26
Apr
Shugaban Hukumar Leƙen Asiri ta Isra’ila Aharon Haliva ya yi murabus, sakamakon harin da ba a taɓa ganin irinsa ba da ƙungiyar Hamas ta kai wa ƙasar a ranar 7 ga watan Oktoba. Haliva ya kasance babban jami’in gwamnatin Isra’ila na farko da ya aje muƙaminsa tun bayan harin Hamas da ya hallaka mutane 120o, sannan ta yi garkuwa da wasu kusan 250 da har yanzu ba a kammala kuɓutar da su ba. Jim kadan bayan harin, tsohon shugaban hukumar leƙen asirin ya ce a ɗora masa laifin rashin daƙile harin da Hamas ta kai cikin ƙasar, don haka ya…