Wasanni

Xavi ya yi amai ya lashe kan batun barin Barcelona

Xavi ya yi amai ya lashe kan batun barin Barcelona

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Kocin Barcelona, Xavi Hernandez ya sauya shawararsa na barin Barcelona a ƙarshen kakar wasa ta bana kuma zai ci gaba da zama koci bayan tattaunawa da shugaban kulob ɗin, Joan Laporta, da shugabannin ƙungiyar a ranar Laraba. An ruwaito Xavi ya gana da shugaban ƙungiyar, Joan Laporta da daraktan wasanni, Deco, a daren Laraba. Bayan taron ya sauya ra'ayi kuma ya amince da sharuɗɗan ci gaba da jagorantar ƙungiyar ta LaLiga. Ƙwararre a harkar wasan ƙwallon aafa Fabrizio Romano ya bayyana hakan a shafinsa na X. Romano ya rubuta: Xavi ya yanke shawarar canja ra'ayinsa ya…
Read More
Birnin Leverkusen ya bai wa ɗan Nijeriya, Boniface, shaidar zama ɗan ƙasa

Birnin Leverkusen ya bai wa ɗan Nijeriya, Boniface, shaidar zama ɗan ƙasa

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Majalisar Birnin Leverkusen ta bai wa Victor Boniface, Nathan Tella da sauran zakarun gasar Bundesliga takardar shaidar zama ɗan qasa na girmamawa. A ranar Lahadi Bayer Leverkusen ta lashe gasar Bundesliga ta farko bayan da ta lallasa Werder Bremen da ci 5-0 inda Victor Boniface ya zura ƙwallon farko sannan kuma ya taimaka aka zura sauran ƙwallayen. Victor Boniface yana ɗauke da fasfo na Nijeriya, yayin da Tella baya ga koren fasfo ɗinsa kuma yana da fasfo na ƙasar Birtaniya kamar yadda iyayen Nijeriya suka haife shi a Ingila.
Read More
Ɗan Nijeriya ya shiga jerin manyan ’yan wasan Tennis na duniya

Ɗan Nijeriya ya shiga jerin manyan ’yan wasan Tennis na duniya

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Wani rahoto da Hukumar Shirya Gasar Tennis ta Duniya, ITTF, ta fitar ya nuna cewa ɗan Nijeriya Quadri Aruna ya shiga jerin manyan ’yan wasan Tennis 20 na duniya. A cikin jadawalin da hukumar ta fitar, ɗan Nijeriyar ya samu matsayi na 19. A jadawali 2 na baya-bayan nan da hukumar ta fitar, Aruna na matsayi na 22 bayan da ya yi rashin nasara a gasar kofin Tennis ta duniya wadda ta gudana a ƙasar Koriya. Yayin da zakaran gasar a Nahiyar Africa Ɗan Ƙasar Masar Omar Assar, shima ya samu matsawa gaba zuwa matsayi na…
Read More
A karon farko cikin shekaru 120 Bayer Leverkusen ta zama zakaran gasar Bundesliga

A karon farko cikin shekaru 120 Bayer Leverkusen ta zama zakaran gasar Bundesliga

Daga IBRAHIM HAMISU Ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Bayer Leverkusen ta zama zakarar gasar Bundesliga na Jamus na shekarar 2023/2024, karon na farko da kafa ƙungiyar shekara 120 da ta gabata, bayan da suka samu nasara a kan Weder Bremen da ci 5-0. Nasarar da suka samu ta kawo ƙarshen shekaru 11 da Bayern Munich ta yi tana lashe gasar. Wannan dai shi ne karo na farko da Bayer Leverkusen suka taɓa lashe gasar a tarihi, ida suka gaza ɗaukar kofin a shekarar 2002 a ranar ƙarshe ta gasar. Har ila yau, a dai wannan shekarar ne su kayi rashin nasara…
Read More
Sifaniya ta hana tawagar Nijeriya bizar zuwa wasanni ƙasarta

Sifaniya ta hana tawagar Nijeriya bizar zuwa wasanni ƙasarta

Daga MAHDI M. MUH'D Hukumar Ƙwallon Ƙafar Nijeriya, NFF, ta ce Ƙasar Sifaniya ta hana ’yan wasan tawagar Nijeriya ta 'yan ƙasa da shekara 15 bizar zuwa buga gasa ƙasar. Ta ce, hana bizar ya shafi 'yan wasa da jami'an da ke cikin tawagar masu lura da su. Don haka, "tawagar ba za ta je Sifaniya ba domin buga gasar UEFA ta 'yan ƙasa da shekara 16," kamar yadda NFF ta wallafa a shafinta na X. Sifaniya dai ba ta bayyana dalilin hana bizar ba. Sai dai hukumomin Sifaniya sun ce dalilin da Hukumar NFF ta bayar na neman bizar…
Read More
Doke Real Madrid sau biyu a jere ba abu ne mai yiwuwa ba, inji Guardiola gabanin karawar UCL

