa, Olusegun Obasanjo, a gidansa da ke Hilltop, Abeokuta, babban birnin Jihar Ogun, a ranar Litinin. Atiku ya samu rakiyar tsohon gwamnan Jihar Cross River, Liyel Imoke, da kuma tsohon gwamnan Jihar Sakkwato, Sanata Aminu Tambuwal. Har zuwa lokacin da aka kammala taron, ba a bayyana takamammen dalilin ganawar ba, amma ana raɗe-raɗin cewa hakan na da nasaba da shirye-shiryen ‘yan adawa na fitar da dabarun da za su taimaka wajen kayar da jam’iyyar APC mai mulki a zaɓen shugaban ƙasa na 2027. Atiku Abubakar…
Read More
2024: OPay da Palmpay sun tara tiriliyan N71.5 wajen hada-hadar kuɗi ta wayar hannu

2024: OPay da Palmpay sun tara tiriliyan N71.5 wajen hada-hadar kuɗi ta wayar hannu

Daga MAHDI MUSA MUHAMMAD Masu bankin intanet a Nijeriya da suka haɗa da Opay, Palmpay da Paga, sun sami ƙaruwar da ba a taɓa ganin irinta ba a shekarar 2024, inda hada-hadar kuɗinsu ta kai Naira Tiriliyan 71.5, adadin da ya ƙaru da kashi 53.4 cikin 100 idan aka kwatanta da shekarar da ta gabata, kamar yadda sabbin bayanai daga Hukumar Kula da Tsare-Tsare na Bankin Nijeriya (NIBSS) suka nuna. Bayanan sun kuma nuna cewa yawan hada-hadar kuɗaɗen wayar hannu ya ƙaru da kashi 23 cikin 100, daga biliyan 3 a shekarar 2023 zuwa biliyan 3.9 a shekarar 2024, wanda…
Read More
Harkokin kasuwanci sun dawo a garin Batsari

Harkokin kasuwanci sun dawo a garin Batsari

Daga ABDULLAHI Muhammad a Katsina A yayin da harkar tsaro ta inganta a garin Batsari, harkokin kasuwanci ya dawo a manyan kasuwannin ƙaramar hukumar Batsari a Jihar Katsina. Karamar hukumar Batsari na ɗaya daga cikin ƙananan hukumomin da 'yan ta'adda suka lalata a jihar. Ɗaruruwan mutane suka rasa rayukansu,wasu sun raunana wasu kuma sun yi gudun hijira zuwa Katsina da jamhuriyar Nijar sakamakon hare haren yan ta'adda a yankin. Haka kuma sun ƙone kasuwannin da ɗaruruwan gidaje musamman a ƙauyukan da suke kewaye cikin garin Batsari,ga rufe makarantu. Sai dai shugaban ƙaramar Batsari Salisu Mamman da yake hira da manema…
Read More
’Yan kasuwa na yunƙurin yada fetur ɗin Dangote don rage farashin mai

’Yan kasuwa na yunƙurin yada fetur ɗin Dangote don rage farashin mai

Daga MAHDI MUSA MUHAMMAD Masu sayar da man fetur a Njjeriya sun bayyana cewa kuɗin da ake kashewa wajen shigo da man fetur zuwa ƙasar ya ragu zuwa N922.65. Rahotanni sun nuna cewa sauƙin farashin ya sanya saukar kuɗin litar mai ƙasa da yadda matatar Dangote ke sayarwa a kan N955. Raguwar farashin ya shafi kuɗin jigilar kaya, harajin shigo da kaya, da kuma tasirin canjin kuɗin waje. Ana hasashen hakan na nuna yiwuwar masu kasuwancin mai su koma shigo da man fetur daga ƙasashen waje maimakon saye a matatar Dangote. Wani babban ɗan kasuwa wanda ya nemi a sakaya…
Read More
Akwai ƙarin Naira 75 tsakanin man Fatakwal da Dangote – PETROAN

Akwai ƙarin Naira 75 tsakanin man Fatakwal da Dangote – PETROAN

Daga MAHDI MUSA MUHAMMAD Kungiyar Masu Sarin Fetur ta Nijeriya (PETROAN) ta bayyana cewa, farashin man da tsohuwar Matatar Fatakwal ta da dawo da aiki a ranar Talata ta saka, ya zarce Naira 75 a kowace lita fiye da wanda matatar Dangote ke sayarwa. Jami’in hulɗa da jama’a na ƙungiyar, Dokta Joseph Obele ne ya bayyana hakan a yayin bikin buɗe matatar man Fatakwal a hukumance, wanda yanzu haka yake aiki da gangar mai 60,000 a kowace rana. Dr Obele, tsohon shugaban ƙungiyar dillalan man fetur mai zaman kanta ta Nijeriya IPMAN, ya yaba wa gwamnatin tarayya kan farfaɗo da…
Read More
Adadin marasa aikin yi a Nijeriya ya ragu zuwa kashi 4.3 a rubu’i biyu na 2024

