Labarai

Yadda wasu jami’an gwamnati suka bada kwagilar wani asibiti sau biyar

Yadda wasu jami’an gwamnati suka bada kwagilar wani asibiti sau biyar

Shugaban hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa (ICPC), Dr. Musa Aliyu (SAN), ya bayyana yadda wani asibiti a Najeriya aka biya kuɗinsa cikakke sau biyar ba tare da an gina shi ba. Ya bayyana hakan ne a wata tattaunawa da ya yi da manyan 'yan jarida a Abuja, inda ya ce wannan na ɗaya daga cikin misalan yadda cin hanci da rashawa ya yi katutu a ƙasar. Ya buƙaci 'yan Najeriya su haɗa kai don yaƙar wannan matsala, yana mai cewa idan ba a daƙile cin hanci ba, ba za a samu ci gaba ba. Dr. Aliyu ya ƙara…
Read More
Marasa lafiya daga jamhuriyyar Nijar na shigo wa Nijeriya neman magani

Marasa lafiya daga jamhuriyyar Nijar na shigo wa Nijeriya neman magani

Daga ABDULLAHI MUHAMMAD a Katsina Duk da tsamin dangantaka da ke akwai tsakanin Nijeriya da Nijar akwai yan ƙasar Nijar da ke shigowa Nijeriya neman magani . Rabi Sani daga ƙauyen Daga a garin Maraɗi ta ce ta zo garin Magama a ƙaramar hukumar jibiya domin a duba lafiyar yaron a babban cibiyar shan maganin na Magaman Jibiya. Tace yaron ta na fama da gudawa ne kuma ya sami kula da ya kamata. Ta fadawa manema labarai cewa mutanen su daga Nijar na shigo wa a kullum domin neman magani. Haka wasu marasa lafiya daga Nijar da suka zo neman…
Read More
Mutanen Nijar da Katsina uwa ɗaya uba ɗaya ne – Na’Allah

Mutanen Nijar da Katsina uwa ɗaya uba ɗaya ne – Na’Allah

Daga ABDULLAHI MUHAMMAD a Katsina Shugaban ƙaramar hukumar Mai'adua Mamman Salisu Na Allah ya ce mutanen Nijar da Katsina uwa ɗaya uba ɗaya suke tun kaka da kakanni. Na Allah yayi wannan magana ne a wata hira da manema labarai a ofishin sa da ke sakatariyar ƙaramar hukumar ta Mai'adua. Ya ce tun iyaye da kakanni akwai kyakkyawar haɗaka na aurataiyaa da kasuwanci a tsakaninsu wanda a yanzu ma ya haɓaka. Shugaban ƙaramar hukumar ya bayyana cewa dubban mutane daga Katsina da wasu sassan Arewacin ƙasar nan na shiga ƙasar Nijar,suma yan ƙasar Nijar suna shigowa Nijeriya harkokin kasuwanci da…
Read More

Hukumar NSCDC a Zamfara ta jajenta wa waɗanda gobarar Ƙauran-Namoda ta shafa

Daga SANUSI MUHAMMAD a Gusau Hukumar tsaro ta Civil Defense (NSCDC) reshen jihar Zamfara ta jajenta wa iyalan waɗanda gobarar makarantar allo ta shafa a ƙaramar hukumar Ƙauran-Namoda da ta yi sanadin mutuwar almajirai 17. Tawagar, ƙarƙashin jagorancin kwamandan jihar, CC Sani Mustapha sun kai ziyarar jaje ga Mai Martaba Sarkin Ƙauran-Namoda, Alh. Sanusi Muhammad Ahmad Asha, Shugaban Karamar Hukumar, Alh. Munnir Mu'azu Haidara da waɗanda lamarin ya rutsa da su. A ranar Larabar da ta gabata ne wata gobara ta laƙume rayukan dalibai almajirai 17 yayin da aka ceto wasu goma 17 da suka samu munanan raunuka. Rahotanni sun…
Read More
‘Yan bindiga sun sace Birgediya Janar Maharazu Tsiga da mutane da dama a Katsina

‘Yan bindiga sun sace Birgediya Janar Maharazu Tsiga da mutane da dama a Katsina

' Daga ABDULLAHI MUHAMMAD a Katsina 'Yan bindiga ɗauke da muggan makamai sun shiga garin Tsiga a ƙaramar hukumar Bakori inda suka kwashe mutane da dama a ciki harda tsohon shugaban hukumar masu yiwa ƙasa hidima Birgediya Janar Maharazu Tsiga. Wani mazaunin garin da baya so a faɗi sunan sa yace 'yan bindigan sun kashe ɗan uwan nasu bisa karya dokar su na kada ayi harbi amma yayi ta harbi a gidan Birgediya Tsiga. Wani mazaunin garin da baya so a faɗi sunan yace basu kashe kowa ba sai da wani ɗan uwan su yan bindigan bayan sun same sa…
Read More
El-Rufai ya magantu kan rikicin Ribadu da Naja’atu

