Labarai

Rundunar sojojin Isra’ila ta amince da murabus ɗin shugaban hukumar leƙen asirinta

Rundunar sojojin Isra’ila ta amince da murabus ɗin shugaban hukumar leƙen asirinta

Shugaban Hukumar Leƙen Asiri ta Isra’ila Aharon Haliva ya yi murabus, sakamakon harin da ba a taɓa ganin irinsa ba da ƙungiyar Hamas ta kai wa ƙasar a ranar 7 ga watan Oktoba. Haliva ya kasance babban jami’in gwamnatin Isra’ila na farko da ya aje muƙaminsa tun bayan harin Hamas da ya hallaka mutane 120o, sannan ta yi garkuwa da wasu kusan 250 da har yanzu ba a kammala kuɓutar da su ba. Jim kadan bayan harin, tsohon shugaban hukumar leƙen asirin ya ce a ɗora masa laifin rashin daƙile harin da Hamas ta kai cikin ƙasar, don haka ya…
Read More
Zamfara: ‘Yan bindiga sun kai hari mahaifar ministan tsaro, sun yi awon gaba da mutane sama da 50

Zamfara: ‘Yan bindiga sun kai hari mahaifar ministan tsaro, sun yi awon gaba da mutane sama da 50

Daga SANUSI MUHAMMAD a Gusau Wasu gungun 'yan ta'adda sun mamaye garin Maradun, hedikwatar ƙaramar hukumar Maradun kuma mahaifar ƙaramin ministan tsaro, Hon. Bello Muhammad Matawalle, inda suka yi garkuwa da mutane fiye da 50 galibinsu mata, a jihar Zamfara Wani mazaunin yankin, Malam Sulaiman Maradun, a wata tattaunawa ta wayar tarho ya tabbatar wa wakilinmu faruwar lamarin. A cewarsa, ‘yan bindigar sun yi wa garin ƙawanya da misalin ƙarfe 12:00 na tsakar daren ran Alhamis inda suka gudanar da harin nasu gida-gida. "Abin takaici ne yadda suka mamaye garinmu saboda sun zo da wasu manyan makamai masu kisa, suka…
Read More
Gwamna Abba Kabir ya ƙaddamar da aikin gadar sama da ƙasa ta Tal’udu

Gwamna Abba Kabir ya ƙaddamar da aikin gadar sama da ƙasa ta Tal’udu

Nan gaba kaɗan gadar Ɗan'agundi za ta biyo baya, inji gwamnan Daga RABIU SANUSI a Kano Gwamna Abba Kabir Yusuf na Jihar Kano ya ƙaddamar da aikin gadar ƙasa da sama da aka fara aikinta a ranar Asabar. Gwamnan ya bayyana cewa wannan aiki na da nasada da alqawarin da aka ɗaukar wa al'umma yayin da suke yawon yaƙin neman zaɓen shekarar 2023 da ya gabata. Maigirma gwamna Abba ya ƙara da cewa wannan aiki da zai gudana yana da nufin kawo sauƙi ga al'ummar ciki da wajen jihar musamman masu shigowa don gudanar da harkokin kasuwanci. "Kamar yadda muka…
Read More
Nijeriya ba ta shirya kafa ‘yan sandan jiha ba – Sufeto Janar

Nijeriya ba ta shirya kafa ‘yan sandan jiha ba – Sufeto Janar

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Sufeto Janar ɗin 'yan sandan Nijeriya Kayode Egbetokun ya bayyana cewa Nijeriya ba ta kai ga ta kafa 'yan sanda jiha ba wanda gwamnoni a jihohi ke da iko da. Egbetokun ya bayyana haka ne a ranar Litinin a taron tattaunawa kan kafa ‘yan sandan jiha wanda kwamitin majalisar wakilai kan duba kundin tsarin mulkin ƙasa ya shirya. Ya ce rundunar 'yan sandan ƙasa ba ta amince da hakan ba, amma kuma ta na rokon Majalisar Ƙasa ta duba yiwuwar ƙara kason 'yan sanda a kasafin kuɗin ƙasa. Ya kuma ce kafa ‘yan sandan…
Read More
Garin Alawa a Neja ya kama hanyar zama kufai saboda rashin tsaro

Garin Alawa a Neja ya kama hanyar zama kufai saboda rashin tsaro

Daga BASHIR ISAH Al'ummar garin Alawa da ke Ƙaramar Hukumar Shiroro a Jihar Neja, na ci gaba da ficewa daga garin saboda tsoron barazanar 'yan bindiga. Wannan na faruwa ne sakamakon janye jami'an tsaro da aka yi daga yankin alhalin yankin na daga wuraren da ke fuskantar barazanar 'yan ta'adda a jihar. Ya zuwa yanzu gwamnatin jihar ba ta ce komai kan batun ba. Majiyarmu ta ce muddin hukumomi ba su yi wani abu kan batun ba, yankin Alawa zai za zama kufai nan ba da daɗewa ba.
Read More
Gwamnan Sakkwato ya tuɓe rawanin hakimai 15

