Labarai

Da Ɗumi-Ɗumi: ‘Yan sanda sun kama Darakta Janar na hukumar bogi, Adeyemi bayan kotu ta bada izinin kama shi

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Jami'an tsaro sun kama Adeniyi Adeyemi, wato wanda ya kira kansa da Darakta Janar na hukumar bogi ta PFIPC. Hakan na zuwa ne bayan da Babbar Kotun Tarayya a Abuja ta bayar da izinin kama shi. Rahotanni sun bayyana cewa, an yi zargin cewa an cafke Adeyemi ne a maɓoyarsa ta Jihar Osun, inda ake sa ran kai shi Hedikwatar Rundunar 'Yan sanda a Abuja, ranar Talata. Babu cikakken bayani game da yadda aka kama shi a lokacin haɗa wannan rahoto. Hakan na zuwa ne sa'o'i bayan Mai Shari'a Mohammed Umar ya umarci a…
Read More
Ɗaukar doka a hannu ke janyo faɗa tsakanin manoma da makiyaya – Alhaji Akote

Ɗaukar doka a hannu ke janyo faɗa tsakanin manoma da makiyaya – Alhaji Akote

Daga JAMIL GULMA a Kebbi Shugaban ƙungiyar Miyetti Allah reshen ƙaramar hukumar Argungu Alhaji Hara Akote Badariya ya bayyana ɗaukar doka a hannu ne dalilin faɗa tsakanin manoma da Fulani makiyaya.Ya yi wannan bayanin ne a wata hira da ya yi da waƙilin jaridar Blueprint Manhaja a garin Argungu.Alhaji Akote Badariya ya ce tsakanin manoma da Fulani a ƙasar nan ba wanda ke iya raba su saboda ɗaya bai yi sai da ɗaya don haka suka tarar tun kakanni da iyaye, idan makiyaya suka yi ɓarna ko dai a yi sulhu tsakanin su ba sai an je ga hukuma ba…
Read More
Dangin juna Afirka ta karrama Danbayo da lambobin yabo biyu kan ayyukan jin ƙai

Dangin juna Afirka ta karrama Danbayo da lambobin yabo biyu kan ayyukan jin ƙai

Daga ABUBAKAR A. BOLARI Gombe Ƙungiyar dangin juna Afirka Initiative (DJAI) ta karrama babban mataimaki na musamman ga Gwamnan Jihar Gombe kan harkokin tsaro da hulɗa da sauran hukumomi, Ambasada Yusuf Musa Danbayo, da lambobin yabo guda biyu saboda ayyukansa na jin ƙai da gudummawar da yake bayarwa wajen ci gaban al'umma. An miƙa lambobin yabon ne a wajen bikin rufe taron ƙasa na DJAI na National Retreat 0.2, wanda aka gudanar a Yankari Game Reserve da ke Jihar Bauchi. Da yake gabatar da lambobin yabon, shugaban ƙungiyar na ƙasa, Usman BK, ya ce an zaɓi Danbayo ne saboda jajircewarsa…
Read More

Badaƙalar hukumar bogi: Adeyemi bai halarci zaman kotu ba yayin da aka shirya gurfanar da shi

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja An dakatar da sauraron ƙarar da aka shigar akan Darakta Janar na hukumar bogi ta PFIPC, Adeniyi Adeyemi sakamakon rashin bayyanarsa a gaban Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja a ranar Talata. Ana sa ran ganin Adeyemi ya bayyana a gaban Alƙali Mohammed Umar ne kan tuhume-tuhume guda takwas da suka shafi zarge-zargen bogi, damfara da sojan gona da aka shirya gabatarwa akansa. Ana ganin Sufeto Janar na Rundunar 'Yan sanda da ya shigar da ƙarar akan Adeyemi, ya nemi kotun ta bayar da izini domin kamo shi a duk inda yake. A ranar…
Read More

Za a kammala kwaso ‘yan Nijeriya a Afirka ta Kudu gobe yayin da 315 suka rage

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Jimillar 'yan Nijeriya guda 315 da suke cikin halin matsi a ƙasar Afirkata Kudu ne rukunin ƙarshe daga cikin waɗanda Gwamnatin Nijeriya take ƙoƙarin tabbatar da dawo da su gida bayan hare-haren ƙyamar baƙi da suka riƙa fuskanta a sassan ƙasar. Ana sa ran jirgin ƙarshe da zai yi jigilar 'yan Nijeriyar ya bar Afirka ta Kudu da misalin ƙarfe 1:30 na dare, inda ake sa ran ya iso Filin Murtala Muhammed da ke Legas da mislain ƙarfe 6:30 na safe. Kakakin Ma'aikatar Harkokin Wajen Nijeriya, Kimiebi Imomotimi Ebienfa ne ya sanar da haka…
Read More

Birtaniya ta sanya sabbin sharuɗɗan shiga ƙasarta ga ‘yan Nijeriya da wasu ƙasashen Afirka 32

