Tattaunawa

Ba abinda ke wahalar da baƙi a Turai kamar rashin iya turanci – Amina Ahmed Gumel

Ba abinda ke wahalar da baƙi a Turai kamar rashin iya turanci – Amina Ahmed Gumel

"Ilimin manya makami ne na gyara al'umma" Daga ABUBAKAR M. TAHIR Amina Ahmed Sani Gumel 'yar Nijeriya ce wanda ta ke zaune a Ƙasar England inda ta ke koyar da ilimin manya masu koyon yaren Turanci a matsayin yare na biyu. A cikin tattaunawarta da wakilin manhaja, ta kawo irin hanyoyin da suke bi wajen koyar da mutane baƙi yaren Turanci wanda zama ya kama su a Ƙasar England. Haka kuma ta kawo irin ƙalubalen da ta fuskanta wajen yaren Turanci dama irin nasarorin da ta samu a matsayin mai koyar da yaren Turanci a Ƙasar England. A sha karatu…
Read More
Na horar da masu ƙananan sana’o’i 4,000 fasahar kasuwancin yanar gizo – Maryam Bichi

Na horar da masu ƙananan sana’o’i 4,000 fasahar kasuwancin yanar gizo – Maryam Bichi

"Samun mata a cikin harkokin kasuwanci zai ƙara zaman lafiya da yalwatar arziƙi" Daga ABBA ABUBAKAR YAKUBU Harkar kasuwanci ta kafafen sadarwa na zamani ba sabon al'amari ba ne a ƙasar nan, musamman ma a wajen matasa waɗanda a lokacin su ne wannan cigaba yake daɗa samuwa. Sai dai ta yaya mutum zai samu ilimin yin wannan harka, da kuma kaucewa faɗawa hannun miyagu masu damfarar jama'a. Wakilin Blueprint Manhaja, Abba Abubakar Yakubu ya zanta da wata matashiya daga Jihar Kano, wacce ta yi fice a kan wannan irin kasuwanci na zamani da ta ce ta koyar da matasa da…
Read More
Na sha wahala a fim ɗin ‘Farida Nabil’ – Haruna Talle Maifata

Na sha wahala a fim ɗin ‘Farida Nabil’ – Haruna Talle Maifata

Daga IBRAHIM HAMISU Haruna Talle Maifata wani fitaccen jarumin ne da ya yi fice a masana'atar fim ta Kannywood, inda ya fi fitowa a matsayin ɗan daba ko mugu, a tattaunawarsa da Ibrahim Hamisu a Jos, za ku ji dalilan da ya sa ya ke fitowa a mugu da kuma irin nasarorin da ya samu a masana'atar. ku biyo mu: MANHAJA: Ko za ka gabatar mana da kanka ga masu karatunmu? HARUNA: Da farko dai ni sunana Haruna Talle maifata. Za mu so jin taƙaitaccen tarihinka? An haifeni a Jos ta Jihar Plateau, na yi karatun primary da secondary, sannan…
Read More
Iyaye su ba wa ‘ya’yansu damar zaɓar abinda suke son zama a rayuwa – Hauwa Mustapha Babura

Iyaye su ba wa ‘ya’yansu damar zaɓar abinda suke son zama a rayuwa – Hauwa Mustapha Babura

"Shelanta sakamakon jarrabawa na ɗaya daga cikin abinda ke sa ƙiyayyar karatu ga yara" (Ci gaba daga satin da ya gabata) Daga ABUBAKAR M. TAHIR MANHAJA: A ɓangare ɗaya, al'ummar ƙasarmu Nijeriya suna da sha'awar kwaikwayo tare da ɗaukar al'adun turawa. Shin kina ganin idan hakan ya ƙara yawaita zai taimaka wurin rage matsalolin da ake fama da su a ƙasar nan? HAJIYA HAUWA: To a gaskiya wanna wani abu ne wanda yana buƙatar al'ummar ƙasarmu musamman matasa su rinqa kulawa sosai da tsarin da zasu koya a rayuwar turawa. Sau dayawa suna zavar ɗabi'un da ya yi masu daɗi…
Read More
Karamcin marubuta ya sa duniyar rubutu ta zama dangi gare ni – Aisha Sani Abdullahi

Karamcin marubuta ya sa duniyar rubutu ta zama dangi gare ni – Aisha Sani Abdullahi

"Marubuta su tabbatar hijabinsu ba kawai na zahiri ba ne har zuciyarsu su rufe" Daga ABBA ABUBAKAR YAKUBU Ɗayyeesherthul-Humaerath, wani suna ne mai wuyar karantawa, amma kuma da shi aka fi sanin marubuciyar wacce matashiya ce daga Jos, da ta zama fitacciya a fagen rubuce rubucen adabi na yanar gizo. Asalin sunan ta Aisha Sani Abdullahi, ta yi rubuce rubuce da dama da suka shafi soyayya, zamantakewa, rayuwar zaman gidan miji da sauran su. Littattafanta Yel, Freeya, da suka zo da wani irin suna da salon da ba a saba da shi ba a tsakanin marubutan adabi sun ja hankali…
Read More
Mauludin Majma’u Niass na nuna ƙauna da haɗin kai ne – Shehi Tijjani Auwalu

