Kasuwanci

Ya kamata gwamnatoci su kafa masana’antun koya sana’o’i a gidajen yari – Doguwa

Ya kamata gwamnatoci su kafa masana’antun koya sana’o’i a gidajen yari – Doguwa

Daga BAKURA K. MUHAMMAD a Bauchi Muƙaddashin Kwanturola na gidan gyara jalin da ke Bauchi, Musa Dauda Doguwa ya buƙaci gwamnatocin lardin arewacin ƙasar nan da su kafa ma’aikatu na koya wa matasa sana’o’i da zummar rage gararambar su. Doguwa ya bayyana cewar, ya yi ayyuka a gidajen gyara hali daban-daban da ke sassan ƙasar nan, waɗanda suka haɗa da na Kano, Jigawa, Neja, Kaduna, Katsina, da sauransu. Amma bai taɓa iske gidan maza da yake da tarin matasa kamar na Bauchi ba. Doguwa ya bayyana hakan ne a yayin da yake jawabi jim kaɗan bayan da kwamitin da ke…
Read More
Kamfanin ‘Google’ zai zuba Dala biliyan guda don bunƙasa fasahar zamani a Nijeriya

Kamfanin ‘Google’ zai zuba Dala biliyan guda don bunƙasa fasahar zamani a Nijeriya

Daga AMINA YUSUF ALI Kamfanin Google ya bayyana cewa, zai ƙara zuba jarin Dalar Amurka har biliyan guda domin ganin an bunkasa fasahar zamani ta yanar gizo a Nijeriya da wasu ƙasashen Afirka. Kamfanin ya bayyana cewa, wannan yunƙurin nasa na zuba jari zai sa a samu rangwamen farashin yanar gizo da kaso 21. Sannan zai ninka ƙarfin yanar gizo sau biyar a ƙasar Nijeriya. Wannan bayani ya fito daga bakin Manajan Daraktan Google na Afirka, Nitin Gajria. A lokacin taron Google na Afirka na farko wanda aka gudanar a Larabar nan da ta wuce. A cewar sa, Kamfanin Google a…
Read More
An ƙara kuɗin ruwan fiyawota a Abuja zuwa Naira 20

An ƙara kuɗin ruwan fiyawota a Abuja zuwa Naira 20

Daga AMINA YUSUF ALI A yanzu haka dai masu kamfanonin buga ruwan leda (fiyawota) a Abuja sun ba da sanarwar ƙarin farashin ruwan leda (fiya wata/ pure water) a faɗin birnin na Abuja. Inda suka bayyana cewa za su fara bayar da sarin kowacce leda a kan Naira 200 inda su kuma masu sayar da ɗai-ɗai za su dinga sayar da shi a kan Naira 240 duk leda ɗaya, kuma idan ƙwalli ɗaya ne, Naira ashirin kowanne ɗaya. Masu kamfanonin ruwa sun bayyana cewa, farashin ruwan ya ƙaru ne sakamakon ƙaruwar farashin kayan aikin da suke amfani da su a…
Read More
E-Naira: Kamfani ya maka CBN a kotu kan zargin satar fasaha

E-Naira: Kamfani ya maka CBN a kotu kan zargin satar fasaha

Daga AMINA YUSUF ALI A halin dai da ake ciki, kotu ta aike wa da Babban Bankin Najeriya CBN, takardar sammaci, a kan zargin satar fasaha da wani kamfani ya yi ƙarar CBN ɗin a kai. Kamfanin ya zargi CBN da yi masa wankiyar fasaha inda ya ce shi ya fara ƙirƙirar fasahar e-Naira. Inda ya nemi kotu ta tursasa Bankin ya cire sannan ya canza wannan sunan na e-Naira domin haƙƙin mallakar kamfaninsa ne. Waɗannan bayanai suna ƙunshe ne a cikin takardar da kamfanin ya aike wa kotu wacce ta ƙunshi sa hannun Olakule Agbebi Esq a madadin kamfanin…
Read More
Noma: Shugaba Buhari ya bayyana dalilin tashin farashin abinci a Najeriya

Noma: Shugaba Buhari ya bayyana dalilin tashin farashin abinci a Najeriya

Daga AMINA YUSUF ALI Shugaban ƙasa Muhammadu Buhari ya bayyana dalilin da ya sa a kullum ake samun hauhawar farashin abinci a ƙasar Najeriya duk da yadda jama'a suka tsunduma ka'in da na'in wajen noma kayan abinci a ƙasar. Wannan jawabi yana ƙunshe ne a cikin jawabin da Shugaban ya gabatar a ranar murnar zagayowar samun 'yancin Najeriya Karo na 61 wanda ya gudanar ranar 1 ga watan Oktoba l, 2021 wato Juma'ar da ta gabata, a Abuja. Inda shugaban ya bayyana cewa, ba wasu ne suke jawo wannan tsadar rayuwar ba illa dillalai. Domin a cewar sa, su ne…
Read More
Rashin tsayayyen farashin Dala na dagula harkar kasuwanci – Yusuf Maiwake

