Tattaunawa

Mun koya wa yara ‘yan makaranta sana’ar hannu- Hajiya Nafisa Halliru

Mun koya wa yara ‘yan makaranta sana’ar hannu- Hajiya Nafisa Halliru

"Iyaye sun yi farin ciki da muka koyar da 'ya'yansu sana'a a lokacin karatu" Daga UMAR AKILU MAJERE  A makon da ya gabata, mun ɗauko tattaunawa da jajirtacciyar mace da ya cancanta a kira da Gimbiya, sakamakon irin gwagwarmayar da take yi wurin ganin ta inganta harkar ilimi musamman ma a karkara, duk da cewa ba mazauniyar karkara ba ce, amma tana tafiyayya har zuwa ƙauyukan nesa, waɗanda da yawa ba su da hanyar da mota za ta iya bi. A cikin tattaunawar, mai karatu da ke bibiyar mu ya ji irin ƙalubalen da Hajiya Nafisa ta fuskanta ciki har…
Read More
Ƙungiyar Jos Peace Vanguard na faɗi-tashin sauya halayyar ’yan daba – Nura Alhassan

Ƙungiyar Jos Peace Vanguard na faɗi-tashin sauya halayyar ’yan daba – Nura Alhassan

Daga ABBA ABUBAKAR YAKUBU Garin Jos, babban birnin Jihar Filato na ɗaya daga cikin manyan biranen arewacin ƙasar nan da suke fama da matsalar taɓarɓarewar tsaro, da ya shafi yadda ƙungiyoyin matasa 'yan daba suke ɗaukar makamai suna shiga anguwanni suna sare-saren kan-mai-uwa-da-wabi da ƙwacen wayoyi. Yawaitar wannan masifa ce ta zaburar da mutane irin su MALAM NURA ALHASSAN da masu ra'ayi irin nasa suka tashi tsaye don ganin yaran da suke wannan aika-aika sun dawo kan hanya, da samar da tsaro a cikin al'umma. Wanne ƙalubale irin wannan aikin sa-kai ke fuskanta? Wacce nasara aka samu? Kuma wanne tallafi…
Read More
Babu adalci a mulkin da ake yi a Nijeriya – Dakta Bello

Babu adalci a mulkin da ake yi a Nijeriya – Dakta Bello

Daga BUSHIRA AMINU NAKURA  Dakta Ahmad S. Bello malami ne da yake koyarwa a Kwalejin Ilimi ta Tarayya da ke Zariya. A tattaunawarsa da Blueprint Manhaja a lokacin da yake bayyana irin halin ƙunci da tsadar rayuwa da rashin tabbacin rayuwa da talakan Nijeriya ke fuskanta, saboda taɓarɓarewar harkar tsaro da ilimi ya bayyana rashin mulki na adalci a matsayin silar taɓarɓarewar al’amura a ƙasar da kuma rashin sauraron al'umma da gwamnati ba ta yi balle ta ji damuwarsu. Ya ƙara da  cewa, idan ma ta ji ɗin, ba ta kulawa. saboda ra'ayinta da dukkan abin da ta ga dama…
Read More
Taɓarɓarewar tarbiyya da zumunci suna ba ni tsoro – Alƙali Nazir Abdullahi 

Taɓarɓarewar tarbiyya da zumunci suna ba ni tsoro – Alƙali Nazir Abdullahi 

"Alƙalanci na buƙatar isasshen lokaci, nazari da bincike" Daga BUSHIRA NAKURA  Alƙali Naziru Abdullahi Tamburawa ya bayyana baƙin ciki da takaicinsa bisa yadda tarbiyya da kuma zumunci a yau suka lalace har ta kai ga ba shi tsoro, saboda taraddadi da zulumun halin da al'umma za ta iya tsintar kanta a ciki, idan har aka ci gaba da tafiya a haka. Mai shari'a Naziru Tamburawa dai ya bayyana hakan ne a lokacin da yake tattaunawa da Wakikiyar Blueprint Manhaja, BUSHIRA NAKURA. Ga cikakkiyar hirar tasu kamar haka: MANHAJA: Mai karatu zai so jin cikakken sunanka, da inkiyarka da kuma taƙaitaccen…
Read More
Sakamakon kamuwa da kansa ya sa na kafa ƙungiyar wayar da kai kan sanƙarar mama – Halisa Muhammad 

Sakamakon kamuwa da kansa ya sa na kafa ƙungiyar wayar da kai kan sanƙarar mama – Halisa Muhammad 

Mu masu cutar sanƙarar mama muna buƙatar taimakon gaggawa DAGA MUKHTAR YAKUBU A  'yan kwanakin nan ne tsohuwar jaruma a Kannywood Halisa Muhammad ta kafa wata sabuwar ƙungiya ta wayar da kan mata a kan sanƙarar mama wadda a yanzu tuni ta yi nisa da wayar da kan mata tare da samar musu gudunmawa a kan yadda  masu larurar za su ci gaba da gudanar da rayuwarsu a cikin yanayin da suka samun kansu. Halisa Muhammad wadda a yanzu ma take kan shan magani tare da samun kulawar likita domin ceto rayuwarta daga larurar sanƙarar mama ta yi wa wakilinmu…
Read More
Ban taɓa nadamar zama malamin makaranta ba – Yunusa Anemosu

