Kasuwanci

Dala ta sake shan kaye a hannun Naira, Dala 1 ta koma N1000

Dala ta sake shan kaye a hannun Naira, Dala 1 ta koma N1000

Daga BASHIR ISAH Kawo yanzu, Dalar Amurka na ci gaba da shan kashi a hannun Naira ta Nijeriya. Bayanai sun ce a wannan Litinin ɗin, an sayar da Dala 1 kan N1000 a kasuwar canji. Idan za a iya tunawa, a Litinin ta makon jiya Babban Bankin Nijeriya (CBN) ya saida wa 'yan canji (BDC) Dala miliyan $15.88 a kan N1,101 ga kowace Dala 1. 'Yan Nijeriya na ci gaba da fatan ganin Naira ta yi wa Dala rugugu ko sa samu sauƙin tsadar rayuwar da ake alƙanta ta da tashin Dala.
Read More
Waɗanne ƙasashen Afirka ne suka fi arziki da talauci a 2024? 

Waɗanne ƙasashen Afirka ne suka fi arziki da talauci a 2024? 

Daga AMINA YUSUF ALI Wani sakamakon bincike da Bankin ba da Lamun na Duniya ya yi, ya bayyana wasu ƙasashen Afirka mafiya talauci da mafiya arziki a shekarar 2024. A sha karatu lafiya.  Ana kallon nahiyar Afrika a matsayin wadda ta fi fama da talauci a faɗin duniya, inda abubuwa suka dabaibaye nahiyar kamar yadda tattalin arziki ke tangal-tangal da rashin tsaro da cin hanci da yaƙin basasa da kuma ayyukan ta'addanci. Asusun Lamuni na Duniya (IMF) ya fitar da jerin ƙasashe mafiya arziki da kuma matalauta a faɗin Afrika na shekara ta 2024. Yayin duba ƙasashe masu arziki a…
Read More
Alaƙar tattalin arzikin Nijeriya da sharrin Yahudawa da Nasara

Alaƙar tattalin arzikin Nijeriya da sharrin Yahudawa da Nasara

Daga ALIYU ƊAHIRU ALIYU  Da yawan mutane suna ɗauka karyewar darajar kuɗin ƙasa kamar sharrin Amurka ne ko kuma ba abu ne mai kyau ba. Amma sau da yawa gwamnatoci da kansu suke karya darajar kuɗin ƙasarsu ta hanyar "devaluation". Me ya sa? Karya darajar kuɗin yana da matsala ta wata fuskar amma yana da alfanu ta wata fuskar. Kuma tamkar kowane sha'ani na tattalin arziki, dole zaɓi ne ake yi a tsakanin matsaloli biyu a ɗauki ɗaya a bar xaya (trade-offs). A tattalin arziki ba a jifan tsuntsu biyu da dutse ɗaya.  Ƙasar da ta karya darajar kuxinta tana…
Read More
Nijeriya ta gurfanar da Shugaban Kamfanin Binance a kotu

Nijeriya ta gurfanar da Shugaban Kamfanin Binance a kotu

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Gwamnatin Tarayyar Nijeriya ta gurfanar da kamfanin Binance Holdings Limited da manyan jami’anta biyu, Tigran Gambaryan da Nadeem Anjarwalla da ya gudu a gaban kotu bisa zargin ƙin biyan haraji. An gurfanar da kamfanin da shugabannin biyu a gaban mai shari’a Emeka Nwite na babbar kotun tarayya da ke Abuja. Ɗaya daga cikin waɗanda ake tuhumar Tigran Gambaryan ya isa kotun ne da misalin qarfe 9:15 na safiyar ranar Alhamis yayin da abokin aikinsa, Anjarwalla ba ya nan saboda an ce yana gudu. Waɗanda ake tuhumar dai suna fuskantar tuhume-tuhume biyar na halasta kuɗaɗen haram, da…
Read More
Ƙarin kuɗin wutar lantarki dakushe tattalin arzikin ƙasa ne – Atiku

Ƙarin kuɗin wutar lantarki dakushe tattalin arzikin ƙasa ne – Atiku

Daga BASHIR ISAH Ɗan takarar Shugaban Ƙasa na babbar jam'iyyar hamayya, PDPD, Alhaji Atiku Abubakar, ya shiga sahun 'yan Nijeriya da ke ci gaba da sukar matakin ƙarin kuɗin wutar lantarki da Gwamnatin Tarayya ta ɗauka. Atiku ya ce, ya yi amannar wannar ƙarin kuɗin wutar babu abin da zai tsinana in ba da ƙara dakusar da tattalin arzikin ƙasar nan tare da ƙara tsananta wa 'yan ƙasa tsadar rayuwa. Kwanan nan aka ji Hukumar Kula da Wutar Lantarki ta Ƙasa (NERC) ta sanar da ƙarin wuta amma a kan masu amfani da lantarkin na rukunin farko, 'Band A', a…
Read More
Ci gaba da ba da tallafin wutar lantarki na kashi 85 na nuni da gwamnatin Tinubu ta al’umma ce –Idris

