Labarai

‘Yan sanda sun sami nasarar ceto mata biyu daga hannun ‘yan bindiga a Katsina

‘Yan sanda sun sami nasarar ceto mata biyu daga hannun ‘yan bindiga a Katsina

Daga ABDULLAHI MUHAMMAD a Katsina Rundunar 'yan sanda a Katsina sun nasarar ceto mata biyu daga hannun 'yan bindiga a ƙaramar hukumar Charanchi tare da daƙile yunƙurin satar dabbobi a ƙaramar hukumar Charanchi. Kamar yadda jami'in hulɗa da jama'a na rundunar 'yan sanda a Katsina DSP Abubakar Sadiq Aliyu ya sanar, ofishin 'yan sanda a Kankia suka sami labarin cewa 'yan bindiga a kan baburan hawa ɗauke da muggan makamai sun Kai hari a matsugunin Jauga a ƙauyen Sabon Gida da ke Kankia. Ya bayyana cewa nan take jami'an 'yan sanda suka isa ƙauyen inda su kai ta ɗauki ba…
Read More
‘Yan ta’adda sun kashe jami’an tsaron daji biyu a Kebbi

‘Yan ta’adda sun kashe jami’an tsaron daji biyu a Kebbi

Daga JAMIL GULMA a Kebbi Rahotanni daga ƙaramar hukumar Danko-Wasagu sun bayyana cewa aƙalla jami'an tsaron daji (Forest Guard) biyu sun rasa rayukan su bayan bata-kashi tsakanin su da waɗansu maharada a ke sa ran masu garkuwa da mutane ne da suka kai farmaki a gonakin garin Tudunbichi a garin Wasagu safiyar litinin.Wani mazaunin garin na Wasagu da bai so a bayyana sunan sa ba saboda dalilan tsaro ya bayyana cewa da rana ne maharan suka kai farmakin, bayan sanar da jami'an su kuma cikin lokaci suka kai wa mutanen garin ɗauki inda a ka yi musayar wuta na wani…
Read More
Tashar lantarki ta Lambar Rimi: Daga shekarun tsaiko zuwa hanyar kammala aiki a bayyane

Tashar lantarki ta Lambar Rimi: Daga shekarun tsaiko zuwa hanyar kammala aiki a bayyane

Daga ABUBAKAR TUKUR IBRAHIM Korafe-ƙorafen da ake yi dangane da tashar samar da wutar Iska ta Lambar Rimi abu ne da ya dace. Kowanne ɗan jihar Katsina na son ganin injinan samar da wutar suna aiki tare da ganin an fara isar da wutar lantarki zuwa gidaje, wuraren kasuwanci, masana'antu da al'ummomi. Sai dai kuma, duk da cewa yana da sauƙi a yi bayanin tarihin aikin, yana da muhimmanci a bayyana gaskiyar abubuwan da suka faru a ƙarƙashin jagorancin mai girma Gwamna Malam Dikko Umaru Raɗɗa, PhD, CON, wajen ceto aikin daga shekaru masu yawa na rashin tabbas tare da…
Read More
Yadda mata ke sayar da ƙwon haihuwarsu domin sayen abinci a Nijeriya

Yadda mata ke sayar da ƙwon haihuwarsu domin sayen abinci a Nijeriya

Daga MAHDI MUSA MUHAMMAD A faɗin Nijeriya, ana samun ƙaruwar yadda matasa mata ke sayar da ƙwayayen haihuwarsu, domin samun kuɗaɗen biyan buƙatun rayuwa, lamarin da ke haifar da muhawara kan illolinsa ga lafiya da kuma tarbiyya. Binciken da Weekend Trust ta gudanar ya nuna cewa cibiyoyin kula da matsalolin haihuwa sun zama wuraren da ɗalibai mata da sauran matasa ke zuwa domin sayar da ƙwayayen haihuwarsu. Wasu sun ce sun yi hakan ne domin biyan kuɗin makaranta, wasu kuma domin sayen gashin doki, tufafi da wayoyin hannu, yayin da wasu uwayen da ke renon yara su kaɗai suka ce…
Read More
Daular Shehu da Shehu kafin Allah ne

Daular Shehu da Shehu kafin Allah ne

Daga NASIRU ADAMU EL-HIKAYA Marigayi Dokta Musa ɗankwairo Maradun ya ce Shehu 3 ag ga Nijeriya Shehu Sakkwato da Shehun Borno sai marigayi Shehu Usman Abubakar na Gombe. A nan kan Shehu na farko da na biyu na ke magana ko ma dai kai tsaye Daular Sokoto da Daular Borno. Wadannan biyun dauloli biyu ne da a ka yi a yankin Arewa da kewaye kuma na addinin musulunci. Duk da zuwan Turawa ya sauya tarihinsu amma har gobe tasirinsu na nan daram. Ba abun da ya ƙarfafa tasirin sai bin tsarin addinin Musulunci wajen ibada da kyautatawa kowa da Musulmi…
Read More
An gudanar da taron zaman lafiya tsakanin manoma da makiyaya a Augie