Doke Real Madrid sau biyu a jere ba abu ne mai yiwuwa ba, inji Guardiola gabanin karawar UCL

Daga MAHDI M. MUH'D Kocin Manchester City, Pep Guardiola ya bayyana cewa ƙungiyarsa na fuskantar babban ƙalubale idan suka kara da Real Madrid a gasar La Liga. Idan dai ba a manta ba, Man City ta fitar da 'yan wasan Carlo Ancelotti a kakar wasan da ta gabata a cikin salo mai ban sha'awa (ci 5-1) a hanyarsu ta ɗaukar kofin zakarun Turai na UEFA a karon farko a tarihinsu. Pep Guardiola ya tattaro haziƙan ’yan wasansa wajen ganin sun lallasa Real Madrid da ci 4-0 a wasan daf da na kusa da ƙarshe a filin wasa na Etihad bayan…
Read More
PSG ta kai wasan ƙarshe a gasar kofin Faransa

PSG ta kai wasan ƙarshe a gasar kofin Faransa

Daga MAHDI M. MUH'D Ƙungiyar ƙwallon koafa ta PSG ta samu kaiwa wasan ƙarshe na kofin Faransa wato French Cup bayan ƙwallon ɗaya tilo da Kylian Mbappe ya zura a ragar Rennes daren ranar Laraba a wasan daf da na ƙarshe da suka doka tsakaninsu. A minti na 40 daf da tafiya hutun rabin lokaci ne Mbappe ya zura ƙwallon bayan tun farko mai tsaron ragar Rennes Steve Mandanda ya varar da fenaritin da tauraron na Faransa ya buga a minti na 33. Mbappe wanda ke matsayin mafi zurawa PSG ƙwallo na taka leda ne a kakarsa ta ƙarshe a…
Read More
Super Eagles ta taki sabon matsayi a jadawalin FIFA

Super Eagles ta taki sabon matsayi a jadawalin FIFA

Daga MAHDI M. MUH'D A yanzu haka tawagar Super Eagles ta Nijeriya ta taki matsayi na 33 inda ta sha gaban abokiyar hamayyarta ta yammacin Afirka a sabon jadawalin FIFA bayan da ta doke ta da ci 2-1 a wasan sada zumunta da suka yi a watan jiya. Duk da cewa sau biyu tawagar Super Eagles ta Nijeriya tana faɗuwa ƙasa a sabuwar kimar hukumar ta FIFA, amma har yanzu zakarun Afirkan na gaban Ghana da ke yammacin Afirka. Super Eagles dai ta kasance ta 28 a duniya a jadawalin watan Fabrairu amma ta koma mataki na 30 a kimar…
Read More
Diawara ya soke kwataraginsa da Faransa bayan haramta wa ’yan wasa yin azumi

Diawara ya soke kwataraginsa da Faransa bayan haramta wa ’yan wasa yin azumi

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Hukumar Ƙwallon Ƙafar Ƙasar Faransa ta gayyaci Dehmaine Tabibou Assoumani na ƙungiyar Nantes a matsayin wanda zai maye gurbin ɗan wasan tsakiyar tawagar ’yan ƙasa da shekara 19 ta ƙasar. Ɗan wasan tsakiyar Mahamadou Diawara ya yanke shawarar barin tawagar ne bayan da hukumar ƙawallon ƙafa ta ƙasar ta kafa wasu sabbin dokoki waɗanda suka haramtawa 'yan wasa Musulmi yin azumin watan Ramadan a lokacin da suke atisaye. Diawara bai ji dadin sabbin dokokin ba, waɗanda aka fara aiwatar da su tun daga matakin tawagar ’yan qasa da shekaru 16 har zuwa babbar tawagar ƙasar. Wannan…
Read More
Zan bayyana makomata bayan gasar kofin Turai – Mbappe

Zan bayyana makomata bayan gasar kofin Turai – Mbappe

Sga MAHDI M. MUHAMMAD Ɗan wasan gaba na PSG Kylian Mbappe ya ce zai bayyana matsayarsa na gaba bayan gasar kofin nahiyar Turai ta 2024. Ɗan wasan na Faransa ya yi magana a karon farko game da raɗe-raɗin da ake yi na yarjejeniyarsa da Real Madrid a bazara. A yayin da yake magana a gidan jaridar Faransa, ya ce “Ban sanar da komai ba saboda babu abin da zan sanar. "Zan bayyana makomata kafin gasar kofin Turai." Dangane da gasar Olympics ta Paris, Mbappe ya ce: “A koyaushe ina da wannan buri, abu ne na musamman kuma a koyaushe ina…
Read More