Wasanni

Real Madrid ta matsa wa UEFA lamba kan zargin Barcelona da bai wa alƙalan wasa cin hanci

Real Madrid ta matsa wa UEFA lamba kan zargin Barcelona da bai wa alƙalan wasa cin hanci

Kungiyar ƙwallon ƙafa ta Real Madrid ta buƙaci ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Turai (UEFA) da ta sake buɗe matakan ladabtarwa kan abokiyar hamayyarta ta Barcelona, tana mai cewa ta samu wasu sabbin hujjoji da ke ƙarfafa zargin da aka daɗe ana yi wa ƙungiyar dangane da biyan kuɗaɗe ga wasu jami’an alƙalanci a abin da aka fi sani da shari’ar “Negreira.” A cikin wata wasiƙa da ta aikewa UEFA, Real Madrid ta ce sabbin bayanan da take da su na ƙara ƙarfafa zargin cewa Barcelona ta riƙa biyan kuɗaɗe ga Jose Maraa Enriƙuez Negreira, tsohon mataimakin shugaban Kwamitin Fasaha na…
Read More
Mbappe ya kafa sabon tarihi a Faransa

Mbappe ya kafa sabon tarihi a Faransa

Tauraron ɗan wasan gaba na Faransa, Kylian Mbappe, ya ci gaba da rubuta tarihi bayan ya zura ƙwallaye biyu a wasan da Faransa ta doke Senegal da ci 3-1 a gasar Kofin Duniya ta 2026. Nasarar ta sa Mbappe ya zama ɗan wasan Faransa mafi yawan cin ƙwallaye a tarihin ƙasar, inda ya zarce tsoffin fitattun 'yan wasa da suka taɓa riƙe wannan matsayi. ƙwallayen nasa sun taimaka wa Faransa wajen fara gasar cikin ƙarfi, tare da ƙara mata damar kai wa matakai na gaba. Masana ƙwallon ƙafa sun yaba da yadda Mbappe ke ci gaba da nuna ƙwarewa da…
Read More
Ana binciken ɗan wasan Ivory Coast kan zargin shirya sakamakon wasa

Ana binciken ɗan wasan Ivory Coast kan zargin shirya sakamakon wasa

Jami’an tsaro a Faransa sun fara bincike kan ɗan wasan ƙasar Ivory Coast, Elye Wahi, bisa wasu zarge-zargen da suka shafi yiwuwar shirya sakamakon wasa da kuma alaƙa da harkokin caca. Rahotanni sun ce an yi wa ɗan wasan tambayoyi a matsayin wani ɓangare na binciken da ake gudanarwa, amma har yanzu ba a gurfanar da shi a gaban kotu ko kuma a same shi da wani laifi ba. Lamarin ya jawo hankalin masu bibiyar wasanni, musamman saboda yana zuwa ne a lokacin da ake gudanar da gasar Kofin Duniya ta 2026. Hukumomi sun ce binciken na ci gaba da…
Read More
Nijeriya ta zama ta biyu cikin manyan ƙasashen da suka gaza kaiwa gasar Kofin Duniya ta 2026

Nijeriya ta zama ta biyu cikin manyan ƙasashen da suka gaza kaiwa gasar Kofin Duniya ta 2026

Tawagar ƙwallon ƙafar Nijeriya, wato Super Eagles, ta zama ƙasa ta biyu mafi matsayi a jadawalin ƙasashen duniya da ba su samu tikitin shiga gasar Kofin Duniya ta FIFA 2026 ba, bisa sabon jadawalin matsayi da Hukumar ƙwallon ƙafa ta Duniya, FIFA, ta fitar. Nijeriya, wadda ke matsayi na 26 a duniya, ita ce ta biyu bayan ƙasar Denmark mai matsayi na 21, a cikin jerin ƙasashen da ke da matsayi mafi girma amma suka kasa samun gurbin shiga gasar da za a gudanar a ƙasashen Amurka, Meziko da Kanada. Rashin ganin Super Eagles a babbar gasar ƙwallon ƙafa ta…
Read More
FIFA ta tabbatar da sabbin dokokin Gasar Kofin Duniya ta 2026

FIFA ta tabbatar da sabbin dokokin Gasar Kofin Duniya ta 2026

Hukumar ƙwallon ƙafa ta Duniya (FIFA) ta tabbatar da wasu sabbin dokoki da za su fara aiki a Gasar Kofin Duniya ta 2026, matakin da ake sa ran zai taimaka wajen rage ɓata lokaci, ƙara gaskiya a yanke hukunci da kuma inganta tafiyar da wasa. Daga cikin manyan sauye-sauyen da aka amince da su akwai sanya iyaka ga lokacin da ‘yan wasa za su ɗauka wajen dawo da ƙwallo cikin wasa, canje-canjen ‘yan wasa, da kuma ƙarin amfani da fasahar Bidiyon Taimaka wa Alƙali (VAR). Sabuwar dokar jefa ƙwallo daga gefe ta tanadi cewa idan ɗan wasa ya yi gangancin…
Read More
Vinicius zai iya barin Real Madrid idan ya so – Perez

