Mata A Yau

Hankalina na tashi idan na ga wanda baya da abin ci da iyalinsa – Aunty Sadiya Kaduna

Hankalina na tashi idan na ga wanda baya da abin ci da iyalinsa – Aunty Sadiya Kaduna

"Burina in ga maraya cikin farin ciki kamar kowa" Daga AISHA ASAS Hajiya Sadiya Abdullahi wadda mutane da yawa suka fi sani da Antin KD, kuma wadda ta kasance 'yar gwagwarmaya da fafutikar ganin marayu da gajiyayyu sun ɗanɗana irin daɗin da masu iyaye da masu hali suke ji a rayuwarsu, ta fuskar tallafa masu da abinci, suturu, da kuma ƙoƙarin inganta lafiyarsu ta hanyar gidauniyar ta. A cikin tattaunawar ta da jaridar Blueprint Manhaja za ku ji wacce ce ita, gwagwarmayar ta da kuma sirrin shaharar ta. MANHAJA: Bari mu fara da jin taƙaitaccen tarihinki. SADIYA KADUNA: Assalamu alaikum.…
Read More
Matan aure barka da Ramadan! (3)

Matan aure barka da Ramadan! (3)

Tare da AMINA YUSUF ALI Masu karatu barkanmu da sake kasancewa a wani makon a filinku mai albarka a jaridarku mai farin jini ta Blueprint Manhaja. A wannan mako mun zo muku da ci gaba na maudu'in nan mai taken matan aure barka ramadan. Allah ya kawo kashi na uku kuma kashin ƙarshen wannan maudu'in da muke kawo muku girke-girke kala-kala wand amarya ko Uwargida za su samu su sabunta tukwanensu ga mai gida da sauran iyali saboda zuwan watan Ramadan mai albarka su ma su samu su samu ƙarin lada da rahamar Ubangiji Subhanahu wata'ala. Kamar yadda kuka sani…
Read More
Matan aure barka da Ramadan! (2)

Matan aure barka da Ramadan! (2)

Tare da AMNINA YUSUF ALI Assalamu alaikum, uwargida da kuma amarya. Ina yi muku sannu da ibada a wannan wata mai alfarma. Fatan Allah ya ba mu dacewa a cikinsa. Har yanzu dai muna kan maudu'in nan namu na sanar da girke-girke ga mata masu aure saboda shigowar watan Ramadan mai albarka domin su sauya wa Maigida samfurin tukunya domin samun ninkin ƙarin lada da watan Ramadan watan rahma da yafe zunubai da ɗaga darajar bayi tare da amsa dukkan buƙatu. Allah ya yi mana katari da dukkan romo da falaloli da suke a wannan wata. Kuma Allah ya nuna…
Read More
Mata ne jaruman watan Ramadan!

Mata ne jaruman watan Ramadan!

Tare da ABBA ABUBAKAR YAKUBU A wannan makon tunatarwar mu za ta mayar da hankali ne kan irin gudunmawar da iyayenmu mata, matanmu na aure, da ƙannenmu mata suke bayarwa a cikin wannan wata mai alfarma na Ramadan, wanda a cikinsa mabiya addinin Musulunci a ko'ina a duniya suke gudanar da azumi, da wasu ayyuka na ibada, don neman ƙarin kusanci ga Allah. Azumi, ɗaya ne daga cikin shika-shikan addinin Musulunci guda biyar wanda Allah Ya farlantawa kowanne mumini, mace ko namiji, don ya kiyaye su a matsayinsa na wanda ya karɓi addinin Musulunci a matsayin hanyar gudanar da rayuwarsa.…
Read More
Matan aure barka da Ramadan!

Matan aure barka da Ramadan!

Tare da AMINA YUSUF ALI Zuwa ga matan aure da suke bibiyar wannan shafinmu na Zamantakewa mai zuwar muku kowanne mako a jaridarku mai farin jini ta Blueprint Manhaja. A wannan mako shafin na matan aure ne. Duba da watan da muke ciki na Ramadan mai albarka. 'Yanuwana mata barkanmu da warhaka da fatan kuna cikin ƙoshin lafiya. Allah ya karɓi ibadunmu ameen. To a wannan mako mun kawo muku wasu dabaru ta hannun ƙanwata Sakina Yazid yadda uwargida da amarya za su kauce wa wahalar azumi, ko ma na ce za su rage wahalar azumi. A wannan yanayi da…
Read More
Saƙo zuwa ga iyayen gida