El-Rufai ya magantu kan rikicin Ribadu da Naja’atu

Tsohon gwamnan Jihar Kaduna, Malam Nasiru El-Rufai, ya mara wa Najaatu Mohammed baya a rikicinta da mai ba shugaban ƙasa shawara Kan tsaro (NSA), Nuhu Ribadu. El-Rufai ya bayyana cewa takardun majalisar dattawa da na zaman majalisar zartaswa ta tarayya (FEC) na shekarar 2006 za su tabbatar da maganganun da ake zargi Ribadu ya yi a wancan lokaci. A cewar El-Rufai, rahoton jaridar Daily Trust na watan Fabrairun 2007 ma yana tabbatar da wannan batu. Ya buƙaci masu ikon samun takardun gwamnati su nemi takardun zaman majalisar Zlzartaswa daga ofishin Sakataren Gwamnatin Tarayya (SGF) domin tabbatar da gaskiya. El-Rufai ya…
Read More
Majalisar Dokokin Kano ta amince da ƙirƙirar rundunar tsaro mai ɗauke da makamai

Majalisar Dokokin Kano ta amince da ƙirƙirar rundunar tsaro mai ɗauke da makamai

Daga IBRAHIM HAMISU a Kano Majalisar dokokin Jihar Kano ta amince da wata doka da zata kafa rundunar tsaro ta jiha domin kare rayuka da dukiyoyin al’umma. Bayan muhawara mai zafi kan wasu sassa na dokar, majalisar ta amince da tanadin da ke hana duk wani wanda ke cikin jam’iyyar siyasa jagorantar rundunar. Shugaban masu rinjaye na majalisar, Hon. Lawan Husaini Dala, ya bayyana cewa an yi nazari sosai kan dokar don tabbatar da cewa tana amfani ga kowane ɓangare na jihar. Sabuwar dokar ta ba wa jami’an rundunar ikon ɗaukar makamai, cafke masu laifi da kuma hana aikata miyagun…
Read More

Yara 17 ne suka rasu a iftila’in gobarar Zamfara

Daga BELLO A BABAJI Kimanin almajirai 17 ne suka rasa rayukansu da wasu 16 da suka samu raunuka a yayin da gobara ta kama a wata makarantar Islamiyya dake ƙaramar hukumar Ƙauran-Namoda a Jihar Zamfara. Gobarar ta fara ci ne daga wani gida da ke kusa da makarantar inda ta yaɗu zuwa masaukin yaran. Tuni aka garzaya da waɗanda suka samu raunuka zuwa asibiti don ba su kulawa. Wani shaida mai suna Yahaya Mahi ya shaida wa manema labarai cewa da farko wutar ta kama ne a wani sashi na ginin da almajiran suke, wadda daga bisani ta bazu har…
Read More

Nijeriya za ta yi amfani da bashi wajen ciyar da tattalin arziƙinta gaba – Shettima

Daga BELLO A. BABAJI Mataimakin Shugaban ƙasa, Kashim Shettima ya ƙaddamar da Ofishin Masu kula da Harkokin Sarrafa Basussuka (DMO) a ƙoƙarin Gwamnatin Tarayya na inganta harkoki da tsare-tsaren kuɗaɗe, wanda wani ɓangare ne na Ajendar Sabonta ƙasa ta Shugaba Bola Tinubu. A lokacin da ya ke magana yayin zaman tawagar ofishin a Fadar Shugaban ƙasa a ranar Laraba, Shettima, wanda shi ne shugabanta, ya yi kira ga mambobi da su samar da salo na musamman wajen sarrafa kuɗaɗen bashi na al'umma. Ya ce Nijeriya za ta cigaba da amfani da kuɗaɗen bashi a matsayin wani ginshiƙi na haɓaka tattalin…
Read More
Gwamnatin Katsina ta raba kayan noma na Naira biliyan takwas

Gwamnatin Katsina ta raba kayan noma na Naira biliyan takwas

Daga ABDULLAHI MUHAMMAD a Katsina A ƙoƙarin ta na inganta noman rani a jihar, gwamnatin Katsina ta rabawa ƙananan hukumomi 34 kayan noma da kuɗin su yakai Naira biliyan takwas. Shugaban ƙaramar hukumar Mani Dr Yunusa Mohammad Sani ya faɗa wa manema labarai haka a ofishin sa. Ya bayyana cewa kayan sun haɗa da garman shanu na zamani da injiunan ban ruwa masu amfani da hasken rana da buhu 13,000 na takin zamani da maganin feshi da sauran su. Ya ce gwamnatin jihar ta rabawa kowace ƙaramar hukuma garmunan shanu guda ɗari da injunan ban ruwa masu amfani da hasken…
Read More