29
Sep
Daga MAHDI M. MUHAMMAD Nijeriya ta rasa damar karɓar baƙoncin gasar kofin Afrika, bayan da aka bayyana sunan ƙasashen Kenya da Uganda da kuma Tanzania a matsayin ƙasashe uku da za su yi tarayya wajen karɓar baƙoncin gasar ta 2027. Gasar ta 2027 za ta zama karon farko da za ta gudana a gabashin Afrika tun bayan shekarar 1976 lokacin da Habasha ta karɓi baƙoncinta. A ɓangare guda makamanciyar gasar da za ta gudana a shekarar 2025 an mika damar ɗaukar nauyinta ga a Moroko bayan da Algeria da Zambia suka janye. Tun farko Nijeriya da Benin suka nemi yin…