14
Jul
Daga ABDULLAHI MUHAMMAD a Katsina Rundunar 'yan sanda a Katsina sun nasarar ceto mata biyu daga hannun 'yan bindiga a ƙaramar hukumar Charanchi tare da daƙile yunƙurin satar dabbobi a ƙaramar hukumar Charanchi. Kamar yadda jami'in hulɗa da jama'a na rundunar 'yan sanda a Katsina DSP Abubakar Sadiq Aliyu ya sanar, ofishin 'yan sanda a Kankia suka sami labarin cewa 'yan bindiga a kan baburan hawa ɗauke da muggan makamai sun Kai hari a matsugunin Jauga a ƙauyen Sabon Gida da ke Kankia. Ya bayyana cewa nan take jami'an 'yan sanda suka isa ƙauyen inda su kai ta ɗauki ba…