Ci gaba da ba da tallafin wutar lantarki na kashi 85 na nuni da gwamnatin Tinubu ta al’umma ce –Idris

Daga BASHIR ISAH Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Mohammed Idris, ya bayyana cewa, ci gaba da ba da tallafin lantarki da kashi 85 da Gwamnatin Tarayya ke yi hakan ya ƙara tabbatar da cewa gwamnatin Shugaba Bola Tinubu ta al'umma ce. Ministan ya bayyana hakan ne ranar Juma'a a lokacin da yake yi wa 'yan jarida jawabi a Abuja. Ta bakinsa, “Kwanaki kaɗan da suka gabata Gwamnatin Tarayya ta bayyana sabon tsarinta don cigaban fannin lantarki mai ƙudurin samar da wadatacciyar wutar lantarki a faɗin ƙasa. "Ɓangare mafi muhimmanci a tsarin shi ne, gwamnatin Tinubu za ta ci…
Read More
Yanzu-yanzu: NERC ta ci AEDC tarar N200m kan saɓa dokar sabon farashin wutar lantarki

Yanzu-yanzu: NERC ta ci AEDC tarar N200m kan saɓa dokar sabon farashin wutar lantarki

Daga BASHIR ISAH Hukumar Kula da Wutar Lantarki ta Ƙasa (NERC), ta ci kamfanin raba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution Plc, (AEDC), tarar Naira miliyan 200 saboda saɓa dokar sabon farashin wutar lantarki. Bayanin haka na ƙunshe ne cikin sanarwar da NERC ta wallafa a shafinta na X a ranar Juma'a. A cewar NERC, an ci AEDC tara ne saboda ƙin yin aiki da ƙa'idojin sabon farashin wutar lantarki wanda hakan ya haifar da ruɗani a tsakanin kostomomi da masu ruwa da tsaki a masana'antar lantarki. Ta ƙara da cewa, ta ɗauki wannan mataki ne biyo bayan bibiyar da…
Read More
Gobara ta ƙone shaguna da dama a Kwara

Gobara ta ƙone shaguna da dama a Kwara

Daga BASHIR ISAH Rahotanni daga Jihar Kwara sun ce shaguna da dama sun ƙone tare da asarar dukiya mai yawa sakamakon ƙobarar da ta auku a Kasuwar Owode da ke garin Offa a jihar. An ce gobarar ta fara ne da asubahin Talata wanda hakan ya yi sanadiyar ƙonewar wasu shaguna a kasuwar. Cikin wani faifan bidiyo na gobara wanda aka yaɗa an jiyo murya cikin harshen Yarabanci na cewa: “Wutar ta yi ƙarfi sosai, ba lantarki ya haifar da gobarar ba, wataƙila sakamakon girki da ake yi kusa da wurin ne." Bayanai sun daga bisani, Jami'an Kwana-kwana na ji…
Read More
Farashi zai ci gaba da tashi muddin gwamnatoci suka dinga biris da ‘yan kasuwa – Sardaunan Gwaram

Farashi zai ci gaba da tashi muddin gwamnatoci suka dinga biris da ‘yan kasuwa – Sardaunan Gwaram

Daga MOHAMMED ALI a Gombe Saboda yadda farashin kayyakin abinci da na masarufi har ma da kusan komai a faɗin ƙasar yake ta ƙara wahal da 'yan Nijeriya, baban ɗan kasuwan nan na Jihar Gombe, Alhaji Ahmed Abdullahi (Sardaunan Gwaram), ya yi kira ga Gwamnatin Tarayya da na jihohi baki ɗaya, da su tashi tsaye yanzun nan su ga sun bunƙasa kasuwanci a ƙasa. Har illa yau, Sardaunan Gwaram ɗin wanda shi ne Mataimakin Sakataren Ƙungiyar Haɗin Kan “Yan Kasuwan Jihar Gombe, ya ce muhimman mafitar dai kenan wato gaggauta bunƙasa kasuwanci sannan tallafi ga “yan kasuwa musamman kamar waɗanda…
Read More
Hukumar Kare Haƙƙin Mallaka ta maka shugaban MTN a kotu

Hukumar Kare Haƙƙin Mallaka ta maka shugaban MTN a kotu

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Hukumar Kare Haƙƙin Mallaka ta Nijeriya, NCC, ta gurfanar da Kamfanin Sadarwar MTN da wasu mutane huɗu a gaban kotu bisa zarginsu da keta haƙƙin mallaka. An shigar da aarar mai lamba FHC/ABJ/CR/111/2024 a babbar kotun tarayya da ke Abuja ranar Litinin. Sauran mutane huɗu da ake tuhuma a shari’ar su ne; Karl Toriola, shugaban MTN na Nijeriya, Nkeakam Abhulimen da Yahaya Maibe. A cikin tuhume-tuhume uku, NCC ta yi zargin cewa waɗanda ake tuhumar, a tsakanin shekarar 2010 zuwa 2017, “sun amfani da fasahar da ba tasu ba”, sun keta ayyukan waƙa na wani mawaƙi,…
Read More