Labarai

Tsaron ƙasa ya fara ne da kula da jin daɗin ‘yan ƙasa  — Sarki Sanusi

Tsaron ƙasa ya fara ne da kula da jin daɗin ‘yan ƙasa  — Sarki Sanusi

Daga RABIU SANUSI a Kano Mai Martaba Sarkin Kano, Khalifa Muhammadu Sanusi II, CON, ya bayyana cewa tsaron kowace ƙasa yana farawa ne daga kare rayuka, walwala da jin daɗin al’ummarta, yana mai jaddada cewa tsaro bai tsaya kawai kan kare iyakokin ƙasa ba. Sarkin ya bayyana hakan ne a lokacin da yake matsayin uban taron wata gagarumar ƙungiyar ƙa’idar Dokokin Jinƙai ta Duniya da Kwalejin Shari’a ta Jami’ar Northwest Kano suka shirya, inda ya gabatar da babban jawabi mai taken “Jagoranci, Zaman Lafiya da Rawar da Cibiyoyin Gargajiya ke Takawa wajen gina ƙasa.” Mai Martaba ya bayyana cewa bai…
Read More
Adeleke ya zargi Oyetola da matsa wa EFCC ta rufe asusun Jihar Osun

Adeleke ya zargi Oyetola da matsa wa EFCC ta rufe asusun Jihar Osun

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Gwamnan Jihar Osun, Ademola Adeleke, ya zargi tsohon gwamnan jihar, Gboyega Oyetola, da kasancewa a bayan matakin da Hukumar Yaƙi da Cin Hanci da Rashawa (EFCC) ta ɗauka na daskarar da asusun gwamnatin jihar. Adeleke ya bayyana hakan ne a ranar Talata yayin wani taron Arise Town Hall da aka shirya domin ’yan takarar kujerar gwamnan Jihar Osun, gabanin zaɓen gwamnan jihar da za a gudanar ranar 15 ga Agusta. Gwamnan ya yi zargin cewa Oyetola, wanda a yanzu yake riƙe da muƙamin Ministan Harkokin Ruwa da Tattalin Arziƙin Teku, yana amfani da sunan…
Read More
Ƙungiyar kamfen ɗin Mahadi Aliyu za su tafi kotu bisa cire sunan ɗan takarar gwamnan ADC a Zamfara

Ƙungiyar kamfen ɗin Mahadi Aliyu za su tafi kotu bisa cire sunan ɗan takarar gwamnan ADC a Zamfara

Daga SANUSI MUHAMMAD a Gusau Kungiyar yaƙin neman zaɓen Mahdi Aliyu Gusau ta ƙi amincewa da ɗora sunan Bilyaminu Shinkafi a shafin yanar gizon hukumar zaɓe mai zaman kanta ta ƙasa, INEC, a matsayin ɗan takarar gwamna na Jam'iyyar African Democratic Congress, ADC, a Jihar Zamfara. Ƙungiyar ta bayyana hakan a matsayin wata dabarar da ba ta dace ba kuma ta yi alƙawarin ƙalubalantar sa a kotu. A cikin wata sanarwa da ta fitar a Gusau ranar Juma'a, wadda ƙungiyar yaƙin neman zaɓen ta sanya wa hannu, ta dage cewa Mahdi Gusau shine halartaccen ɗan takarar gwamna na ADC a…
Read More
Kwamishina ya yabi malaman tsangaya kan goyon bayan Inuwa da Jamilu gwamna a 2027

Kwamishina ya yabi malaman tsangaya kan goyon bayan Inuwa da Jamilu gwamna a 2027

Daga ABUBAKAR A BOLARI Gombe Kwamishinan ƙananan hukumomi na Jihar Gombe, Barista Sani Ahmad Haruna, ya yaba wa malaman tsangaya na jihar bisa goyon bayan da suka bayyana wa Gwamna Muhammadu Inuwa Yahaya da ɗan takarar gwamnan jihar na jam’iyyar APC, Dakta Jamilu Isiyaku Gwamna a zaɓen 2027. Kwamishinan ya bayyana hakan ne a zantawarsa da manema labarai jim kaɗan bayan kammala wani babban taro da ƙungiyar malaman tsangaya ta jihar ta gudanar, inda malaman suka bayyana aniyarsu ta mara wa Dakta Jamilu Gwamna baya tare da tabbatar masa da ƙuri’u 150,000 a zaɓen 2027. Ya ce matakin malaman na…
Read More

Ma’aikatar kuɗi ta ɗora wa NNPCL laifin ɓatan bayanai yayin da majalisa ke binciken aron Dala 3bn da kuɗaɗen NLNG

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Ma'aikatar Kuɗi ta Tarayya ta ɗora wa Babban Kamfanin Man Fetur na Ƙasa (NNPCL) laifi bisa rashin gabatar da rahotannin bayanan da ake buƙata don warware tambayoyin kuɗaɗe da aka yi a rahoton shirin tabbatar da gaskiya da adalci kan kuɗaɗen masana'antun fitarwa (NEITI) na mai da gas na 2021 zuwa 2023. Babban Sakataren ma'aikatar, Raymond Omachi ne ya bayyana haka a ranar Alhamis yayin bayyana a gaban kwamitin binciken kuɗaɗen al'umma na Majalisar Dattawa, inda yake amsa tambayoyi kan rashin fahimtar haƙiƙanin yadda aka sarrafa wasu kuɗaɗe daga rahoton NEITI. Daga cikin ababen…
Read More
Osun 2026: INEC ta fara rarraba kayan zaɓe masu muhimmanci

