Wasanni

Hada-hadar ’yan wasan ƙwallon ƙafa

Hada-hadar ’yan wasan ƙwallon ƙafa

Real Madrid ta nuna matsuwa kan ɗan wasan Bournemouth mai shekara 19 daga Sifaniya, Dean Huijsen, wanda cikin yarjejeniyarsa ake iya biyan fam miliyan 50 domin sayensa ga wata ƙungiya. Barcelona na duba yiwuwar mallake ɗan wasan Newcastle mai shekara 27 daga Brazil, Bruno Guimaraes, wanda ƙungiyoyin Arsenal da Manchester City ke zawarci. Dan wasan tsakiya a Bayern Munich da Jamus, Joshua Kimmich mai shekara 30 na son zuwa Arsenal, yayinda ita ma Paris St-Germain ke nuna zawarcinta. Dan wasan Manchester United da Brazil, Antony mai shekara 25, ya nuna sha'awar cigaba da zama a Real Betis idan yarjejeniyar zaman…
Read More
Arsenal ta kafa sabon tarihi a gasar Zakarun Turai

Arsenal ta kafa sabon tarihi a gasar Zakarun Turai

Kwallaye bakwai da ƙungiyar Arsenal ta jefa a ragar PSɓ Eindhoɓen a karawar da suka yi, ya ba ta damar kafa sabon tarihi a gasar zakarun Turai. Wannan nasara da Arsenal ta samu a filin wasa na Philips, irin ta ce ta farko da wata ƙungiya da ta je baƙunci ta taɓa samu a zagayen ’yan 16 a gasar zakarun Turai. Bayan tashi daga wasan, mai horas da ƙungiyar ta Arsenal Mikel Arteta, ya ce ’yan wasansa sun yi mura da wannan nasarar da suka samu kan PSɓ ta 7-1. "Gaskiya abin farin ciki ne, ina farin ciki da kasancewa…
Read More
Ban taɓa nuna wa wani ɗan wasa wariyar launin fata ba – Mourinho

Ban taɓa nuna wa wani ɗan wasa wariyar launin fata ba – Mourinho

Kocin Fenerbahce Jose Mourinho ya ce shi "sun yi hannun riga da wariyar launin fata" bayan an zarge shi da yin kalaman wariya ka 'yan wasan Galatasaray. Galatasaray ta ce za ta "kai ƙara kotu" game da kalaman na Mourinho saboda ya yi "kalaman wariya" bayan karawar da suka tashi 0-0 a tsakaninsu ranar 24 ga watan Fabrairu. "Ba su yi dabara ba a suka ta da suka yi, saboda ba su san tarihina ba," kamar yadda ya shaida wa Sky Sports. "Ba su san alaƙata da Afirka ba, da 'yan Afirka, da 'yan wasan Afirka, da ƙungiyoyin agaji na…
Read More
LeBron James ya zama ɗan wasan NBA na farko da ya zura ƙwallaye 50,000

LeBron James ya zama ɗan wasan NBA na farko da ya zura ƙwallaye 50,000

James ya kai maki 50,000 a kakar wasannisa 22, wanda ake alaƙanta shi da ɓince Carter na wanda ya fi zura ƙwallaye a kwando a tarihin gasar NBA. LeBron James ya zama ɗan wasan ƙwallon ƙwando ta Amurka na farko a tarihi da ya zura ƙwallaye 50,000, idan aka hada da ƙwallayen da ya ci kafin da kuma lokacin kakar wasanni a daren ranar Talata. James ya fara da wani bugu mai kyau da ya zura ƙwallo da maki 3 a farko zagaye na farko na wasan Los Angeles Lakers da New Orleans Pelicans. James ya samu maki 49,999 a…
Read More
An dakatar da Bellingham daga buga wasa biyu a La Liga

An dakatar da Bellingham daga buga wasa biyu a La Liga

An dakatar da ɗan wasan Real Madrid, Jude Bellingham daga buga wasa biyu a La Liga, sakamakon jan katin da aka yi masa a wasan Osasuna. Real Madrid ta tashi 1-1 a wasan mako na 24 da ta je gidan Osasuna ranar Asabar 15 ga watan Fabrairu. An kori ɗan wasan tawagar Ingila a karawar a minti na 39, saboda faɗar kalaman da ba su da ce ba ga rafli, Jose Luis Munuera. Kenan Bellingham ba zai yi wa Real Madrid wasan La Liga da za ta fafata da Girona da kuma Real Betis ba. Tuni Real Madrid, wadda take…
Read More
Yadda Real Madrid ta fitar da Man City daga gasar Zakarun Turai

