Mata A Yau

Mun sha zama da majalisar dokoki kan ilimin mata – Nafisa Halliru

Mun sha zama da majalisar dokoki kan ilimin mata – Nafisa Halliru

"Tun 2012 zuwa yau nake ba wa gwamnatin Jigawa gudunmawa wajan cigaban ilimi" Daga UMAR AKILU MAJERE Hajiya Nafisa Halliru Haruna wata fitacciyar ýar gwagwarmayar ƙungiyoyi ce da sunanta ya jima a harkar Jihar Jigawa akan harkokin ilimi da kiwon lafiya. Hajiya Nafisa tana ɗaya daga cikin mata da suka sadaukar da rayuwarsu domin cigaban al'umma musamman wajan ganin ta sanya 'ya'ya mata sun shiga andama wajan samun ilimin boko da na zamani. Nasani mai karatu zai so ya ji tarihin hajiya Nafisa da jin asalinta ko daga ina ta fito? Hajiya Nafisa Halliru an haife ta a garin Birnin…
Read More
Ni ke yi wa mijina komai duk da cewa ina aiki – Hannatu Muhammed

Ni ke yi wa mijina komai duk da cewa ina aiki – Hannatu Muhammed

"Ba addinin da ya bai wa mata gata kamar Musulunci" "Duk wadda za ta zuga ki ki yi wa mijinki rashin kunya ba mai son ki ba ce" (Ci gaba daga makon jiya) Daga UMAR GARBA a Katsina  A satin da ya gabata, mun faro tattaunawa da jajirtacciyar 'yar jarida, kuma shugabar ƙungiyar mata 'yan jarida ta Jihar Katsina, wato NAWOJ. A tattaunawar mun taɓo ɓangarori da dama, wanda muka yada zango a tambayar da muka yi alƙawarin kawo maku amsarta kafin wasu su biyo baya. Har wa yau dai, wakilinmu a Katsina, Umar Garba ne ke jan ragamar tattaunawar.…
Read More
Ko namiji aka ci zarafinsa za mu tsaya ma shi – Hannatu Muhammed 

Ko namiji aka ci zarafinsa za mu tsaya ma shi – Hannatu Muhammed 

"Dalilin shugabancina mata sun samu 'yanci a Katsina" Daga UMAR GARBA a Katsina Hajiya Hannatu Muhammed ita ce Shugabar ƙungiyar Mata 'Yan Jarida Reshen Jihar Katsina, wato NAWOJ, a halin yanzu ita ce mataimakiyar babban manja na gidan talabijin na ƙasa, wato NTA da ke Katsina, ta yi fice a fannoni da dama kama daga gabatar da shirye shirye a gidan talabijin, bai wa mata shawara game da yadda zasu kyautata zamantakewa da iyalansu. Kazalika fitacciyar 'yar jaridar ta kasance 'yar gwagwarmaya da ke wayar da kan mata don su fuskanci ƙalubalen rayuwa da ke gabansu. Wakilin Manhaja a Katsina…
Read More
Kwalliya ce jarin ‘ya mace – Hauwa Ibrahim

Kwalliya ce jarin ‘ya mace – Hauwa Ibrahim

“Tun ban fi shekara 18 ba na fara aikin gwagwarmaya"  Daga AISHA ASAS A yanzu dai kai ya waye, kusan na ce birni da ƙauye mun aminta mace mai sana'a ita ce mace, wadda ba ta yi kuwa ta rako su ne. Muhimmancin sana'a ga 'ya mace ba zai misaltu ba, hakan ya sanya a kullum ake faɗa tare da janyo hankalin mata kan neman na kai. A wannan satin filin mata a yau ya yi wa masu karatu babban kamu, inda mu ka ɗauko maku ɗaya daga cikin matan da su ka cancanci a kirasu da Gimbiya saboda jajircewa…
Read More
Ko a tarbiyya za a gane ‘ya’yan mace mai ilmi – Dakta Erisa Danladi

Ko a tarbiyya za a gane ‘ya’yan mace mai ilmi – Dakta Erisa Danladi

"Ina cikin mata masu ƙananan shekaru da suka yi fice a duniya"  Daga ABUBAKAR A. BOLARI, a Gombe Dakta Erisa Sarki Danladi, Babbar manomiya ce kuma yar gwagwarmaya a ɓangaren ayyukan raya karkara, kuma mai fafutuka tsakanin ƙungiyoyin da ba na gwamnati ba wato NGO's. Mace mai ƙoƙarin taimakon marasa galihu. Gatan marar gata. Ita ce babbar daraktar ƙungiyar nan mai suna 'Motherhen Deɓelopment Foundation', da ta ke koyawa mata da matasa sana’o'in hannu, sannan kuma ko-odinata ce ta Arewa maso Gabas ta wata ƙungiyar tallafa wa mata 'yan siyasa wato 'women in political empowerment', da sauran ƙungiyoyi da dama…
Read More
Ku bar mata su nemi na kansu – Jiddah Nguru 