Rashin tsayayyen farashin Dala na dagula harkar kasuwanci – Yusuf Maiwake

Daga IBRAHIM MUHAMMAD a Kano An bayyana ta'azzarar  farashin Dala da cewa yana dagula harkar kasuwancin 'yan kasuwar hatsi na Dawanau da ya sa suka ma rasa yaya za su yi. Alhaji Yusuf Barau Maiwake jigo a kayan amfanin gona na Dawanau shi ya bayyana haka. Ya ƙara da cewa, Dala ta zama abinda za ka ji yanzu an ɗaga farashinta, an jima  za ka ji farashin ya sake hawa, tun da su kayansu waje ake fitarwa kuma da Dalar ake amfani. Idan farashin bai tsaya ba, kowane ɗan kasuwa yana cikin ruɗani. Ya ce da a lokaci irin wannan,…
Read More
Tattalin arzikin Nijeriya na dab da rushewa – Sanusi II

Tattalin arzikin Nijeriya na dab da rushewa – Sanusi II

Daga SANI AHMAD GIWA Tsohon Gwamnan Babban Bankin Nijeriya (CBN), kuma Sarkin Kano na 14, Mai Martaba Muhammadu Sanusi II, ya ce, tattalin arzikin Nijeriya yana dab da rushewa. Sanusi ya bayyana haka ne a cikin jawabin da ya yi na ranar rufe gagarumin taron hannayen jari da aka yi a Kaduna mai taken KADINVEST 6.0, Sanusi ya ce baya ga cewa Nijeriya tana da matsala wurin samar da mai, a yanzu kasuwannin duniya ba su siya. Ya ce makomar ƙasar nan ta dogara ne da tattalin arziki mai dogaro da ilimi, kuma Nijeriya an bar ta a baya a…
Read More
DisCos za su yi ƙarin kuɗin wutar lantarki ya zuwa 1 ga Satumba

DisCos za su yi ƙarin kuɗin wutar lantarki ya zuwa 1 ga Satumba

Hukumar Kula da Sha'anin Lantarki ta Nijeriya (NERC) ta sahale wa kamfanonin rarraba wutar lantarki su 11(DisCos) damar ƙara kuɗin wutar lantarkin da ake sha daga ranar 1 ga Satumba 2021. Bayanan da MANHAJA ta kalato sun nuna cewa, hukumar NERC ta bai wa kamfanonin damar cajin kuɗin wuta gwargwadon yadda suke bada ita ne cikin wasiƙar da ta fitar mai taken "Sanarwar Ƙarin Kuɗin Wuta". Binciken MANHAJA ya gano cewa, tuni kamfanin rarraba wutar lantarki na Eko Electricity Distribution Company (EKEDC), ya sanar da kwastomominta a hukumance cewa zai ƙara farashin lantarki daga ranar 1 ga Satumba mai zuwa.…
Read More
Ɗangote ya zama na 117 a jerin masu kuɗin duniya

Ɗangote ya zama na 117 a jerin masu kuɗin duniya

Shugaban Rukunin Kamfanin Ɗangote, Aliko Dangote, ya zama na117 daga jerin masu kuɗin duniya, kamar yadda ƙididdigar jaridar Bloomberg ta nuna.Ƙididdigar na bibiyar masu kuɗin duniya ne kulli yaumi sannan bayan haka a fitar da jerin sunayen su gwargwadon yadda suka fi juna arziki tare da wallafa matsayin kowannensu a shafinsa na intanet. Ƙididdigar ta nuna ana tattara bayanan da kuma sabunta su dangane da masu arzikin ne a-kai-a-kai, inda a wannan karo Ɗangote ya zama na 117 da ƙarfin arzikinsa ya kai Dala nilyan $17.8. Ƙididdigar ta Bloomberg ta nuna Elon Musk shi ne ya zo na ɗaya a…
Read More
Har yanzu ba a sabunta wa kamfanin Airtel lasisin zamansa a Nijeriya ba – NCC

Har yanzu ba a sabunta wa kamfanin Airtel lasisin zamansa a Nijeriya ba – NCC

Daga UMAR M. GOMBE Hukumar Kula Sadarwa ta Nijeriya (NCC) ta ce har yanzu ba ta amince da sabunta wa kamfanin sadarwa na Airtel lasisin gudanar da harkokinsa ba a Nijeriya saɓanin iƙirarin da shugaban kamfanin a Nijeriya, Mr. Olusegun Ogunsanya, ya yi. Daraktan Sahen Hulɗa da Jama'a na NCC, Dr. Ikechukwu Adinde, shi ne ya bayyana hakan cikin wata sanarwa da ya fitar a Lahadin da ta gabata. NCC ta tabbatar da cewa lallai kamfanin Airtel ya aika da takardar neman sabunta lasisin zamansa a Nijeriya, amma hukumar ba ta amince da hakan ba tukuna. NCC ta ci gaba…
Read More