Wasanni

FIFA ta kira taron gaggawa yayin da matsin lamba ke ƙaruwa kan buƙatar tsige Infantino

FIFA ta kira taron gaggawa yayin da matsin lamba ke ƙaruwa kan buƙatar tsige Infantino

Shugaban Hukumar ƙwallon ƙafa ta Duniya (FIFA), Gianni Infantino, ya kira taron gaggawa na manyan jami’an hukumar a birnin Rabat na ƙasar Moroko, yayin da ake ci gaba da fuskantar matsin lamba kan ya sauka daga muƙaminsa saboda wata taƙaddama da ta shafi shirin shigar da masu zuba jari masu zaman kansu cikin harkokin gudanar da gasar FIFA. Taron na ranar Laraba ya haɗa da Sakatare Janar na FIFA, Mattias Grafstrom, da mambobin kwamitin gudanarwar hukumar domin nazarin rikicin da ya biyo bayan shirin kafa kamfanin FIFA Forward Enterprise (FFE), wanda daga bisani aka soke. Wannan na zuwa ne a…
Read More
Sayen Vinicius babban haɗari ne ga Arsenal – Given

Sayen Vinicius babban haɗari ne ga Arsenal – Given

Tsohon mai tsaron ragar Newcastle United, Shay Given, ya gargaɗi Arsenal cewa yunƙurin sayen tauraron Real Madrid, Vinicius Junior, na iya jawo wa ƙungiyar babban haɗari. Rahotanni sun bayyana cewa Arsenal na nazarin yiwuwar ɗaukar ɗan wasan na Brazil a wata yarjejeniya mai tsadar gaske, inda ake zargin kocin ƙungiyar, Mikel Arteta, ne ke jagorantar ƙoƙarin ganin an kawo shi zuwa arewacin birnin Landan. An ce wannan yunƙuri na nuna sabon matsayi da Arsenal ta kai bayan lashe gasar Firimiya ta Ingila, tare da nuna irin ƙarfin kuɗin da ƙungiyar ke da shi a kasuwar musayar 'yan wasa. Sai dai,…
Read More
Yadda Salah ya samu gagarumar tarba a Trabzonspor

Yadda Salah ya samu gagarumar tarba a Trabzonspor

ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Trabzonspor ta Turkiyya za ta tabbatar da sayen Mohamed Salah yayin da magoya bayanta suka yi masa tarba ta karamci a lokacin da ya isa Turkiyya. ɗaruruwan magoya baya sun taru a wajen filin jirgin saman Ataturk da ke Istanbul ranar Laraba yayin da Salah ya fito sanye da kaya masu launukan Trabzonspor. ɗan wasan gaban mai shekarA 34 ya bar Liverpool a ƙarshen kakar wasa da ta gabata bayan shekara tara a Merseyside, inda ya zura ƙwallaye 257. Ba a tabbatar da albashin da Salah zai samu a Trabzonspor ba, amma tunda shi ɗan wasa…
Read More
An bai wa Vozinha izinin amfani da laƙabinsa a Colo-Colo

An bai wa Vozinha izinin amfani da laƙabinsa a Colo-Colo

Hukumar ƙwallon ƙafa ta Chile (ANFP) ta amince ta bai wa mai tsaron ragar Cape Verde, Vozinha, damar sanya sunan da aka fi saninsa da shi a bayan rigarsa ta ƙungiyar Colo Colo. Dan wasan mai shekaru 40 ya rattaba hannu kan kwantiragin watanni shida da ƙungiyar ta Chile (Liga de Primera) a ranar Litinin, bayan ya samu yabo a duniya saboda rawar da ya taka a gasar cin kofin duniya. A bisa ƙa'idojin gasar, ya kamata ya buga wasa da sunansa na asali, wato Josimar Jose Evora Dias, kasancewar dokokin ANFP sun tanadi cewa "ba a yarda a sanya…
Read More
Za ai wa ɗan wasan Manchester City Rodri tiyata

Za ai wa ɗan wasan Manchester City Rodri tiyata

Daga USMAN KAROFI Ɗan wasan tsakiya na Manchester City kuma kyaftin din tawagar ƙasar Spain, Rodri, zai shiga tiyatar baya a ranar Litinin, kamar yadda sabon kocin ƙungiyar, Enzo Maresca, ya tabbatar. Wannan na zuwa ne bayan Rodri ya taka muhimmiyar rawa wajen jagorantar Sifaniya zuwa lashe Kofin Duniya, inda kuma aka ba shi lambar gwarzon gasar. Rodri mai shekaru 30 ya sha fama da raunuka a shekarun baya-bayan nan. A kakar 2024/25, ya yi jinyar dogon lokaci sakamakon raunin jijiyar gwiwa (ACL), sannan wasu ƙarin raunuka suka rage masa yawan buga wasanni a kakar da ta gabata. Duk da…
Read More
FIFA na duba yiwuwar faɗaɗa gasar Kofin Duniya zuwa ƙasashe 64 kafin gasar 2030

