Labarai

Ta’addanci na haifar da illa musamman ga mata — Amina Mohammed

Ta’addanci na haifar da illa musamman ga mata — Amina Mohammed

Daga WAKILINMU Mataimakiyar Sakatare Janar ta Majalisar Ɗinkin Duniya, Amina Mohammed, ta jaddada muhimmancin magance matsalolin ta'addanci da tallafa wa al'ummomin da abin ya shafa a faɗin Afirka. Mataimakiyar ta bayyana haka ne a yayin da aka yi wani taro na yaƙi da ta’addanci da aka gudanar a ranar Litinin a Birnin Tarayya Abuja. Ofishin Mai Ba Da Shawara kan Harkokin Tsaro (ONSA) tare da hadin gwiwar ofishin yaƙi da ta'addanci na Majalisar Dinkin Duniya UNOCT ne suka shirya. Taron ya aka yi wa taken 'Karfafa Hadin Gwiwar Yanki Da Ci Gaban Cibiyoyi Don Tinkarar Barazanar Ta'addanci a Afirka'. Amina…
Read More
Zan yi murabus muddin ba a hukunta Yahaya Bello ba — Shugaban EFCC

Zan yi murabus muddin ba a hukunta Yahaya Bello ba — Shugaban EFCC

Daga BASHIR ISAH Shugaban Hukumar Yaƙi da Rashawa ta EFCC, Ola Olukoyede, ya lashi takobin bin diddigin zargin almundahanar Naira biliyan 80.2 da ake yi wa tsohon Gwamnan Jihar Kogi, State Yahaya Bello har zuwa ƙarshe. Olukoyede ya furta haka ne a hirar da ya yi da manema labarai a Babban Ofishin hukumar da ke Abuja, inda ya ce babu makwa zai yi murabus muddin ba a hukunta Bello ba. "Idan ni da kaina ban ga ƙarshen wannan binciken game da Yahaya Bello ba, zan a jiyen' muƙamina a matsayin Shugaban EFCC Chairman,” in ji Olukoyede. Ya ce Bello ya…
Read More
Yadda rabuwar aure ke kawo damuwa ga iyalai

Yadda rabuwar aure ke kawo damuwa ga iyalai

Tare da ABBA ABUBAKAR YAKUBU Zaurukan sada zumunta sun ɗauki hankali a makon da ya gabata, sakamakon wasu maganganu da fitaccen jarumin Kannywood kuma mawaƙi Adam A. Zango ya yi a wani ƙaramin bidiyo da ya ɗora a shafinsa, a matsayin martani ga masu yaɗa maganganu marasa daɗi a kansa. Tun bayan da jarumin finafinan Hausan ya sanar da rabuwa da matarsa ta baya-bayan nan surutai suke yawa a kansa, ana zarginsa da rashin iya riƙon aure, ko kuma auri-saki, kasancewar duk matan da ya aura ba sa jimawa tare da shi ake rabuwa, bisa wasu dalilai daban-daban. Ɓacin ran…
Read More
NDE ta horas da matasa 50 dabarun noma da kiwo a Jigawa

NDE ta horas da matasa 50 dabarun noma da kiwo a Jigawa

Daga UMAR AKILU MAJERI a Dutse Hukumar Samar da Aikin yi ta Ƙasa, NDE, reshen Jihar Jigawa, ta zaɓo matasa maza da mata su 50 daga sassan jihar tare da ba su horo a kan harkar noman rani da kiwon dabobi da kiwon kaji da noman kifi da nufin inganta rayuwarsu. Matasan da suka ci gajiyar shirin sun haɗa maza 20 da mata 30. Shugaban NDE a jihar, Alhaji Sa'adu Iya Yarima, shi ne ya shaida wa manema labarai haka jim kaɗan bayan kammala bai wa matasan da lamarin ya shafa horo a cibiyar hukumar da ke Jigawa . Yarima…
Read More
Da Ɗumi-ɗumi: EFCC ta tsare Hadi Sirika kan almundahanar N8bn

Da Ɗumi-ɗumi: EFCC ta tsare Hadi Sirika kan almundahanar N8bn

Daga BASHIR ISAH Hukumar yaƙi da rashawa ta EFCC, ta tsare tsohon Ministan Sufurin Jirgin Sama, Hadi Siriki, sakamakon binciken da take gudanarwa kan badaƙalar karkatar da biliyan N8,069,176,864.00 na Kamfanin Nigeria Air. Jaridar Punch ta rawaito tsohon Ministan ya isa ofishin EFCCda ke Abuja da misalin ƙarfe 1:00 na rana a ranar Talata, 23 ga Afrilun 2024. Majiyarmu ta ce, bayan da ya isa ofishin na EFCC, an yi ea Sirika tambayo kan wasu kwangiloli da ake zargin ya bayar bisa ƙa'ida ba ga kamfanin Engirios Nigeria Limited mallakar wani ƙaninsa, Abubakar Sirika. Majiya ta kusa da EFCC wadda…
Read More
Yaƙi da Ta’addanci: Akwai buƙatar samar da dakarun yanki don daƙile safarar makamai — Tinubu

Yaƙi da Ta’addanci: Akwai buƙatar samar da dakarun yanki don daƙile safarar makamai — Tinubu

