Kasuwanci

An sauke wa acaɓa, keke napep farashin fetur zuwa N430 a Borno

An sauke wa acaɓa, keke napep farashin fetur zuwa N430 a Borno

An sauke farashin litar mai zuwa Naira 430 don amfanin 'yan acaɓa da matuƙa adaidaita-sahu da 'yan taksi a jihar Borno. Bayanai sun ce ƙaddamar da dogayen motoci guda 70 da gwamnatin jihar ta yi don rage raɗaɗin rayuwa inda jama'a kan biya N50, hakan ya sa sauran masu abubuwa na 'yan kasuwa a jihar kowa na neman matsaya. An ce wasu masu hannu da shuni a jihar suka bai wa gidajen mai a babban birnin jihar kwangilar sayar da fetur N430 kan kowace lita a maimakon N637. Bayanai sun ce masu hannu da shunin sun ɗauki wannan mataki ne…
Read More
Rana ko iska a matsayin makamashi

Rana ko iska a matsayin makamashi

Tare da BASHIR MUDI YAKASAI Batunmu na wannan makon shine, hasken rana da kuma iska a matsayin sinadiran da za su samar da makamashi da zai samar da wutar lantarki ga gidajenmu da ofisoshinmu da guraren gudanar da sana’oi da suke buƙatar wutar lantarki har da masana’antu da suke buƙatar wutar lantarki har da masana’antu da kamfanoni da gonaki, kai da duk wuni guri da ake buƙatar wutar lantarki. Kimiya, wato Ilimin ƙwaƙwa da na ci da kuma zurfafa tunani kan al’amari mai tafiya da kuma komowa, sai kuma ilimin fasaha wato, ilimin sarrafa abubuwa zuwa wani abun. Ɗan Adam…
Read More
NNPCL ya yi wa wasu shugabannin kamfanin ma’aikatansa ritayar dole

NNPCL ya yi wa wasu shugabannin kamfanin ma’aikatansa ritayar dole

Daga AMINA YUSUF ALI Kamfanin rarraba man fetur a Nijeriya (NNPCL) ya yi wa wasu daga cikin manyan ma'aikatansa/ shugabannin kamfanin ritayar dole. Wato ya tilasta wa wasu manyan ma'akatansa da wa'adin yin ritayar aikinsu ba ta wuce nan da watanni 15 masu zuwa ba yin ritayar dole. Wannan jawabin yana ƙunshe ne a cikin wani jawabi da hukumar gudanarwar ta kamfanin ta bayar a ranar Litinin ɗin da ta gabata ranar 18 ga Satumba, 2023, sannan ta wallafa a asusunta na shafin X (wanda da aka fi sani da Tiwita) a safiyar ranar Talata. Hakazalika, sanarwar ta bayyana cewa,…
Read More
‘Yan ƙasa ga Tinubu: Ba ma buqatar tallafin rage raɗaɗi, a rage mana farashin fetur kawai

‘Yan ƙasa ga Tinubu: Ba ma buqatar tallafin rage raɗaɗi, a rage mana farashin fetur kawai

*A zuba kuɗin tallafin rage raɗaɗi zuwa harkar ilimi da lafiya - 'yan ƙasa*Tallafin rage raɗaɗi ba shi da wata ma'ana - Inji ɗan kasuwa*Dole gwamnati ta sake tunani – Kwamared Alifia Daga AMINA YUSUF ALI A ƙoƙarinta na rage raɗaɗi da wahala da 'yan ƙasa suke sha a sakamakon cire tallafi a kan man fetur, gwamnatin tarayya ta shigo da tsarin ba da tallafin rage raɗaɗi, amma 'yan Nijeriya da suka samu kansu cikin matsuwa irin ta tattalin arziki sun fito sun bayyana cewa, sun fi qaunar a rage farashin man fetur fiye da tallafin rage raɗaɗin. Shugaba Bola…
Read More
UAE ta ɗage haramcin bai wa ‘yan Nijeriya bisar shiga ƙasar

UAE ta ɗage haramcin bai wa ‘yan Nijeriya bisar shiga ƙasar

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu da takwaransa na Haɗaɗɗiyar Daular Larabawa (UAE), Mohamed bin Zayed Al Nahyan, sun cimma yarjejeniyar ɗage haramcin bai wa matafiya daga Nijeriya bisa ta shiga ƙasar. A ranar Litinin shugabannin biyu suka cimma wannan matsaya a Abu Dhabi, inda aka amince jiragen Etihad Airlines da na Emirates Airlines su ci gaba da zirga-zirga a Nijeriya nan take. Kuma yarjejeniyar ci gaba da zirga-zirgar jiragen ba ta shafi gwamnatin Nijeriya ta biya wasu kuɗaɗe nan take ba. La'akari da manufar Tinubu ta inganta tattalin arzikin Nijeriya haɗa da sauran tsare-tsaren bunƙasa tattalin arzikin ƙasa da ya…
Read More
Kamfanin Google ya naɗa ɗan Nijeriya muƙamin Mananjan Darakta na Afirka 