FIFA na duba yiwuwar faɗaɗa gasar Kofin Duniya zuwa ƙasashe 64 kafin gasar 2030

Shugaban Hukumar ƙwallon ƙafa ta Duniya (FIFA), Gianni Infantino, ya bayyana cewa hukumar za ta yi nazari kan yiwuwar ƙara yawan ƙasashen da za su halarci Gasar Kofin Duniya daga 48 zuwa 64 kafin gasar shekarar 2030. Wannan shiri ya biyo bayan nasarar da aka samu a sabon tsarin gasar ta 2026, inda aka ƙara yawan ƙasashen da ke halarta daga 32 zuwa 48, abin da ya bai wa ƙarin ƙasashe 16 damar shiga gasar. Da yake magana a wata hira, Infantino ya ce za a mika wannan shawara ga kwamitocin da abin ya shafa na FIFA domin su tattauna…
Read More
Makaranta zan koma da zarar na yi ritaya daga ƙwallon ƙafa –Osimhen

Makaranta zan koma da zarar na yi ritaya daga ƙwallon ƙafa –Osimhen

Fitaccen ɗan wasan gaba na Super Eagles, Victor Osimhen, ya bayyana cewa yana da burin komawa makaranta domin yin karatun jami'a bayan ya yi ritaya daga taka leda, yana mai jaddada cewa ilimi na ci gaba da kasancewa muhimmin buri a rayuwarsa duk da irin nasarorin da ya samu a harkar ƙwallon ƙafa. ɗan wasan na Nijeriya ya bayyana hakan ne a wata hira da ta sake yawo a kafafen sada zumunta a ranar Litinin, inda ya waiwayi yadda rayuwarsa ta kasance, darussan da ya koya a rayuwa da kuma muhimmancin shiryawa don rayuwa bayan barin wasan ƙwallon ƙafa. Osimhen…
Read More
Kofin Duniya 2026: Manyan ƙasashe huɗu na jadawalin FIFA sun kafa tarihi a wasan kusa da na ƙarshe

Kofin Duniya 2026: Manyan ƙasashe huɗu na jadawalin FIFA sun kafa tarihi a wasan kusa da na ƙarshe

Gasar Kofin Duniya ta FIFA ta 2026 ta kafa sabon tarihi, bayan da karo na farko tun bayan fara gasar maza, ƙasashe huɗu mafi matsayi a jadawalin Hukumar ƙwallon ƙafa ta Duniya (FIFA) suka samu gurbi a wasan kusa da na ƙarshe. Rahoton BBC Sport ya nuna cewa, bayan buga wasanni sama da 100 tare da cin ƙwallaye fiye da 290 a faɗin Arewacin Amurka, wannan ne karon farko a tarihin gasar da ƙasashe huɗu mafi daraja a jadawalin FIFA suka mamaye matakin wasan kusa da na ƙarshe. Domin tabbatar da adalci da kuma rage yiwuwar manyan ƙasashe su haɗu…
Read More
An gano mahaifin tauraron ɗan wasan Faransa Michael Olise tsohon ɗan wasan cricket ne na Nijeriya

An gano mahaifin tauraron ɗan wasan Faransa Michael Olise tsohon ɗan wasan cricket ne na Nijeriya

An bayyana cewa mahaifin tauraron ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Faransa, Michael Olise, wanda ya haskakawa a Gasar Kofin Duniya ta FIFA 2026, tsohon ɗan wasan ƙungiyar cricket ta ƙasa ta Nijeriya ne. Rahoton jaridar The Sun Sport ya ce wannan sabon bayani ya jawo hankalin masu sha'awar wasanni, inda ya nuna cewa asalin hazaƙar wasanni a gidan Olise bai taƙaitu ga ƙwallon ƙafa kaɗai ba. Michael Olise, wanda ke taka leda a ƙungiyar Bayern Munich ta Jamus, na daga cikin fitattun 'yan wasan da suka taka muhimmiyar rawa a tafiyar tawagar Faransa ƙarƙashin jagorancin kocinta Didier Deschamps a gasar Kofin…
Read More
Real Madrid ta matsa wa UEFA lamba kan zargin Barcelona da bai wa alƙalan wasa cin hanci

Real Madrid ta matsa wa UEFA lamba kan zargin Barcelona da bai wa alƙalan wasa cin hanci

Kungiyar ƙwallon ƙafa ta Real Madrid ta buƙaci ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Turai (UEFA) da ta sake buɗe matakan ladabtarwa kan abokiyar hamayyarta ta Barcelona, tana mai cewa ta samu wasu sabbin hujjoji da ke ƙarfafa zargin da aka daɗe ana yi wa ƙungiyar dangane da biyan kuɗaɗe ga wasu jami’an alƙalanci a abin da aka fi sani da shari’ar “Negreira.” A cikin wata wasiƙa da ta aikewa UEFA, Real Madrid ta ce sabbin bayanan da take da su na ƙara ƙarfafa zargin cewa Barcelona ta riƙa biyan kuɗaɗe ga Jose Maraa Enriƙuez Negreira, tsohon mataimakin shugaban Kwamitin Fasaha na…
Read More