Yadda Real Madrid ta fitar da Man City daga gasar Zakarun Turai

Real Madrid ta fitar da Manchester City a wasan cike gurbi a Gasar Zakarun Turai, bayan da ta ci 3-1 ranar Laraba a Santiago Bernabeu. Real Madrid ta kai zagayen gaba da cin 6-3 gida da waje kenan, bayan da ta yi nasara 3-2 a Etihad ranar Talata 11 ga watan Fabrairu. City ta ci ƙwallo biyu ta hannun Erling Haaland a Etihad, yayin da Kylian Mbappe da Brahim Diaz da Jude Bellingham suka ci wa Real Madrid ƙwallayenta. Kylian Mbappe ne ya fara cin ƙwallo a minti na 4 da fara wasan, karon farko da Real ta ci ƙwallo…
Read More
Lookman ya bayyana takaici kan kalaman kocinsa

Lookman ya bayyana takaici kan kalaman kocinsa

Ademola Lookman ya ce, ya ji takaicin irin kalaman da kocinsa Gian Piero Gasperini ya yi a kansa, bayan da ya kwatanta ɗan wasan da "wanda ya fi kowa rashin iya buga fenareti" da ya taɓa gani. Kocin ya yi kalaman ne bayan da Atalanta ta yi rashin nasara a hannun Club Brugge da ci 3-1 ranar Talata a gasar Zakarun Turai, abu kuma da ya sa ƙungiyar ta fice daga gasar da ƙwallo 5-1 gida da waje. "Abin ɓacin rai ne in yi martani a irin wannan rana, saboda abin da muka cimma a matsayin ƙungiya," kamar yadda Lookman…
Read More
Man United za ta ƙara rage ma’aikata

Man United za ta ƙara rage ma’aikata

Daya daga wanda ya yi haɗakar mallakar Manchester United, Sir Jim Ratcliffe na duba yiwuyar yadda za a ƙara rage ma'aikatan ƙungiyar. Wata majiya ta tabbar da cewar Man United na duba yadda za ta kara rage kuɗin da take kashewa da zai kai yuro miliyan 300 a shekara uku. Man United ba ta ce komai ba kan rahoton cewar Ineos Group, ƙarƙashin Ratcliffe na auna yadda zai sake rage ma'aikata kimanin 100 zuwa 200 ba. Daga baya ne za a fayyace yawan ma'aikatan da za a rage da guraben da suke aiki, domin aiwatar da shirin. Haka kuma United…
Read More
Shahararrun ’yan wasa da asalinsu ‘yan Nijeriya ne amma suke wakiltar wasu ƙasashe

Shahararrun ’yan wasa da asalinsu ‘yan Nijeriya ne amma suke wakiltar wasu ƙasashe

Akwai wasu zaratan 'yan ƙwallo da asalinsu 'yan Nijeriya ne, amma suke wakiltar wasu ƙasashen duniya. Wasu zaratan 'yan ƙwallo da tauraronsu ke haskawa a duniya, waɗanda asalin 'yan Nijeriya ne, wato ko dai iyayensu bakiɗaya ko wani ɓangare daga cikin iyayen nasu ’yan Nijeriya ne. Na farko shi ne - Jamal Musiala: Jamal Musiala, wanda aka haifa a ranar 26 ga Fabrairun shekarar 2003, fitaccen ɗan ƙwallon ƙasar Jamus ne da ƙungiyar Bayern Munich ta Jamus ɗin kuma yana cikin matasan 'yan ƙwallon da suke tashe a duniya a yanzu. An haife shi ne a garin Stuttgart da ke…
Read More
Kano Pillars ta dakatar da kocinta, Usman Abdallah

Kano Pillars ta dakatar da kocinta, Usman Abdallah

Hukumar Gudanarwar ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Kano Pillars, ta dakatar da mai horar da 'yan wasanta, Usman Abdallah har tsawon makonni uku. Sanarwar da shugaban hukumar gudanarwar ƙungiyar, Alhaji Ali Muhammad Umar ya fitar, ta ce mataimakin mao horarwar, Ahamd Garba Yaro-Yaro ne zai ci gaba da riƙon muƙamin nasa. Wannan ya biyo bayan rashin kataɓus ɗin da ƙungiyar ta yi a baya-bayan nan, haɗi da harzuƙa magoya bayan ƙungiyar, bayan tashi daga wasan da Kano Pillars din ta yi kunnen doki da Bayelsa United a filin wasa na Sani Abacha da ke Kano. Sanarwar ta ci gaba da cewa,…
Read More