Labarai

INEC ta saka ranar bai wa zaɓaɓɓun gwamnoni da ‘yan majalisun jiha takardar shaidar cin zaɓe

INEC ta saka ranar bai wa zaɓaɓɓun gwamnoni da ‘yan majalisun jiha takardar shaidar cin zaɓe

Daga SANI AHMAD GIWA Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta a Nijeriya, INEC, ta ce ta saka ranakun da za ta bayar da takardar shaidar cin zaɓe ga zaɓaɓɓun gwamnoni a jihohin ƙasar da aka gudanar da zaɓen gwamna. A wata sanarwar da hukumar INEC ɗin ta fitar mai ɗauke da sa hannun shugaban kwamitin yaɗa labarai da ilimantar da masu kaɗa ƙuri'a na hukumar, Festus Okoye, ta ce sashe na 72 (1) na Dokar Zaɓen ƙasar ta 2022, ya ɗora wa hukumar alhakin bayar da takardar shaidar cin zaɓe ga zaɓaɓɓun 'yan takara a cikin kwana 14 da yin zaɓen.…
Read More
Oladipo Diya ya rasu yana da shekara 79

Oladipo Diya ya rasu yana da shekara 79

Daga BASHIR ISAH Tsohon Shugaban Ma'aikatan Fadar Shugaban Ƙasa a gwamnatin marigayi Sani Abacha, Lt-General Donaldson Oladipo Diya, ya riga mu gidan gaskiya yana da shekara 79. Ɗan marigayin, Prince Oyesinmilola Diya, shi ne ya ba da sanarwar rassuwar mahaifin nasa cikin sanarwar da ya fitar da safiyar ranar Lahadi. Sanarwar ta ce, “A madadin ahalin Diya na gida da waje, muna sanar da rasuwar maigidanmu, mahaifinmu, kakanmu, ɗan uwanmu, wato Lt- General Donaldson Oladipo Oyeyinka Diya (mai murabus) GCON, LLB, BL, PSC, FSS, mni." Marigayi Oladipo diya Sanarwar ta nuna marigayin ya cika ne ranar Lahadi, inda iyalansa suka…
Read More
Duniya na fuskantar barazanar ƙarancin ruwa – MƊD

Duniya na fuskantar barazanar ƙarancin ruwa – MƊD

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Wani rahoton Majalisar Ɗinkin Duniya ya yi gargaɗin cewa duniya na cikin barazanar fuskantar ƙarancin ruwan sha saboda amfani da buƙatar ruwa sosai da ake da ita ga kuma matsalar sauyin yanayi. "Duniya na cikin matsalar faɗa wa mawuyacin hali saboda yawan amfani da ruwa,'' inji rahoton. Wallafa rahoton na zuwa ne gabanin taron MƊD na farko kan ruwa tun 1977. Dubban wakilai ne daga sassan duniya za su halarci taron ƙolin na kwanaki uku da za a yi a birnin New York daga ranar Laraba. Sakatare Janar na MDD Antonio Guterres, ya ce…
Read More
Kotu ta yi watsi da buƙatar Abba Kyari

Kotu ta yi watsi da buƙatar Abba Kyari

Daga BAKURA MOHAMMED a Bauchi Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja ta yi watsi da buƙatar da tsohon shugaban sashen tattara bayanan sirri na rundunar 'yan sandan Nijeriya Abba Kyari ya gabatar a gabanta, yana neman kotun ta yi watsi da zarge-zargen da ake yi masa. Yayin zaman kotuna a ranar Laraba alƙalin kotun mai shari'a Emeka Nwite ya yi watsi da buƙatar Abba Kyari, yana mai cewa kotun na da hurumin sauraron ƙararrakin da suke da alaƙa da ta'ammali da miyagun ƙwayoyi kamar yadda kundin tsarin mulki da dokar da ta kafa hukumar NDLEA suka ba ta dama. Abba…
Read More
Emefiele ya roƙi gafarar ‘yan Nijeriya kan matsalar hada-hadar kuɗi ta intanet

Emefiele ya roƙi gafarar ‘yan Nijeriya kan matsalar hada-hadar kuɗi ta intanet

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Gwamnan Babban Bankin Nijeriya (CBN), Godwin Emefiele ya nemi gafara kan 'yan Nijeriya kan qalubalen da aka fuskanta kan tsarin hada-hadar kuɗi ta intanet. Emefiele ya nemi gafarar ne a taron kwamitin tsarin kuɗi na MPC da aka gudanar a ranar Talata a Abuja, inda gwamnan ya aminta da cewa, an samu ƙalubalen wanda a yanzu an warware ƙalubalen. Da yake amsa tambayoyi akan abin da ya shafi bankuna ganin yadda wasu bankuna a ƙasar Amurka ke durƙushewa, gwamnan ya ce bankuna a ƙasar nan ba za su durƙushe ba kamar yadda aka samu…
Read More
Wani soja ya yi kuskuren bindige mata da miji da jaririnsu a Neja