Gwamnan Sakkwato ya tuɓe rawanin hakimai 15

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Gwamnatin Sakkwato ta sallami hakimai 15 bisa zargin su da taimakawa rashin tsaro, satar filaye da sauran laifuka. An sallami hakimai 9 daga muqamansu bisa zargin su da rashin biyayya da taimakon rashin tsaro da satar filaye da kuma karkatar da dukiyar jama’a da rashin ɗa’a. Waɗanda aka sallama sun haɗa da hakiman Uguwar Lalle, Yabo, Wamakko, Tulluwa, llela, Dogon Daji, Kebbe, Alkammu, da kuma Hakimin Gyawa. Gwamnatin jihar ta kuma sauke wasu hakimai shida da tsohuwar gwamnatin jihar ta naɗa. Abubakar Bawa, Sakataren yaɗa labarai na Gwamna Ahmed Aliyu, ya bayyana cewa an…
Read More
Tsananin zafi: An buƙaci mutane su dauki matakan kariya na kiwon lafiya

Tsananin zafi: An buƙaci mutane su dauki matakan kariya na kiwon lafiya

Daga IBRAHIM HAMISU a Kano A halin da ake ciki na yanayin tsananin zafi, an yi kira ga al’umma da su ɗauki matakan kariya na kiwon lafiya domin kare lafiyarsu daga faɗa wa haɗari. Kwamishinan Lafiya na Jihar Kano, Dakta Abubakar Labaran Yusuf ne ya yi kiran a cikin wata sanarwar manema labarai da ma'aikatarsa ta fitar ranar Alhamis wadda aka raba wa manema labarai. Sanarwar wadda ta sami sa hannun Ibrahim Abdullahi, Dakta Labaran ya ce yanayin zafin da ake ciki ya fara ne tun daga watan Maris na wannan shekara, wanda ya sanya ƙaruwar zazzaɓi da mace-mace, ya…
Read More
Fursunoni 118 sun tsere bayan da ruwan sama ya lalata gidan yari a Neja

Fursunoni 118 sun tsere bayan da ruwan sama ya lalata gidan yari a Neja

Daga BASHIR ISAH Rahotanni daga garin Suleja a Jihar Neja sun ce, aƙalla fursunoni 119 ne suka tsere daga gidan yarin Suleja biyo bayan ruwan sama mai ƙarfi da aka samu a garin a daren Laraba wanda ya lalata wani sahshe na gidan yarin. Mai magana da yawun Hukumar Kula da Gidajen Yari na yankin FCT, Adamu Duza ya tabbatar da aukuwar hakan cikin wata sanarwa da ya fitar da safiyar Alhamis. Ya ce, “Ruwan sama mai ƙarfi da aka yi na awanni masu yawa a ranar Laraba, 24 ga Afrilun 2024, ya haifar da akasi a matsakaicin gidan yarin…
Read More
Majalisar Dokokin Kano ta amince da naɗin Lawan Badamasi matsayin Kwamishinan KANSIEC

Majalisar Dokokin Kano ta amince da naɗin Lawan Badamasi matsayin Kwamishinan KANSIEC

Daga RABIU SANUSI Kwamitin tantance abinda ya shafi harkokin zaɓe a Majalisar Dokokin Jihar Kano ƙarƙashi shugabancin Rt. Hon Jibrin Falgore, ta kammala tantace Alhaji Lawan Badamasi, wanda aka ambata a mastayin sabon Kwamishinan Zaɓe na Jihar Kano ta miƙa dukkan bayanai ga zauren majalisar don dubawa. Majalisar ta bayyana hakan ne a lokacin da take zamanta, a yayin da shugaban kwamitin, Hon Murtala Muhammad Kadage mai wakiltar Garko ya ce, wanda aka wanda naɗin ya shafa ya cancanta da matsayin kwamishinan zaɓen na jiha. Injiniya Murtala Kadage ya kuma ce, cancantar Badamasin yana dai-dai da abin da kundin tsarin…
Read More
Gwamnan Kano ya isa Amurka don halartar taron zaman lafiya

Gwamnan Kano ya isa Amurka don halartar taron zaman lafiya

Daga RABIU SANUSI Gwamna Abba Kabir Yusuf na jihar Kano ya isa ƙasar Amurka domin halartar babban taron tattaunawa da Cibiyar Zaman Lafiya ta Amurka ta shirya a ranar Talatar da ta gabata Wannan na ƙunshe ne a wata sanarwar da Darakta-Janar mai kula da harkokin yaɗa labarai na gwamnan, Sanusi Bature Dawakin Tofa, ya sanyawa hannu. Bature ya ce, taron na kwanaki uku da gwamnonin Kano, Katsina, Zamfara, Kaduna, Niger, Sokoto, Kebbi, Jigawa, Plateau ke halarta, an shirya shi ne domin magance matsalar rashin tsaro a Arewacin Nijeriya da kuma mafi kyawun zaɓi na daƙile ƙalubalen. "Haɗin kai mai…
Read More