Adadin marasa aikin yi a Nijeriya ya ragu zuwa kashi 4.3 a rubu’i biyu na 2024

Daga MAHDI MUSA MUHAMMAD Hukumar ƙididdiga ta ƙasa (NBS) ta ce, adadin marasa aikin yi a Nijeriya ya ragu zuwa kashi 4.3 a rubu'i biyu na shekarar 2024. Ofishin ya bayyana haka ne a cikin rahotonta na NLFS na kashi na biyu na shakrar 2024 da aka fitar ranar Litinin. Adadin rashin aikin yi ya ragu zuwa kashi 4.3 a cikin rubu'i biyu daga kashi 5.3 a cikin rubu'i ɗaya na 2024. Hukumar ta NBS ta ayyana rashin aikin yi a matsayin ƙaruwar ma’aikatu (samuwar aikin yi da ma’aikatu), waɗanda ba su da aikin yi suna yawan samun aiki. "Rashin…
Read More
Mun samu masu sa jari a Nijeriya daga ƙasashen BRICS – Shettima

Mun samu masu sa jari a Nijeriya daga ƙasashen BRICS – Shettima

Mataimakin Shugaban ƙasa Kashim Shettima ya bayyana cewa Najeriya ta samu kuɗaɗen zuba jari daga waje har Dalar Amurka biliyan 1.27 daga ƙasashen BRICS zuwa watan Juni 2024. Wannan ya nuna ƙaruwar kuɗaɗen da aka samu idan aka kwatanta da Dalar Amurka miliyan 438.72 da aka samu a irin wannan lokaci a shekarar 2023. Ƙasashen BRICS sun haɗa da Brazil, Rasha, Indiya, Sin, da Afirka ta Kudu, tare da sabbin mambobi kamar Iran, Masar, Habasha, da Haɗaɗɗiyar Daular Larabawa. A lokacin taron China-Africa Inter-Bank Association Forum da aka gudanar a Abuja a ranar Laraba, Shettima wanda ya samu wakilcin mai…
Read More
Nijeriya na shirin haƙo ɗanyen mai gangan miliyan huɗu kullum zuwa 2030

Nijeriya na shirin haƙo ɗanyen mai gangan miliyan huɗu kullum zuwa 2030

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Gwamnatin Tarayya ta ce tana shirin samar da ganga miliyan huɗu a kowace rana na ɗanyen mai, da kuma ƙafa biliyan 10 na iskar gas nan da shekarar 2030. Olu Verheijen, mai ba shugaban ƙasa shawara na musamman kan harkokin mai ne ta bayyana hakan a cikin wata sanarwa da ya raba wa kamfanin dillancin labarai na Nijeriya ranar Juma'a a Abuja. Sanarwar ta samu sa hannun Morenike Adewunmi, Manajan masu ruwa da tsaki a ofishin mai ba da shawara na musamman. Verheijen ta ce, za a cimma wannan buri ne ta hanyar yin gyare-gyare a…
Read More
Ƙoƙarin Gwamnatin Kano na inganta ilimi ya sa ta ba mu aikin kujeru – Ƙungiyar Kafintoci

Ƙoƙarin Gwamnatin Kano na inganta ilimi ya sa ta ba mu aikin kujeru – Ƙungiyar Kafintoci

Daga IBRAHIM MUHAMMAD a Kano Ambasada Alhaji Nafiu Nuhu, Shugaban ƙungiyar Gandun Albasa 'general furniture' ya bayyana cewa Gwamnatin jihar Kano ƙarƙashin jagorancin Alhaji Abba Kabir Yusuf ta ba su aikin gudanar da dubban kujeru na zaman ɗalibai da malamai da za a sa a dukkan makarantun jihar. Ya ce, wannan gagarumin aiki da gwamnati ta ɗauko ya nuna jihar Kano tayi nasarar samun  nagantaccen shugaba jajirtacce da zai tsaya ya dubi matsalolin al'umma ya share musu kuka  wannan shine shugabanci nagari. Ya ƙara da cewa, kwanakin baya ya ayyana dokar ta ɓaci akan ilimi duk wanda yake Kano zai…
Read More
Hauhawar farashin kayayyaki a Nijeriya ta ragu zuwa kashi 32.15 – NBS

Hauhawar farashin kayayyaki a Nijeriya ta ragu zuwa kashi 32.15 – NBS

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Hukumar ƙididdiga ta ƙasa (NBS) ta sanar da cewa, hauhawar farashin kayayyaki a Nijeriya ya ragu tsawon watanni biyu a jere, daga kashi 34.19 a watan Yuni zuwa kashi 33.40 a watan Yuli, kuma yanzu haka ya kai kashi 32.15 a watan Agusta. Dangane da rahoton ƙididdigar farashin kayayyaki da ofishin ya fitar, an samu raguwar hauhawar farashin kayayyaki zuwa kashi 32.15 cikin 100 a watan Agustan 2024, yayin da hauhawar farashin kayayyakin abinci ya kai kashi 37.52 a cikin wannan wata. "Farashin watan Agusta 2024 ya nuna raguwar maki 1.25 idan aka kwatanta da farashin…
Read More