Daga MAHDI M. MUH’D
Kocin Manchester City, Pep Guardiola ya bayyana cewa ƙungiyarsa na fuskantar babban ƙalubale idan suka kara da Real Madrid a gasar La Liga.
Idan dai ba a manta ba, Man City ta fitar da ‘yan wasan Carlo Ancelotti a kakar wasan da ta gabata a cikin salo mai ban sha’awa (ci 5-1) a hanyarsu ta ɗaukar kofin zakarun Turai na UEFA a karon farko a tarihinsu.
Pep Guardiola ya tattaro haziƙan ’yan wasansa wajen ganin sun lallasa Real Madrid da ci 4-0 a wasan daf da na kusa da ƙarshe a filin wasa na Etihad bayan da suka tashi babu ci a Bernabeu.
Wannan rashin nasara dai wani babban rauni ne ga Real Madrid wadda ta lashe kofin gasar zakarun Turai, wadda ke yunƙurin ɗaukar kofin zakarun Turai karo na sha biyar a tarihinta.
Yanzu dai ɓangarorin biyu sun sake karawa – a wannan karon a wasan daf da na kusa da ƙarshe a gasar ɗaya kuma Pep Guardiola na fatan kare kambunsa.
Da yake magana gabanin fafatawar, Guardiola mai shekaru 53 ya ce baya tsammanin faruwar irin wannan lamari da ya faru a karon baya.
Ya ƙara da cewa, Real Madrid za ta yi waje domin ɗaukar fansa.
Guardiola ya ce: “Yana da matuƙar wahala irin wannan abu ya sake faruwa, doke Real Madrid sau biyu a jere ba zai yiwu ba, sun koyi kuma za su so ɗaukar fansa.”
A halin yanzu, Carlo Ancelotti yana son ƙungiyarsa ta nuna ƙarfin hali a karawarsu ta gaba.
Karawar Real Madrid da Manchester City wasa ne mai cike da ruɗani. Yayin da za a kalli furucin na Pep Guardiola a matsayin wasa na hankali, ana sa ran Real Madrid za ta ɗauki darasi da babban kashin da ta sha a kakar wasan da ta wuce.