Daga BASHIR ISAH Shugaban Ƙasa Bola Tinubu, ya jaddada kira kan samar da dakarun yanki masu zamn ko-ta-kwana a matsayin kayan aikin magance dukkan matsalolin tsaron da ake fuskanta a yanzu da ma waɗanda ka iya tasowa a gaba a yankin Afirka Kazalika, ya ce samar da dakarun zai taimaka ainun wajen daƙile safarar makamai a tsakanin ƙasashen Afirka. Tinubu ya bayyana haka ne sa'ilin da yake jawabi a wajen buɗe babban taron yaƙi da ta'addanci a Afirka wanda aka shirya ranar Litinin a Abuja. Shugaban ya ƙara da cewa, ya zama wajibi a kawo ƙarshen ta'addanci a yankin Afirka…
Read More
Gwamnatin Tinubu za ta haramta wa ɗalibai ‘yan ƙasa da shekara 18 neman gurbin karatu a manyan makarantu

Gwamnatin Tinubu za ta haramta wa ɗalibai ‘yan ƙasa da shekara 18 neman gurbin karatu a manyan makarantu

Daga BASHIR ISAH Gwamnatin Tarayya ƙarkashin jagorancin Shugaba Bola Ahmed Tinubu, ta ce tana shirin haramta wa ɗalibai 'yan ƙasa da shekara 18 nan gurbin karatu a jami'o'i da sauran manyan makarantu da ke faɗin Nijeriya. Ministan Ilimi Farfesa Tahir Mamman ne ya bayyana haka a lokacin da yake yi wa manema labarai ƙarin haske a lokacin da yake zagayen duba yadda jarrabawar UTME ta 2024 ke gudana a wasu cibiyoyin rubuta jarrabawar ranar Litinin a Abuja. Ministan ya bayyana rashin jin daɗinsa bisa ƙarancin shekarun wasu daga cikin ɗaliban da ya gani suna rubuta jarrabawar, yana mai cewa shekarunsa…
Read More
Gwamna Lawal ya jaddada buƙatar amfani da fasahar zamani wajen yaƙi da rashin tsaro

Gwamna Lawal ya jaddada buƙatar amfani da fasahar zamani wajen yaƙi da rashin tsaro

Daga NASHIR ISAH Gwamna Dauda Lawal na Jihar Zamfara ya jaddada buƙatar da ke akwai ta amfani da fasahar zamani wajen yaƙi da rashin tsaro a Jihar da ma yankin Arewa baki ɗaya. Lawal ya bayyana haka ne a wajen taron da shi da wasu takwarorinsa suka yi da Mataimakiyar Sakataren Majalisar Ɗinkin Duniya, Amina J. Mohammed, ranar Juma'a a Washington, D.C. Mahalarta taron sun haɗa da gwamnonin Zamfara da Benue da Jigawa da Kaduna da Katsina da Kebbi da kuma Neja, kamar yadda mai magana da yawun Gwamnan Zamfara, Sulaiman Bala Idris, ya bayyana cikin sanarwar da ya fitar…
Read More
‘Yan sandan Kenyan sun cika hannu da shugaban Binance da ya tsere daga Nijeriya

‘Yan sandan Kenyan sun cika hannu da shugaban Binance da ya tsere daga Nijeriya

Daga BASHIR ISAH 'Yan Yaƙi da Manyan Laifuka na Ƙasa da Kasa, sun damƙe shugaban kamfanin Binance, Nadeem Anjarwalla, a ƙasar Kenya. MANHAJA ta tattaro cewar, 'yan sandan na nan suna shirin miƙa Anjarwalla ga Gwamnatin Nijeriya bayan kammala ɓangarensu. Majiya ta kusa da gwamnati wadda ba ta amnince a ambaci sunanta ba, ita ce ta tabbatar da kama Anjarwalla ran Lahadi da daddare. Idan za a iya tunawa, MANHAJA ta rawaito Gwamnatin Tarayyar Nijeriya ta bayyana cewa ta gano inda tserarren shugaban Binance da ya tsere, Nadeem Anjarwalla ya ɓoye. Gwamnatin ta ce, ta gano Anjarwalla yana ƙasar Kenya…
Read More
Jigawa za ta yi wa yara miliyan ɗaya allurar riga-kafin shan inna

Jigawa za ta yi wa yara miliyan ɗaya allurar riga-kafin shan inna

Daga UMAR AKILU MAJERI a Dutse Gwamnatin Jihar Jigawa ta shirya tsab don yi wa ƙananan yara su miliyan ɗaya da rabi allurar rigakafin shan inna a matsayin ƙoƙarin da gwamnatin jihar ke yi na hana cutar ɓulla a jihar. Darakta a hukumar lafiya matakin farko, Dakta Shehu Sambo, shi ne ya sanar da hakan ga taron manema labarai jim kaɗan bayan ƙaddamar da shirin allurar na bana a fadar Sarkin Dutse, Alhaji Hamim Nuhu Muhammed Sunusi a ranar Litinin. Jami'in ya ce yara miliyan ɗaya da rabi ake sa sunasa ran za su amshi allurar a fadɗn Jihar. Ya…
Read More