Wasanni

Nijeriya ta rasa damar karɓar baƙoncin gasar kofin Afrika ta 2027

Nijeriya ta rasa damar karɓar baƙoncin gasar kofin Afrika ta 2027

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Nijeriya ta rasa damar karɓar baƙoncin gasar kofin Afrika, bayan da aka bayyana sunan ƙasashen Kenya da Uganda da kuma Tanzania a matsayin ƙasashe uku da za su yi tarayya wajen karɓar baƙoncin gasar ta 2027. Gasar ta 2027 za ta zama karon farko da za ta gudana a gabashin Afrika tun bayan shekarar 1976 lokacin da Habasha ta karɓi baƙoncinta. A ɓangare guda makamanciyar gasar da za ta gudana a shekarar 2025 an mika damar ɗaukar nauyinta ga a Moroko bayan da Algeria da Zambia suka janye. Tun farko Nijeriya da Benin suka nemi yin…
Read More
An kori babban sakataren hukumar ƙwallon ƙafar Sifaniya

An kori babban sakataren hukumar ƙwallon ƙafar Sifaniya

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Hukumar Ƙwallon Ƙafar Sifaniya ta kori babban sakatarenta Andreu Camps tare da neman afuwa kan abin da ya faru bayan wasan ƙarshe na cin Kofin Duniya na mata. Hukumar ta ce, ta hanzarta yi wa tsarinta garambawul domin cika alƙawarin da ta yi wa 'yan wasa. Tun da farko, mafi yawan 'yan wasan sun amince da su kawo ƙarshen kaurace wa tawagar ƙasar. 'Yan wasan sun fara ƙaurace wa tawagar ne bayan tsohon shugaban hukumar Luis Rubiales ya sumbaci 'yar wasa Jenni Hermoso lokacin nasarar da Sifaniya ta samu a kan Ingila a wasan ƙarshe na…
Read More
’Yan wasan da suka fi ɗaukar katin gargaɗi a duniyar ƙwallon ƙafa

’Yan wasan da suka fi ɗaukar katin gargaɗi a duniyar ƙwallon ƙafa

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Katin gargaɗi wato ‘Yellow Card’ kati ne wanda alƙalin wasa yake bawa ɗan wasa domin ya rage duka da sauran wasu ɗabi’u da basu kamata ba yayin da ake fafata wasa a tsakiyar fili. Akwai wasu ’yan wasa guda biyar da tarihin katin gargaɗi bazai taɓa mantawa da su ba har kawowa iyanzu. Ga jerin sunayen ’yan wasan da suka fi ɗaukar katin tun daga na 1 har zuwa na 5. Sergio Ramos: Sergio Ramos Garcia ɗan wasan ƙasar Sifaniya wanda yake fafata wasan sa a Paris saint-german da tawagar ƙasar Spain. Yana doka wasan sa…
Read More
Majalisar Tarayya: Kotu ta tabbatar da nasarar ɗan takarar NNPP a Kano

Majalisar Tarayya: Kotu ta tabbatar da nasarar ɗan takarar NNPP a Kano

Kotun Sauraren Ƙararrakin Zaɓen Majalisar Tarayya da ta jiha, ta tabbatar da nasarar ɗan takarar Jam'iyyar NNPP, Mudassir Zawachiki, a matsayin wakilin al'ummar Kumbotso a Jihar Kano a Majalisar Wakilai ya Tarayya. Kwamitin alƙalan ƙarƙashin jagorancin Mai Shari'a L. B. Owolabi, ya yi watsi da ƙarar da Sagir Abdulkadir-Panshekara na Jam'iyyar APC ya shigar inda yake ƙalubalantar nasarar Zawachiki a zaɓen da ya gudana ran 18 ga Maris, 2023. Kotu ta ce mai ƙarar ba shi da hurumi kuma ya kasa gabatar da hujjoji kan cewa an yi arigizon ƙiri'u, tada zaune tsaye da amfani da takardun bogi yayin zaɓen.…
Read More
Guardiola zai ja ragamar wasan Man City da West Ham bayan dawowa daga jinya

Guardiola zai ja ragamar wasan Man City da West Ham bayan dawowa daga jinya

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Ana sa ran Pep Guardiola zai koma Ingila ranar Laraba, domin jan ragamar wasan da Manchester City za ta kara da West Ham a gasar Firimiyar Ingila. Ranar Asabar 16 ga watan Satumba City za ta ziyarci West Ham, domin fafatawa a wasan mako na biyar a babbar gasar tamaula ta Ingila. City tana matakin farko a kan teburi da maki 12, bayan cin dukkan wasa huɗu da fara kakar nan, yayin da West Ham mai maki 10 take ta huɗu. Guardiola, wanda ya yi jinya sakamakon ciwon baya, bai ja ragamar City wasan Firimiya da…
Read More
An dakatar da Pogba kan zargin yi wa kansa allurar ƙara kuzari