Kamfanin Google ya naɗa ɗan Nijeriya muƙamin Mananjan Darakta na Afirka 

Daga AMINA YUSUF ALI A ranar Talatar da ta gabata ne dai kamfanin Google ya ba da sanarwar naɗin wani ɗan Nijeriya, Alex Okosi a matsayin Manajan Darakatan Google na Afirka domin taimaka wa kasuwanci da tattalin arziki su bunƙasa.  Mataimakin Shugaban EMEA na Google, Meir Brand shi ya hayyana hakan a wani jawabi. Sannan ya ce, a yanzu Mista Okosi shi ne zai ja ragamar ayyukan Google a Afirka. Mista Brand ya ƙara da cewa, wannan muƙami kuma zai taimaka wa biliyoyin masu amfani da shafin na Google su samu ƙarin abubuwa daga gare shi.   “Alex shugaba ne na…
Read More
Farashin mai ya kusa sakkowa a Nijeriya – Bincike

Farashin mai ya kusa sakkowa a Nijeriya – Bincike

Daga AMINA YUSUF ALI Akwai yiwuwar farashin man fetur a Nijeriya ya yi raga-raga in dai har farashin ɗanyen man fetur a duniya ya cigaba da faɗowa. A tarihi dai an riga an san cewa duk lokacin da farashin mai ya ɗaga a duniya, to farashin man fetur yana ƙaruwa a gidajen mai a Nijeriya ma. Alal misali ma wannan tsadar man fetur da ake fama da ita a Nijeriya ta afku ne sanadiyyar tashin farashin ɗanyen man fetur a duniya a karo na farko a watan Mayun shekarar 2023. Saboda haka, ake tunanin a halin yanzu da farashin ɗanyen…
Read More
Za mu kai ziyarar ba-zata ga bankunan da ake zargi da cinikin Dala ta haramtacciyar hanya – Gwamnnan CBN

Za mu kai ziyarar ba-zata ga bankunan da ake zargi da cinikin Dala ta haramtacciyar hanya – Gwamnnan CBN

Daga AMINA YUSUF ALI Babban Bankin Nijeriya (CBN) ya yi barazanar gurfanar da bankunan da suke cinikayyar Dala ba bisa ƙa'ida ba. Wato ta haramtacciyar hanya. Sannan kuma a gurfanar da wannan banki da ya karya doka a gaban kuliya. Gwamnna riƙon ƙarya na CBN, Folashodun Shonubi, shi ya bayyana haka a wata lacca da aka gabatar a kan samar da mafita ga tattalin arzikin Nijeriya, wanda aka yi a Abuja. Taron ya mai da hankali a kan yadda za a katange shigar da kuɗaɗen gwamnati zuwa haramtacciyar hanya tare da shigar da su inda ya dace don kawo cigaban…
Read More
Kirifto Karansi: Tsakanin mutanen MTFE da ƙwararru

Kirifto Karansi: Tsakanin mutanen MTFE da ƙwararru

Daga ƊANLADI Z. HARUNA Kasuwanci, musamman na yanar gizo, yana tattare da kasada da ganganci da kuma tarangahuma. Wasu ma sun ce kasuwancin intanet tamkar cinikin biri a sama ne. Don haka masu bincike suke ɗora nazarinsu akan cewa kasuwancin intanet ya sha bambam da na zahiri. Domin shi a mafi yawan lokuta, daji ne da ba shi da ƙyaure. Kowacce irin harkar intanet na ɗauke da wasu alamu da a zahiri ana iya alaƙanta su da damfara ko rashin tabbas. Ta haka idan an samu matsala, ana shan wahala kafin a warware ta. Wannan kenan. Bayyanar MTFE, ya zo…
Read More
Hukumomin Kwastam, NCC, da ma’aikatu 61 na tarayya za su fara tattara haraji ƙarƙashin inuwa guda

Hukumomin Kwastam, NCC, da ma’aikatu 61 na tarayya za su fara tattara haraji ƙarƙashin inuwa guda

Daga AMINA YUSUF ALI 'Yan kwamitin shugaban ƙasa a kan haraji da gyara al'amurran tattalin arziki na Nijeriya sun bayyana cewa, daga yanzu hukumar Kwastam da sauran hukumomi da ma'aikatu guda 62 na gwamnatin Tarayya za su daina amsar haraji kai-tsaye. Shugaban kwamitin mai suna, Taiwo Oyedele, shi ya yi wannan jawabi a wata tattaunawarsa da gidan talabijin ɗin Channels Television a wani shiri da suka saba gudanarwa duk ranar Laraba. Ya ƙara da cewa, hukumar tattara haraji ta tarayya ita ce za ta cigaba da harajin dukkan waɗannan hukumomi da ma'aikatu. Oyedele, ya bayyana cewa, Nijeriya tana daga cikin…
Read More