Vinicius zai iya barin Real Madrid idan ya so – Perez

Shugaban ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Real Madrid, Florentino Perez, ya bayyana cewa ba zai hana tauraron ɗan wasan gaba na ƙungiyar, Vinicius Junior, barin ƙungiyar ba idan har ya yanke shawarar komawa wata ƙungiya. Kalaman na Perez sun zo ne a daidai lokacin da ake ci gaba da tattaunawa kan sabunta kwantiragin ɗan wasan na Brazil, tattaunawar da har yanzu ba a kai ga cimma matsaya ba. Da yake magana kan raɗe-raɗin da ke yawo game da makomar Vinicius, shugaban na Real Madrid ya bayyana cewa yana da burin ganin ɗan wasan ya ci gaba da zama a ƙungiyar har…
Read More
Rikicin shugabancin Real Madrid: Mahaifin Haaland ya ƙ aryata iƙirarin ɗan takara kan sayen ɗansa

Rikicin shugabancin Real Madrid: Mahaifin Haaland ya ƙ aryata iƙirarin ɗan takara kan sayen ɗansa

Zaɓen neman shugabancin ƙungiyar Real Madrid ya rikiɗe zuwa cece-kuce mai zafi bayan da ɗan takarar shugabancin kulab ɗin, Enrique Riquelme, ya yi iƙirarin cewa, ya ƙulla yarjejeniyar sayen taurarin ƙwallon ƙafa Erling Haaland da Rodri idan ya lashe zaɓen. Riquelme, ɗan kasuwa mai harkar makamashi, ya bayyana hakan ne a shirin talabijin na El Hormiguero, inda ya nuna rigar Real Madrid mai ɗauke da sunan Haaland, yana mai cewa ɗan wasan yana da sha’awar komawa Santiago Bernabeu. Sai dai wannan iƙirari ya jawo gaggawar martani daga ɓangaren ɗan wasan, inda wakilinsa Rafaela Pimenta tare da mahaifinsa Alfie Haaland suka…
Read More
PSG ta kare kambun gasar zakarun Turai bayan doke Arsenal

PSG ta kare kambun gasar zakarun Turai bayan doke Arsenal

Daga USMAN KAROFI Ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Paris Saint-Germain (PSG) ta sake lashe kofin gasar zakarun Turai ta UEFA bayan ta doke Arsenal a wasan ƙarshe da aka buga cikin tsananin fafatawa. Wasan ya ƙare da ci 1-1 bayan ƙarin lokaci, kafin PSG ta yi nasara a bugun daga kai sai mai tsaron gida domin kare kambunta. Arsenal ce ta fara zura ƙwallo tun a minti na shida ta hannun Kai Havertz, lamarin da ya ba ta damar mamaye wasu sassan wasan. Sai dai PSG ta nuna jajircewa tare da dawowa cikin wasan, inda gwarzon ɗan wasanta Ousmane Dembélé ya…
Read More
Liverpool ta sallami Arne Slot

Liverpool ta sallami Arne Slot

Daga USMAN KAROFI Ƙungiyar ƙwallon kafa ta Liverpool ta sallami kocinta, Arne Slot, bayan ya shafe shekaru biyu yana jagorantar ƙungiyar. Rahotanni sun bayyana cewa an ɗauki matakin ne sakamakon rashin kyakkyawan sakamako a kakarsa ta biyu, duk da cewa ya lashe gasar firimiya a shekararsa ta farko. Arne Slot, mai shekaru 47, ya jagoranci Liverpool zuwa lashe kofin gasar lig na 20 a kakarsa ta farko, abin da ya ƙara masa suna a cikin kwallon kafa ta Ingila. Sai dai a kakarsa ta biyu, ƙungiyar ta fuskanci matsaloli da suka kai ta kammala kakar a mataki na biyar a…
Read More
Ronaldo ya kafa tarihi bayan zura wa kowace ƙungiya a Saudi League ƙwallo

Ronaldo ya kafa tarihi bayan zura wa kowace ƙungiya a Saudi League ƙwallo

Fitaccen ɗan wasan ƙwallon ƙafa na ƙasar Portugal, Cristiano Ronaldo, ya sake kafa wani sabon tarihi a duniya bayan jagorantar ƙungiyarsa ta Al-Nassr zuwa gagarumar nasarar 4-2 a kan Al-Shabab. Ronaldo ya cimma wannan bajinta ne bayan ya zura wa dukkan ƙungiyoyin da ya kara da su a gasar Saudi Pro League ta bana ƙwallo, abin da ya ƙara tabbatar da matsayinsa a matsayin ɗaya daga cikin fitattun ’yan wasa mafiya tarihi a duniyar tamaula. Kafin wasan, Al-Shabab ita ce kaɗai ƙungiyar da Ronaldo bai samu damar zura wa ƙwallo ba a kakar 2025/2026. Sai dai tauraron ɗan wasan ya…
Read More