Mauludin Majma’u Niass na nuna ƙauna da haɗin kai ne – Shehi Tijjani Auwalu

Mauludin bana, wanda ƙungiyar Majma’u Ahbab Sheikh Ibrahim Inyas ta shirya, shi ne mauludi karo na 37 wanda ya yi daidai da shekarun Sheikh Ibrahim Niass shekara 123. Gagarumin mauludi ne da ake shirya shi duk shekara don tunawa da Sheikh Ibrahim Niass da gabatar da wasu ayyuka na musamman da tunasarwa ga mabiya ɗariƙar Tijjaniya. A wannan shekarar, za a gabatar da mauludin ne ranar 18 ga Fabrairu, 2023, a Jihar Kebbi idan Allah ya yarda. Don jin taƙaitaccen tarihin wannan mauludin da ƙudirce-ƙudircen da aka tanada da muhimmancin mauludin a wurin al’umma musamman mabiya Ɗariƙar Tijjaniya da Faira,…
Read More
Da jarin Naira 50 na fara kasuwanci – Matashi Dini Majia

Da jarin Naira 50 na fara kasuwanci – Matashi Dini Majia

DAGA MUKHTAR YAKUBU a Kano A wannan lokacin da ake ganin matasa suna da son su samu rayuwa cikin sauqi ba tare da sun tashi sun nemi na kansu ba. Don haka da yawa sai matasan suka zama marassa aikin yi da kuma dogon buri na yin rayuwa mai tsada. Sai dai ba a taru an zama ɗaya ba, domin kuwa Dini Muhammad Majia yaro ne matashi da tun farkon rayuwar sa ya taso da zuciyar neman na kansa, wanda a yanzu yana cikin matasan 'yan kasuwa a cikin garin Kano, wanda kuma yake da kishin samar wa matasa hanyoyin kasuwanci…
Read More
Cikin sauƙi Atiku zai lashe zaɓen 2023, In ji Saraki

Cikin sauƙi Atiku zai lashe zaɓen 2023, In ji Saraki

Daga NASIRU S. GWANGWAZO, Anuja Wannan wata tattaunawa ce da gidan talabijin ɗin ARISE TV ya yi da tsohon Gwamnan Jihar Kwara kuma tsohon Shugaban Majalisar Dattawan Nijeriya, Dakta Abubakar Bukola Saraki, inda ya yi bayani mai tsawo kan irin cancantar tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa, Alhaji Atiku Abubakar, ga shugabancin Nijeriya fiye da sauran abokan takararsa a babban zave mai ƙaratowa na 2023. Blueprint Manhaja ta fassaro muku hirar, saboda irin muhimman batutuwan ƙasa da tsohon Shugaban Majalisar Dattawan ya tattauna a cikinta. Ga yadda tattaunawar tasu ta kasance: Shin ta waɗanne hanyoyi kake ganin ɗan takarar Shugaban Ƙasa na…
Read More
Tilas ce ta sa na fito takarar Gwamnan Sakkwato – Dakta Sifawa

Tilas ce ta sa na fito takarar Gwamnan Sakkwato – Dakta Sifawa

Daga AMINU AMANAWA a Sakkwato Yayin da manyan zaɓukan 2023 musamman ma zaɓen gwamnoni ke daɗa ƙaratowa, wani abu da ya soma ɗaukar sabon salo a siyasar Nijeriya shi ne, fitowar jama'a takarar gwamnoni a ƙananan jam'iyyun siyasa duk wasu na masu kallon 'yan amshin shata ne kawai ta la'akari da cewa, ba su fiye yin tasiri ba  a siyasar Nijeriya wajen kafa gwamnati. Wakilin Blueprint Manhaja a Sakkwato, Aminu Alhussaini Amanawa ya zanta da ɗan takarar gwamna na jami'ar ADP, Dakta Ibrahim Mahammad Liman Sifawa, wanda ya ce tilas ce ta sa shi fitowa takarar domin canza abinda ya…
Read More
Zargin badaƙalar kuɗi: Ya kamata hukumomi su yi bincike –Malagi

Zargin badaƙalar kuɗi: Ya kamata hukumomi su yi bincike –Malagi

Daga IBRAHIM MUHAMMAD HAMZA a Abuja Alhaji Idris Mohammed Malagi, ɗaya daga cikin masu magana da yawun ɗan takarar jam'iyyar APC, Alhaji Asiwaju Bola Ahmed Tinubu, ya gana da manema labarai a ciki har da Wakilin Blueprint Manhaja a ofishin kamfe ɗin Tinubu a Abuja dangane da tonon sililin da tsohon ma'aikacin Atiku Abubakar, ɗan takarar kujerar Shugaban Qasa na jam'iyyar PDP a 2023, Micheal Achimugu, ya yi na cewa, Atiku ya yi wasoson kuɗin jama'a lokacin da yake riƙe da muƙamin Mataimakin Shugaban Ƙasa daga 1999 zuwa 2007. Ga yadda tattaunawar ta kasance: BLUEPRINT MANHAJA: Mene dalilin ganawa da…
Read More