24
Apr
Daga WAKILINMU Mataimakiyar Sakatare Janar ta Majalisar Ɗinkin Duniya, Amina Mohammed, ta jaddada muhimmancin magance matsalolin ta'addanci da tallafa wa al'ummomin da abin ya shafa a faɗin Afirka. Mataimakiyar ta bayyana haka ne a yayin da aka yi wani taro na yaƙi da ta’addanci da aka gudanar a ranar Litinin a Birnin Tarayya Abuja. Ofishin Mai Ba Da Shawara kan Harkokin Tsaro (ONSA) tare da hadin gwiwar ofishin yaƙi da ta'addanci na Majalisar Dinkin Duniya UNOCT ne suka shirya. Taron ya aka yi wa taken 'Karfafa Hadin Gwiwar Yanki Da Ci Gaban Cibiyoyi Don Tinkarar Barazanar Ta'addanci a Afirka'. Amina…