Doke Real Madrid sau biyu a jere ba abu ne mai yiwuwa ba, inji Guardiola gabanin karawar UCL

Daga MAHDI M. MUH’D

Kocin Manchester City, Pep Guardiola ya bayyana cewa ƙungiyarsa na fuskantar babban ƙalubale idan suka kara da Real Madrid a gasar La Liga.

Idan dai ba a manta ba, Man City ta fitar da ‘yan wasan Carlo Ancelotti a kakar wasan da ta gabata a cikin salo mai ban sha’awa (ci 5-1) a hanyarsu ta ɗaukar kofin zakarun Turai na UEFA a karon farko a tarihinsu.

Pep Guardiola ya tattaro haziƙan ’yan wasansa wajen ganin sun lallasa Real Madrid da ci 4-0 a wasan daf da na kusa da ƙarshe a filin wasa na Etihad bayan da suka tashi babu ci a Bernabeu.

Wannan rashin nasara dai wani babban rauni ne ga Real Madrid wadda ta lashe kofin gasar zakarun Turai, wadda ke yunƙurin ɗaukar kofin zakarun Turai karo na sha biyar a tarihinta.

Yanzu dai ɓangarorin biyu sun sake karawa – a wannan karon a wasan daf da na kusa da ƙarshe a gasar ɗaya kuma Pep Guardiola na fatan kare kambunsa.

Da yake magana gabanin fafatawar, Guardiola mai shekaru 53 ya ce baya tsammanin faruwar irin wannan lamari da ya faru a karon baya.

Ya ƙara da cewa, Real Madrid za ta yi waje domin ɗaukar fansa.

Guardiola ya ce: “Yana da matuƙar wahala irin wannan abu ya sake faruwa, doke Real Madrid sau biyu a jere ba zai yiwu ba, sun koyi kuma za su so ɗaukar fansa.”

A halin yanzu, Carlo Ancelotti yana son ƙungiyarsa ta nuna ƙarfin hali a karawarsu ta gaba.

Karawar Real Madrid da Manchester City wasa ne mai cike da ruɗani. Yayin da za a kalli furucin na Pep Guardiola a matsayin wasa na hankali, ana sa ran Real Madrid za ta ɗauki darasi da babban kashin da ta sha a kakar wasan da ta wuce.