Tattaunawa

Na samu rufin asiri a sana’ar rubuta finafinai – Yahaya S. Kaya

Na samu rufin asiri a sana’ar rubuta finafinai – Yahaya S. Kaya

Daga IBRAHIM HAMISU, a Kano Yahaya S. Kaya fasihin marubucin labarin fim ne, da ya rubuta finafinai fiye da 20 a masana'antar fim ta Kannywood. A tattaunawasa da Ibrahim Hamisu a Kano za ku ji cikakken tarihinsa da kuma irin nasarorin da ya samu cikin shekaru 8 da shigar sa Kannywood, ku biyo mu: MANHAJA: Ka gabatar mana da kanka? YAHAYA S. KAYA: Sunana Yahaya S Kaya. Ni marubuci ne, ina rubutun littafi, ina na film. Ko za ka ba mu taƙaitaccen tarihinka? An haife ni a Garin Zariya, a shekarar 1996, na ta so a garin Zariya, anan na…
Read More
Rashin haɗin kai ne ke hana tasirin marubutan Jihar Sakkwato – Zarah BB

Rashin haɗin kai ne ke hana tasirin marubutan Jihar Sakkwato – Zarah BB

"Rubutu madubi ne da ke haska gobe" Daga AISHA ASAS Jihar Sakkwato na ɗaya daga cikin jihohin da ke ɗauke da kwararrun marubuta duk da cewa ba kasafai ake sanin su ba, wataƙila hakan ba ya rasa nasaba da daidaitacciyar Hausa da suke amfani da ita, wadda ke hana a gane su da Hausa irin ta Sakwatawa, har sai dai idan su ne suka faɗa. A yau shafin adabi ya ɗauko ma ku ɗaya daga cikin jajirtattun marubuta da suka fito daga Birnin Shehu, Fatima Bello Bala, wacce aka fi sani da Zarah BB. Matashiyar marubuciya ce da ke bada…
Read More
Sarari ya ɗaukaka darajar MOPPAN zuwa ƙololuwa, inji Habibu Barde

Sarari ya ɗaukaka darajar MOPPAN zuwa ƙololuwa, inji Habibu Barde

“Muna son samar da tsarin shugabancin da zai saita masana'antar Kannywood” Daga MUKHTAR YAKUBU a Kano Alhaji Habibu Barde Muhammad shi ne sabon shugaban haɗaɗiyar ƙungiyar kwararru ta masu shirya fim ta ƙasa, wato MOPPAN, da ya kama mulki bayan saukar da tsohon shugaban Dakta Ahmad Muhammad Sarari ya yi a ƙarshen watan Janairun da ya gabata, wanda kafin hakan shi ne mataimaki na Arewa ta Tsakiya . Domin jin wanene Habibu Barde Muhammad da kuma irin gudunmawar da ya bayar a harkar fim, jaridar Blueprint Manhaja ta tattauna da shi, don haka sai ku biyo mu ku ji yadda ta…
Read More
Yadda muke ƙoƙarin sauya halayyar ’yan daba a Jos – Ƙungiyar ‘Jos Peace Vanguar’

Yadda muke ƙoƙarin sauya halayyar ’yan daba a Jos – Ƙungiyar ‘Jos Peace Vanguar’

Daga ABBA ABUBAKAR YAKUBU Garin Jos, babban birnin Jihar Filato na ɗaya daga cikin manyan biranen arewacin ƙasar nan da suke fama da matsalar taɓarɓarewar tsaro, da ya shafi yadda ƙungiyoyin matasa 'yan daba suke ɗaukar makamai suna shiga anguwanni suna sare-saren kan-mai-uwa-da-wabi da ƙwacen wayoyi. Yawaitar wannan masifa ce ta zaburar da mutane irin su MALAM NURA ALHASSAN da masu ra'ayi irin nasa suka tashi tsaye don ganin yaran da suke wannan aika-aika sun dawo kan hanya, da samar da tsaro a cikin al'umma. Wanne ƙalubale irin wannan aikin sa-kai ke fuskanta? Wacce nasara aka samu? Kuma wanne tallafi…
Read More
Rubutu ya sauya min rayuwata da duniyata – Ramlat Manga Maidambu

Rubutu ya sauya min rayuwata da duniyata – Ramlat Manga Maidambu

"Na sha wahalar rubuta littafina na farko" Daga ABBA ABUBAKAR YAKUBU Ramlat Abdulrahman Manga, wacce aka fi sani da Maidambu, na daga cikin jajirtattun marubuta onlayin da aka sha gwagwarmaya da su a duniyar marubuta, tun ba a san ko ita wacce ce ba. Ta yi rubuce rubuce da dama, waɗanda suka samu karvuwa a wajen jama'a har kuma ita ma ta yarda cewa ta samu alheri sosai. Tana daga cikin marubutan adabi da suka fito daga Jihar Bauci kuma take bai wa mara ɗa kunya wajen ɗaga sunan jihar a harkar batun rubuce-rubucen Hausa. A zantawarta da Abba Abubakar…
Read More
Mun canja rayuwar ’yan shaye-shaye fiye da ɗari – CAWI