Saƙo zuwa ga iyayen gida

Daga FATIMA GARBA DANBORNO Saƙona zuwa ga mata shi ne, su rage dogon buri. Su gane auren mai kuɗi ba shi ba ne ƙarshen auren ba. Idan har suka ce sun dage sai mai kuɗi, ƙarshe sai kin ga an zo ana danasani. Su yi iya yinsu su dage da addu'a babu dare babu rana, akan Allah ya yi masu zaɓi da mafi alkhairi. Sau tari auren wani mai kudin ba alkhairi ba ne. Amma daga lokacin da mace ta kai goshinta ƙasa ta yi addua akan Allah ya yi mata zaɓi da miji na gari mai tsoron Allah, mai…
Read More
Kin iya kunu? (2)

Kin iya kunu? (2)

Tare da AMINA YUSUF ALI Masu karatu barkanmu da sake haɗuwa a wani sabon makon a shafinku mai albarka na zamantakewa mai zuwar muku kowanne mako a jaridarku mai farin jini ta Blueprint Manhaja. Da farko ina taya ku murnar shigowar watan azumi na Ramadan watan rahama watan yafiyar zunubai. Dafatan za mu dage da zikiri da ambaton Allah da istigifari don rabauta da wannan gwaggwavan lada. A makon da ya gabata mun fara bayani a kan sirrin madafi. Wato a game da tambayar mata sun iya kunu? Ba kunun kaɗai ba, kin san sirrin tukunya? A makon da ya…
Read More
Iyaye ku ja ‘ya’yanku masu nakasa a jiki don kwanciyar hankalinsu – Fatima Bello

Iyaye ku ja ‘ya’yanku masu nakasa a jiki don kwanciyar hankalinsu – Fatima Bello

"A dena ɗora wa aljannu alhakin matsalar nakasa" Daga ABUBAKAR M. TAHEER Fatima Bello matashiya ce da ta ke taimakon yara masu buƙatar ta musamman, inda ta buɗe gidauniyar tallafa musu mai suna Haske Children Foundation. A cikin wannan tattaunawa da wakilin Manhaja, Abubakar M Taheer ya yi da ita, ta nuna takaicin ta kan yadda al'umma suka ɗauki masu buƙata ta musamman a matsayin wani abu da ya shafi aljannu, dama wasu batutuwa da ya shafi taimakon masu buƙata ta musamman. A sha karatu lafiya. MANHAJA: DA farko za mu so ki gabatar mana da kanki ga masu karatunmu.…
Read More
Dandalin shawara: Na reni ‘ya’ya uku da mijina ya haifa a waje ba tare da sani na ba

Dandalin shawara: Na reni ‘ya’ya uku da mijina ya haifa a waje ba tare da sani na ba

(Ci gaba daga makon jiya) Daga AISHA ASAS TAMBAYA: Assalamu alaikum. Barka da safiya malama Aisha. Na san ba ki san ko wacce ce ni ba, sunana…………kuma na samu number ki ta hannun Hajiya…………ƙawata ce, lokacin da na ke mata bayanin halin da nake ciki ne, sai ta ce, ga number na kira ki, ke ce wadda ki ka zo har gida lokacin da matsalarta da……………..ta yi tsanani, ke ki ka taimaka har aka samu mafita. Malama Aisha, mijina ne can baya shekaru da yawa, shi da wani wan babanshi suka shigo da yamma, wan baban nasa ɗauke da jinjiri,…
Read More
Ba dalilin da zai sa ka ƙaro aure alhali gidanka bai ƙoshi ba – Nafisa Usman

Ba dalilin da zai sa ka ƙaro aure alhali gidanka bai ƙoshi ba – Nafisa Usman

"idan ba ki da haƙuri ba za ki iya samun kwangila a gwamnati ba" Daga AISHA ASAS Mace halitta ce da aka halita da wata baiwa ta musamman da ba kasafai ake samunta a maza ba, wato baiwar iya yin ababe da dama a lokaci guda. Ma’ana dai mace za ta iya aikin kula da kanta, iyalinta kuma ta samu iya neman kai ba tare da ɗaya ya samu rauni ba. Haka kuma mace za ta iya yin ayyuka da dama da ake ganin ƙarfin ƙwaƙwalwarta da ƙwazonta bai kai ba. A wannan makon shafin Gimbiya ya ɗauko maku matar…
Read More