Ban taɓa nadamar zama malamin makaranta ba – Yunusa Anemosu

Kar ka bari alaƙar shashanci ta shiga tsakaninka da ɗalibanka matuƙar ka na son su ji tsoron ka Daga BUSHIRA NAKURA Yunusa Anemusu mai burin shiga aji domin bayar da ilimi ga ɗalibai, malami a Jami'ar Usman ɗanfodiyo da ke Sokoto, amma mazaunin Kano. A tattaunawarsa da wakiliyar Blueprint manhaja, ya bayyana mana burinsa anan gaba. Ga yadda hirar ta kasance; MANHAJA: Mai karatu zai ji daɗi idan ka faɗa mana cikakken sunanka da sunan da aka fi saninka da shi, da kuma tarihinka a taƙaice. YUNUSA: Assalamu alaikum. Sunana Yunusa Ibrahim Adamu, ana kirana da Anemosu. An haife ni a…
Read More
Ko gobe mutane za su karɓi taliya su yi zaɓe saboda yunwa – Bello Guiwa

Ko gobe mutane za su karɓi taliya su yi zaɓe saboda yunwa – Bello Guiwa

Daga AISHA ASAS Dakta M.B Abubakar, wanda aka fi sani da Bello Guiwa, ba ya buƙatar gabatarwa, musamman a Jahar Sakkwato da maƙwaftanta. Mutum ne da ya ga jiya da kuma yau a fannin siyasa da al’amurran yau da kullum. Jajirtaccen mutum da dubattan mutane suka jima suna cin moriyar sa ta fuskoki da dama, kuma ɗaya daga cikin mutanen da jama'a ke hasashen da za a same su a madafun iko zai kawo sauyi mai matuƙar tasiri ga talakan Jahar Sakkwato.  A  tattaunawarsa da jaridar Blueprint Manhaja, mai karatu zai samu muhimman batutuwa da suka shafi gwamnati da kuma…
Read More
Don ba wa al’adarmu gudunmuwa na ƙirƙiro sababbin abincin gargajiya – Sharif Atiku 

Don ba wa al’adarmu gudunmuwa na ƙirƙiro sababbin abincin gargajiya – Sharif Atiku 

Daga BUSHIRA NAKURA A daidai lokacin da matasa ke ƙyamatar al'adunsu, da barin duk wata ɗabi’a da za ta iya nuna su ɗin Hausawa ne, sakamakon kallon mai irin ɗabi’ar a matsayin wanda bai waye ba, an samu wani matashi da ke da kishin ƙasarsa ta Hausa, tare da burin haɓaka ta don tafiya da zamani.  A tattaunawar Blueprint Manhaja da Sharif Atiku, mai karatu zai fa'idantu matuƙa, musamman ma idan ya kasance mai so da sha'awar sanin al'adunmu na Hausa.  A sha karatu lafiya; MANHAJA: Assalamu alaikum warahamatullah wabarakatuhu. Mai karatu zai ji daɗi idan ka faɗa mana cikakken…
Read More
 Idan mace ba ta samu damar karatu ba to ta kama sana’a – Farfesa Sa’adatu Hassan Liman 

 Idan mace ba ta samu damar karatu ba to ta kama sana’a – Farfesa Sa’adatu Hassan Liman 

Ni ce mace ta farko da ta riƙe muƙamin shugabar jami’a a tarihin jami’ar Nasarawa Daga JOHN D. WADA, Lafia Farfesa Sa’adatu Hassan Liman ita ce sabuwar shugabar babbar jami’ar gwamnatin Jihar Nasarawa ta yanzu. ƙwararriya ce a fannin ilimin addinin Islamiya kuma mace tafarko da aka taɓa naɗa a muƙamin na shugabar babbar jami’ar jihar a tarihin jami’ar bakiɗaya. A tattaunawar nan ta musamman da wakilinmu a Jihar Nasarawa John D. Wada, ya yi da ita a ofishinta da ke jami’ar a garin Keffi ya gano cewa farfesar a yanzu haka tafi kowacce mace a jihar ta Nasarawa samun…
Read More
Cinikin da muke a rana yanzu da ƙyar yake samuwa a sati – Tijjani Bashir

Cinikin da muke a rana yanzu da ƙyar yake samuwa a sati – Tijjani Bashir

Daga BUSHIRA NAKURA TIJJANI ISAH BASHIR jajirtaccen matashin ɗan kasuwa ne mai neman na kansa a birnin Kano. A zantawarsa da Wakiliyar Blueprint Manhaja, Bushira Nakura, ya bayyana mana yadda al’amuran ciniki da kasuwanci suka sauya yanzu bayan rikicewar harkokin tattalin arzikin al’ummar Nijeriya. Ga yadda tattaunawar ta kasance: MANHAJA: Assalamu alaikum warahamatullah wabarakatuhu. Mai karatu zai ji daɗi idan ka faɗa mana cikakken sunanka da sunan da aka fi saninka da shi, sannan da tarihinka a taƙaice. TIJJANI: Amin waalaikumussalam warahamatullah wabarakatuhu. Sunana Tijjani Isah Bashir. Ana kira na da Tijjani. Na taso a Unguwar Garke Kwanar Dala. Na…
Read More