Mun canja rayuwar ’yan shaye-shaye fiye da ɗari – CAWI

Daga ABBA ABUBAKAR YAKUBU A wani ɓangare na cigaba da ƙoƙarin ganin an dawo da hankalin matasa da hankalin su ke neman ɓacewa ta dalilin shaye-shayen miyagun ƙwayoyi da sinadarai masu bugarwa, wasu matasa a Jos babban birnin Jihar Filato sun yunƙuro domin wayar da kan sauran matasa 'yan uwansu da suka ɗauki hanyar shaye-shaye, da nufin canja musu tunani da salon rayuwa, ta yadda za su zama mutane nagari waɗanda al'umma za ta yi alfahari da su. Muhammad Lawal DeeDee Abubakar shi ne jagoran waɗannan matasa da suka kafa ƙungiyar 'Community Aid Workers Initiative' (CAWI) a ganawarsa da wakilin…
Read More
Nijeriya na buƙatar matashin Shugaban Ƙasa don kawo sauyi – Jikan Sanata

Nijeriya na buƙatar matashin Shugaban Ƙasa don kawo sauyi – Jikan Sanata

Daga AISHA ASAS Tsundumar matasa a harkokin siyasa abu ne mai matukar muhimmanci, domin matasa su ne kashin bayan kowace al'umma, don haka idan sun gyaru, to dukkan kasar ta gyaru. Wakiliyar Blueprint Manhaja, AISHA ASAS, ta samu damar tattaunawa da jajirtaccen matashin da ya jima yana fafutukar wayar da kan matasa kan hanyoyin da za su iya cin gajiyar kurciyarsu ta fuskar siyasa, sannan matashi ne da ya shiga harkar siyasa da kafar dama, kuma ya jima yana cin moriyar ta, tare kuma da janyo matasa ‘yan uwansa don su lashi zumar da ya samu ba tare da kyashi…
Read More
Shaye-shaye: Ya dace gwamnati ta tallafa wa ƙungiyoyi – Abdulrazaq Shehu

Shaye-shaye: Ya dace gwamnati ta tallafa wa ƙungiyoyi – Abdulrazaq Shehu

Daga AMINU AMANAWA a a Sakkwato Idan da akwai wata matsala da a yanzu ta fi damun iyaye da dama, musamman a jihohin Arewa bai wuce matsalar fatauci ko tu'ammali da miyagun ƙwayoyi ba musamman a tsakanin matasa da kuma mata. Malam Abdulrazak Shehu sanannen mai fafutikar yaqi da matsalar ne musamman a jihohin Sakkwato, Kebbi da kuma Zamfara, wanda ma har ya samar da qungiya sukutum domin yaƙi da matsalar wato "Center for Sensitization Against Drug Abuse" a turance.A zantawarsa da wakilinmu na Sakkwato Aminu Amanawa ya tattauna da Malam Abdulrazak Shehu wanda ya yi bayani sosai kan matsalar…
Read More
Na gaji fasahar rubutu daga mahaifiyata – Khairat U.P

Na gaji fasahar rubutu daga mahaifiyata – Khairat U.P

"Rubutu ba ruwansa da girman ka ko ƙanƙantarka" Daga ABBA ABUBAKAR YAKUBU Akwai masu ganin cewa ba a gadon basira ko wata baiwa ta ƙirƙira, domin kuwa wannan kyauta ce ta Allah. Amma fa duk da haka da akwai waɗanda za a iya cewa ƴan na gada ne da sun wuce ƴan na koya. Ummulkhairi Sani Panisau da aka fi sani da Khairat UP na daga cikin marubutan da suka taso cikin gidan rubutu, domin kuwa ƴa ce a wajen fitacciyar marubuciyar nan Sadiya Garba Yakasai, wacce ta rubuta littattafai fiye da 80, kuma har yanzu tana jan zarenta a…
Read More
Kuɗin namiji ba shi ne ya kamata mace ta yi tinƙaho da shi ba – Raihan Ƙamshi

Kuɗin namiji ba shi ne ya kamata mace ta yi tinƙaho da shi ba – Raihan Ƙamshi

"Idan har kasuwanci ka ke son yi sosai, sai ka soke bayar da bashi" DAGA MUKHTAR YAKUBU A yanzu dai za a iya cewa mata sun farka daga zaman rashin sana'a da a ke ganin an bar su a baya musamman a Ƙasar Hausa ta yadda a baya a ke yi wa matan yankin kallon koma baya a fagen kasuwanci da dana'a. Raihan Imam Ahmad wadda aka fi sani da Raihan Imam (Ƙamshi) ta na ɗaya daga cikin matasan mata da suke gudanar da harkokin kasuwancin su, kuma a yanzu ta kai matakin zama babbar 'yar kasuwa a vangaren kayayyakin…
Read More