An dakatar da Pogba kan zargin yi wa kansa allurar ƙara kuzari

Daga MAHDI M. MUHAMMAD An dakatar da ɗan wasan Juventus, Paul Pogba kan zargin karya dokar shan abubuwan kara kuzari ga 'yan wasa. Hukumar Hana Shan Abubuwan Ƙara Kuzarin Wasa ta Italiya (NADO) ta ce, ta samu wani sinadari fiye da ƙima a jikin Pogba, bayan tashi daga karawar da Juve ta ci Udinese 3-0 ranar 20 ga watan Agusta. Ɗan ƙwallon na tawagar Faransa, mai shekara 30 ya yi zaman benci a karawar, amma aka zaɓo shi cikin jerin 'yan wasan da aka gwada bayan karawar. Idan aka samu Pogba da laifi za a iya dakatar da shi shekara…
Read More
Wasannin da ke gaban Real Madrid cikin watan Satumba

Wasannin da ke gaban Real Madrid cikin watan Satumba

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Real Madrid za ta buga wasa biyar a cikin watan Satumba nan gaba, ciki har da huɗu a gasar La Liga da daya a gasar Zakarun Turai. Kenan cikin mako biyu za ta yi karawa biyar, wadda za ta fara da karvar baƙuncin Real Sociedad ranar Lahadi 17 ga wata a wasan mako na biyar a La Liga. Real Madrid, wadda ta ke ta ɗaya a kan teburin babbar gasar tamaula ta Sifaniya na fatan lashe karawar domin ta ci gaba da jan ragama. Kwana uku tsakani da fuskantar Sociedad za ta buga wasan farko a…
Read More
Ballon d’Or 2022/23: Messi da Haaland sun shiga jerin ’yan takara 30

Ballon d’Or 2022/23: Messi da Haaland sun shiga jerin ’yan takara 30

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Mujallar Faransa ta fitar da sunan 'yan wasa 30 da ke takarar gwarzon ɗan ƙwallon ƙafa, wato Ballon d'Or na duniya na 2022/23. Cikin 'yan wasan har da Lionel Messi da Erling Haaland, waɗanda ake hasashen wani daga ciki ka iya lashe kyautar. Wasu 'yan wasan da suka taka rawar gani da ake ganin za su iya lashe kyautar sun haɗa da Vinicius da Rodri ko kuma Kevin de Bruyne. Tsohon ɗan wasan Real Madrid, wanda ya koma taka leda a babbar gasar tamaula ta Saudiyya, Karim Benzema, shi ne gwarzon Ballon d'Or na bara. Wannan…
Read More
Arteta na takarar zama gwarzon koci a Firimiya na watan Agusta

Arteta na takarar zama gwarzon koci a Firimiya na watan Agusta

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Mikel Arteta na takarar gwarzon koci a Firimiya na watan Agusta, bayan da ya ja ragamar Arsenal wasa huɗu ba tare da an doke ƙungiyar ba. Kocin ya doke Nottingham Forest da Crystal Palace da yin 2-2 da Fulham a dai gasar ta firimiya da haɗa maki bakwai a watan na Agusta. Wannan ƙwazon na koci ya sa shi cikin koci biyar da ke takara kocin da ba kamarsa a watan na jiya. Mikel, wanda ya lashe kyauta huɗu ta gwarzon koci a firimiya a bara na takara tare da Pep Guardiola na Manchester City, bayan…
Read More
Roma da kammala ƙulla yarjejeniyar karvar aron Lukaku daga Chelsea

Roma da kammala ƙulla yarjejeniyar karvar aron Lukaku daga Chelsea

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Ƙungiyar Ƙwallon Ƙafa ta Roma ta kammala ƙulla yarjejeniyar karɓar aron Romelu Lukaku daga Chelsea wanda zai shafe tsawon kakar bana ya na takawa ƙungiyar mai doka gasar Serie A leda. Roma ƙarƙashin jagorancin Jose Mourinho ta bi sahun manyan ƙungiyoyin Turai da suka miƙa buƙatar karvar aron Lukaku ne bayan da Mauricio Pochettino ya bayyana cewa ɗan wasan baya sahun waɗanda zai yi amfani da su a wannan kaka. Lukaku ɗan Belgium mai shekaru 30 da kanshi ya zabi komawa Roma fiye da Inter Milan ƙungiyar da ya kai wasan ƙarshe na gasar kofin zakarun…
Read More