Wani soja ya yi kuskuren bindige mata da miji da jaririnsu a Neja

Daga AMINA YUSUF ALI Wani soja a Jihar Neja ya bindige mutane uku 'yan Jamhuriyar Benin har lahira a yankin Babana da ke ƙaramar hukumar Borgu a jihar Neja. Ciyaman ɗin ƙararmar hukumar Borgu, Alhaji Suleiman Yarima, wanda ya tabbatar da faruwar al'amarin ya roƙi al'ummar Babana da su kasance cikin lumana a game da kisan da aka yi wa danginsu, tare da ba su tabbacin cewa rundunar sojojin Nijeriya suna kula da lamarin. Kuma ya ba wa mutanen tabbacin cewa shari'a za ta nuna ikonta. Wani shaidar gani da ido kuma mazaunin yankin da abin ya faru, Audu Alkali,…
Read More
Aikata rashawa: Za mu cafke wasu gwamnoni da zarar sun sauka daga kan mulki – EFCC

Aikata rashawa: Za mu cafke wasu gwamnoni da zarar sun sauka daga kan mulki – EFCC

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Hukumar Yaƙi da Cin Hanci da Rashawa (EFCC) ta bayyana cewa, ta kammala shirye-shiryen kama tare da hukunta wasu gwamnonin da wa’adin mulkinsu ke ƙarewa waɗanda ake zargi da ayyukan rashawa. Hakazalika, EFCC ɗin bayyana shirinta na kama wasu gurɓatattun masu riƙe da muƙaman gwamnati bayan miƙa mulki a ranar 29 ga watan Mayu. Shugaban EFCC, Mista Abdulrasheed Bawa ne ya bayyana haka ranar Alhamis yayin tattaunawa da manema labarai. Sai dai Bawa bai bayyana sunaye ko kuma yawan waɗanda suke shirin kamawa ba da zarar sun sauka daga kan mulki. A sane cewa a bisa…
Read More
‘Yan Shi’a sun koka da ci gaba da tsare Sheikh El-Zakzaky

‘Yan Shi’a sun koka da ci gaba da tsare Sheikh El-Zakzaky

Daga SANI AHMAD GIWA Ƙungiyar Harkar Musulunci a Nijeriya, wato Shi'a, ta sake kokawa kan ci gaba da tsare shugabansu, Sheikh Ibraheem Yaqoub El-Zakzaky. A cewar ƙungiyar, shugabansu ba shi da cikakkiyar lafiya a lokacin da yake tsare, wanda shi ne babban dalilin da ya sa suka fara muzaharar 'Free Zakzaky' a Abuja. Idan dai ba a manta ba, duk da wasu hukunce-hukuncen da kotuna suka yanke na bayar da umarnin sakin jagoran da matarsa ​​Zeenat Ibraheem ba tare da wani sharaɗi ba, gwamnatin Buhari na ci gaba da tauye musu haqqinsu ta hanyar sanya musu takunkumin tafiye-tafiye tare da…
Read More
Mutum 21 sun mutu a hatsarin mota a hanyar a Maiduguri

Mutum 21 sun mutu a hatsarin mota a hanyar a Maiduguri

Daga ABUBAKAR M. TAHEER Wata mota ƙirar Hummer mai laba JMA 59 XA, wadda ta taso daga garin Hadejia zuwa Maiduguri ta yi haɗari wanda hakan ya yi sanadiyar mutuwar mutum 21. Lamarin ya faru ne a garin Udubo da ke Ƙaramar Hukumar Gawama, Jihar Bauchi, bayan da tayar gaban motar ta fice, hakan yasa direban motar rikicewa nan take ta doke mutane huɗu dake gefen titi ta kuma kama da wuta. Bayan zuwan jami'an 'yan sanda wurin, sun ɗauki mutum huɗu da suka ji raunuka da gawarwakin mutum 21 zuwa FMC da ke Azare. Daga nan ne aka kwashi…
Read More
Majalisa za ta binciki ƙin amincewa da gyaran wasu sassan Kundin Tsarin Mulki da Buhari ya yi

Majalisa za ta binciki ƙin amincewa da gyaran wasu sassan Kundin Tsarin Mulki da Buhari ya yi

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Majalisar Dattawan Nijeriya ta kafa wani kwamiti da zai binciki dalilin da ya sa shugaban ƙasa Muhammadu Buhari ya ƙi amincewa da ƙuduri 19 cikin 35 na kundin tsarin mulkin ƙasar da majalisar ta miƙa masa. Shugaban Majalisar Dattawa, Ahmad Lawan, a ranar Talata, 21 ga watan Maris, 2022, ya bayyana hakan a jawabinsa yayin da ake ci gaba da zama bayan kammala zaɓen gwamna da na ’yan majalisun jihohi. A makon da ya gabata ne shugaba Buhari ya rattaba hannu a kan wasu dokoki 16 na gyara kundin tsarin mulkin qasar daga cikin ƙudirori 35…
Read More