Daga IBRAHIM HAMISU a Kano
Shugaban ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Kano Pillars, Alh. Babangida Little, ya bayyana dakatar da mai horar da ‘yan wasan ƙungiyar, Abdu Maikaba, a ranar Talata.
Babangida Little ya bayyana dakatarwar da kuma kafa wani kwamiti wanda zai binciki kocin kuma idan aka same shi da laifi, to, zai fuskanci ladaftarwa.
Kawo yanzu ba a bayyana ainihin dalilin dakatarwar da aka yi masa ba, sai dai wasu na zargin furucin da Abdu Mai-kaba ya yi a lokacin wani taro da ƙungiyar magoya bayan Kano Pillars suka yi a cibiyar ‘yan Jaridu ta jiha ne ya haifar da dakatarwar.
A saurari ƙarin bayani….