29
Aug
Daga SANUSI MUHAMMAD a Gusau Gwamnatin Jihar Zamfara ta yi gargaɗi ga malaman makarantun sakandare 250 da aka horar kan su guji yin sakaci kan aikin su, tana mai cewa duk wani malami da aka samu yana da halin rashin ɗa'a da rashin zuwa aiki zai fuskanci hukuncin ladabtarwa bisa ga doka. Kwamishinan Ilimi, kimiyya da fasaha, Hon. Abdulmalik Gajam ne ya bayar da gargaɗin a yau Asabar a bikin rufe taron horar da malamai na tsawon makonni biyu na shirin Global Standard Change Program (GSTTP) da aka gudanar a Gusau. Shirin gina ƙarfin aiki ya samu hirar da malaman…