An gudanar da taron zaman lafiya tsakanin manoma da makiyaya a Augie

Daga JAMIL GULMA a Kebbi An gudanar da wani muhimmin taron zaman lafiya tsakanin manoma da makiyaya a ƙaramar hukumar Augie da ke jihar Kebbi, domin ƙarfafa zaman lafiya da warware matsalolin da suka shafi rikice-rikicen noma da kiwo a yankin. Taron ya biyo bayan ƙorafe-ƙorafen da manoma suka gabatar, inda suka zargi wasu makiyaya da yin ɓarna ga amfanin gonakinsu da ke tudu da kuma fadamomi. Da yake jawabi a wajen taron da aka gudanar a sakatariyar ƙaramar hukumar Augie, Shugaban ƙungiyar Miyetti Allah Cattle Breeders Association of Nigeria (MACBAN) reshen Augie, Alhaji Shehu Rugga, ya yi alƙawarin ci…
Read More

Sojoji sun samu muhimman bayanan ISWAP bayan halaka mai ɗaukar hotonsu

Dakarun Atisayen Haɗin Kai sun sanar da halaka wani mai ɗaukar bidiyo na ƙungiyar ISWAP tare da gano bayanai masu nuna cewa wasu baƙi 'yan ƙasashen waje uku na taimaka wa ƙungiyar a Jihar Borno. Kakakin rundunar na Arewa maso Gabas, Kyaftin Muhammed Goni ya ce al'amarin ya faru ne bayan dakarun sun daƙile wani yunƙurin da mayaƙan ISWAP suka yi na kutsawa Cross Kauwa da ke ƙaramar hukumar Kukawa a daren Asabar wayewar Lahadi domin sace kayan maganin cutar kwalara a yankin. A cewarsa, dakarun sun gano motsin 'yan ta'addan ne akan lokaci tare da buɗe musu wuta, lamarin…
Read More

Kotu ba ta soke zaɓukan fidda gwanin ADC ba, inji Atiku yayin da ya garzaya Kotun Ƙoli

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa kuma ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar ADC, Atiku Abubakar, ya yi watsi da iƙirarin cewa Kotun Ɗaukaka Ƙara ta soke zaɓukan fidda gwani na jam'iyyar da aka gudanar domin babban zaɓen 2027, yana mai bayyana rahoton a matsayin ƙarya da ke ƙoƙarin ruɗar da 'yan Nijeriya da raunana ɓangaren adawa. Atiku, a wata takarda da Mai taimaka masa akan harkokin yaɗa labarai, Phrank Shaibu ya fitar a ranar Litinin, ya yi kira ga mambobin ADC da magoya baya a sassan Nijeriya da su kwantar da hankali tare da cigaba…
Read More

Hedimastan Oyo ya shaƙi iskar ‘yanci sa’o’i bayan sace shi

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Hedimastan makarantar Nomadic Basic School da ke Igbojaye a Ƙaramar Hukumar Itesiwaju ta Jihar Oyo, Mista Mathew Kolawale Owoade ya shaƙi iskar 'yan bayan garkuwa da shi da aka yi na tsawon kusan sa'o'i 48. An sako hedimastan mai shekaru 60 ne da misalin ƙarfe 6 na yammacin ranar Litinin, 13 ga Yuli, 2026. Da fari, masu garkuwar sun buƙaci a biya Naira miliyan 30 a matsayin kuɗin fansa, inda iyalan suka yi magiya akan su karɓi miliyan N3, wanda da farko sun amince. Bayan iyalan sun tara miliyan N3, an yi zargin cewa…
Read More

Sojoji sun miƙa ɗalibai da malaman Oriire da aka ceto ga gwamnatin Oyo

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Rundunar Sojin Nijeriya ta miƙa ɗalibai da malaman nan da aka sace na makarantu a yankin Oriire da ke Jihar Oyo ga gwamnatin jihar a hukumance bayan kammala aikin duba lafiyarsu da nazari a kai a sa'ilin da aka ceto su. A ranar, Juma'a, 10 ga Yuli, 2026 ne suka shaƙi iskar 'yanci bayan shafe kwanaki 56 a hannun 'yan bindiga. An damƙa su ne bayan sama da kwanaki biyu ana musu magani a Asibitin Shiyya ta 2 ta hedikwatar Rundunar Sojin da ke Barikin Odogbo a Ibadan. Wannan na nufin kawo ƙarshen aikin…
Read More