08
Dec
Daga SANUSI MUHAMMAD a Gusau Wata Babbar Kotun Jihar Zamfara ta yanke wa wani Anas Dahiru hukuncin kisa ta hanyar rataya bisa samunsa da laifin kashe abokinsa a kan Naira 100. An gurfanar da Dahiru kotu ne a watan Yunin 2017 bisa zargin kashe abokinsa Shamsu Ibrahim inda ya daɓa masa wuƙa har lahira a lokacin da suke faɗa da juna saboda Naira 100. Da yake karanta hukuncin, Alƙalin Kotun, Mai shari’a Mukhtar Yusha’u ya ce wanda ake zargin Anas Dahiru da ke Unguwar Dallatu a garin Gusau a Jihar Zamfara, ya gurfana a gaban kotu a shekarar 2017 bisa…