Ku bar mata su nemi na kansu – Jiddah Nguru 

“A wannan zamani kusan dole ne neman na kai ga ’ya mace” Daga AISHA ASAS  Kalmar neman na kai ga 'ya mace na da ma'anoni da dama a tsakanin al'umma, musamman a ƙasar Hausa. Yayin da ka ce, ku ƙyale 'ya'ya mata su nemi na kansu, wasu kan fassara hakan da ku bar mata su lalace, ko su ba wa mata dama su zama kamar maza, ko kuma su bar mata su yi yadda suke so. Wasu kuma sai suke ganin kamar hanya ce ta yaɗa manufofin Yahudu.  Wannan na ɗaya daga cikin dalilan da suke sa wasu mazan tirjiya…
Read More
Akwai buƙatar dawo wa da sarakuna ƙarfin mulkin da suke da shi a baya – Gimbiya Umma Usman Nagoggo

Akwai buƙatar dawo wa da sarakuna ƙarfin mulkin da suke da shi a baya – Gimbiya Umma Usman Nagoggo

"Mata ba su da wata rawa da suke takawa a masarautun ƙasar Hausa" Daga ABBA ABUBAKAR YAKUBU Shafin Gimbiya na wannan makon ya lalubo muku Gimbiya ce ta gaske, domin kuwa tana daga cikin ýaýa 42 da tsohon Sarkin Katsina marigayi Usman Nagoggo ya haifa, wato Hajiya Umma Hassan, ýar uwa ga marigayi Janar Hassan Usman Katsina, tsohon Gwamnan tsohuwar Jihar Arewa. Gimbiya ýar sarki, matar sarki, kuma uwar sarki, wacce ta shafe tsawon shekaru tana hidima ga al'umma da taimakon raunana, kuma mamba a Jam'iyyar Matan Arewa. A zantawarta da wakilin Blueprint Manhaja Abba Abubakar Yakubu, Gimbiya Umma Hassan…
Read More
Chayilo: Yarinyar da mijin mahaifiyarta ya maida tamkar kuyangar sa

Chayilo: Yarinyar da mijin mahaifiyarta ya maida tamkar kuyangar sa

"Chayilo ta sanar da mahaifiyar ta abinda mijinta ke yi mata, amma ta hauta da faɗa" Daga COMFORT MUKOLLO a Gombe  Shafin Gimbiya na wannan mako ya yi waiwaye kan yadda cin zarafin 'ya'ya mata ya yawaita musamman a Arewacin Nijeriya, inda yara ƙanane da ma manya ke fuskantar barazanar cin zarafi, abin takaici kaso mai yawa daga cikinsu makusantansu ne ke keta masu haddi. Da wannan ne shafin namu ya yi ɗamarar bada gudunmawa ta hanyar wallafa rahotannin da bayyanai da ka iya taimako ko ƙwato haƙƙin waɗanda aka ci zarafinsu, ko bada kariya ga waɗanda ba su faɗa…
Read More
Ta yaya za ki kula da fatarki a lokacin sanyi

Ta yaya za ki kula da fatarki a lokacin sanyi

Daga AISHA ASAS  Yayin da aka ce sanyi ya ƙarato, mutane da yawa suna tausayawa halin da fatarsu za ta shiga yayin da suka yi arangama da yanayin na sanyi. A lokacin sanyi fata na yamushewa saboda yanayin iskar hunturu, kuma yakan yi muni musamman ga waɗanda ba su san yadda za su ba wa fatar tallafi ba. Yanayin sanyi ba iya fata ya tsaya ba, domin hunturu na taɓa lafiyar gashi, ta hanyar yawan karyewa, sai kuma uwa uba kaushi ko fasau da ƙafa ke yi. Waɗannan matsalolin na lokacin sanyi na sauya fasalin jiki tare da sanya shi…
Read More
Rayuwar mata bayan mutuwar miji

Rayuwar mata bayan mutuwar miji

Daga AISHA ASAS Akwai bambanci sosai tsakanin wadda aka saki da wadda mijin ya mutu - Sa'adatu Kankia  “Ta hanyar gina matanku ne kawai za ku samun tabbacin ‘ya’yanku ba za su tagayyara bayan mutuwarku” Kamar yadda aka sani, shafin Gimbiya na jaridar Blueprint Manhaja bai tsaya a iya tattaunawa da mata kan rayuwarsu ba. Shafin kan taɓo matsaloli, cigaba da kuma wani abu da ke ciwa mata tuwo a ƙwarya, don tattaunawa da kuma nema masu mafita. A yau shafin zai yi duba kan halin da mata ke shiga bayan mutuwar mazajensu, wanda ba kasafai ake fahimtar halin da…
Read More