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Ƙasar Birtaniya ta umarci Nijeriya da wasu ƙasashen Afirka guda 32 da su mallaki takardar tantancewa ta shiga gabanin zuwa ko wucewa ta ƙasar. Birtaniya ta sanar da haka ne ta ofishin hukumar shige da ficenta a ranar Litinin. Sabon jaddawalin sharuɗɗan ya ƙunshi matafiya su tabbatar da cika ƙa'idojin biyan ƙudin jirgin zuwa ƙasar, inda ta yi gargaɗin cewa waɗanda ba su da takardun da ake buƙata ka iya fuskantar jinkiri ko soke tafiyarsu. Haka kuma, 'yan ƙasashe sama da 100 da yankunan ake buƙatar su mallaki biza gabanin shiga Ingila da nufin…
Read More
Hon Safana ya yi alƙawarim ci gaba da farfaɗo da shirin bunƙasa al’umma

Hon Safana ya yi alƙawarim ci gaba da farfaɗo da shirin bunƙasa al’umma

Daga ABDULLAHI MUHAMMAD a katsina Mai bai wa gwamnan Jihar Katsina shawara kan ayyukan ƙananan hukumomi, Hon. Lawal Rufa'i Safana, ya jaddada muhimmancin farfaɗo da shirin Community Development domin ƙarfafa ci gaban al'umma a dukkan ƙananan hukumomin jihar. Hon. Safana ya bayyana hakan ne lokacin da shugabanni da mambobin ƙungiyar daraktocin Ilimi da ci gaban al'umma (ESD) na ƙananan hukumomi suka kai masa ziyarar neman goyon baya a ofishinsa. Ya ce sashen ayyuka zai samar da kayan aikin Community Development domin rabawa ƙananan hukumomi, inda ya bayyana cewa za su kasance ƙarƙashin kulawar sassan ESD. Ya kuma yi bayani kan…
Read More
Kotu ta mayar wa kamfani mallakar fili a Gombe tare da diyyar Naira miliyan 65

Kotu ta mayar wa kamfani mallakar fili a Gombe tare da diyyar Naira miliyan 65

Daga ABUBAKAR A BOLARI Gombe Babbar Kotun Jihar Gombe mai lamba ta tara ta tabbatar da cewa kamfanin Emir General Integrated Ltd ne halastaccen mamallakin wani fili mai faɗin hekta 1.30 da ke kan titin Gombe–Bajoga a ƙaramar hukumar Gombe, tare da bai wa kamfanin diyyar Naira miliyan 65 bayan ta gano cewa an kutsa masa tare da rusa kadarorinsa ba bisa ƙa'ida ba. Mai shari'a Daurabo S. Sikkam ce ta yanke hukuncin a shari'a mai lamba GM/116/2026, inda ta tabbatar da cewa takardar mallakar fili (Certificate of Occupancy) mai lamba GM/15926 da kamfanin ke da ita tana nan da…
Read More

Badaƙalar hukumar bogi: Adeyemi ya buƙaci Tinubu ya sanya wakilan manyan ƙasashen waje cikin kwamitin bincike

Adeniyi Adeyemi, wanda ke iƙirarin cewa shi ne Darakta Janar na abin da ya kira Hukumar Bunƙasa Zuba Jarin Ƙasashen Waje ta Fadar Shugaban Ƙasa (PFIPC), ya rubuta buɗaɗɗiyar wasiƙa ga Shugaba Bola Tinubu inda ya buƙaci a kafa kwamitin bincike mai zaman kansa domin binciken takaddamar da ta dabaibaye hukumar. A cewarsa, ya kamata kwamitin ya haɗa da wakilan Majalisar Ɗinkin Duniya (UN), Amurka, Birtaniya, Tarayyar Turai, ECOWAS, AU, ƙungiyoyin fararen hula da masu sa ido na ƙasa da ƙasa domin tabbatar da gaskiya da amincewar jama'a. Rahotanni sun bayyana cewa, Adeyemi ya ce ba zai amince ICPC ita…
Read More

Amurka da Iran sun yi musayar wuta a mashigar Hormuz

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Kasar Iran ta ce ta ƙaddamar da hare-hare akan wasu manyan jiragen dakon mai a yankin mashigar Hormuz da ke gaɓar ruwan iyakarta Dakarun juyin juya halin Musulunci na Iran sun ce suna kai hare-hare kan ne akan jiragen da kuma wuraren da ke da alaƙa da Amurka a ƙasar Bahrain, yayin da rikici a tsakanin ƙasashen biyu ya sake caɓewa. Dakarun sun ce, sun lalata wasu jiragen ruwan dakon mai bayan sun yi watsi da gargaɗin da aka yi musu tare da kashe na’urorin da ke nuna inda suke zirga-zirga. A nata ɓangaren,…
Read More