Osun 2026: INEC ta fara rarraba kayan zaɓe masu muhimmanci

Daga USMAN KAROFI Hukumar zaɓe mai zaman kanta ta ƙasa (INEC) ta fara rarraba muhimman kayan zaɓe zuwa ƙananan hukumomi 30 na Jihar Osun, gabanin zaɓen gwamnan jihar da aka shirya gudanarwa ranar Asabar, 15 ga Agusta 2026. Kwamishinan INEC mai kula da zaɓen Osun, Kunle Ajayi, ya bayyana cewa ana gudanar da rabon kayan ne daga ofishin Babban Bankin Najeriya (CBN) da ke Osogbo, babban birnin jihar. Ajayi ya ce an samu jinkirin rarraba kayan zaɓen ne sakamakon jinkirin isowar sabbin takardun kaɗa ƙuri’a da sauran kayan zaɓe daga Abuja. Ya bayyana cewa an sake buga takardun ne bayan…
Read More

NAHCON ta amince da kamfanoni biyar don jigilar hajjin 2027

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Hukumar Jigilar Alhazan Nijeriya NAHCON, ta amince da kamfanonin jiragen sama guda biyar da za su gudanar da jigilar mahajjatan ƙasar yayin harkokin aikin Hajjin shekarar 2027. NAHCON ta sanar da haka ne wata sanarwa da ta fitar a ranar Alhamis. Ta ce, kamfanonin da aka amince da su sun haɗa da Air Peace Limited, Flynas, Max Air Limited, Saudi Air da UMZA Aviation Services Limited. A cewarta, an zaɓi kamfanonin ne bayan tantance su da kwamitin tantance kamfanonin jiragen sama ya gudanar, bisa la’akari da ƙa’idojin tsaro, ƙarfin matakin gudanar da aiki da…
Read More
Chadi za ta bai wa ƙasashen Afirka izinin shiga ƙasar babu biza

Chadi za ta bai wa ƙasashen Afirka izinin shiga ƙasar babu biza

Daga MAHDI MUSA MUHAMMAD Jamhuriyar Chadi ta sanar da cewa daga 1 ga Janairu, 2027, ’yan ƙasa daga dukkan ƙasashen Afirka za su samu damar shiga ƙasar ba tare da neman takardar izinin shiga ƙasa, wato biza, ba. Shugaban ƙasar Chadi, Mahamat Idriss Deby, ya ce matakin na daga cikin ƙoƙarin ƙasar na ƙarfafa haɗin kan Afirka da kuma sauƙaƙa zirga-zirgar mutane da kayayyaki tsakanin ƙasashen nahiyar. Deby ya bayyana cewa cire takunkumin biza zai taimaka wajen ƙarfafa alaƙa tsakanin ƙasashen Afirka, tare da sauƙaƙa tafiye-tafiye daga wata ƙasa zuwa wata. A cewarsa, wannan manufa ta nuna yadda Chadi ke…
Read More
Karramawar Blueprint ta ƙara mana ƙaimin taka-tsantsan da kuɗin al’umma – Gwamna Namadi

Karramawar Blueprint ta ƙara mana ƙaimin taka-tsantsan da kuɗin al’umma – Gwamna Namadi

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya karɓi lambar yabo ta Blueprint Newspapers ta shekarar 2025 kan kula da kuɗaɗen gwamnati da sauye-sauyen harkar noma, yana mai cewa karramawar za ta ƙara wa gwamnatinsa ƙwarin gwiwar yin taka-tsantsan da ci gaba da yin amfani da albarkatun jama’a cikin tsanaki da bunƙasa harkar noma. Gwamnan Namadi ya bayyana hakan ne a wata wasiƙa mai kwanan watan 5 ga Agusta, 2026, wacce Babban Sakataren Ofishinsa na Musamman, Adamu M. Garun-Gabas, ya sanya wa hannu, a matsayin martani ga wasiƙun da Blueprint Newspapers Limited ta aiko masa…
Read More
Zaɓen Osun: Sufeto Janar ya tura DIG Ishyaku domin jagorantar tsaro

Zaɓen Osun: Sufeto Janar ya tura DIG Ishyaku domin jagorantar tsaro

Daga MAHDI MUSA MUHAMMAD Babban Sufeto Janar na ’Yan Sandan Nijeriya, IGP Olatunji Disu, ya tura Muƙaddashin Babban Sufeto Janar, DIG Ishyaku Mohammed, zuwa Jihar Osun, domin jagorantar daidaita ayyukan tsaro yayin zaɓen gwamnan njihar da za a gudanar ranar Asabar, 15 ga Agusta, 2026. A cikin wata sanarwa da Jami’in Hulɗa da Jama’a na Rundunar ’Yan Sandan Nijeriya (FPRO), CSP Anietie Iniedu, ya fitar a Abuja, ya ce tura babban jami’in na daga cikin matakan da rundunar ta ɗauka domin tabbatar da gudanar da zaɓe cikin zaman lafiya, tsaro da sahihanci a faɗin jihar. Ya ce, DIG Ishyaku Mohammed…
Read More