Editor

9204 Posts
Bikin Easter: Rabaran Dakuru ya shawarci ma’aurata su mutunta juna

Bikin Easter: Rabaran Dakuru ya shawarci ma’aurata su mutunta juna

Daga JOHN D. WADA, a Lafiya Babban Rabaran na Cocin ECWA na 1 dake Uke a jihar Nasarawa, Rabaran Dokta Joshua Bulus Dakuru, ya bayyana wasu munanan ɗabi'u dake yin sanadin mutuwar aure da rashin zaman lafiya a auratayya da sauran su inda ya shawarci ma'aurata baki ɗaya musamman kiristoci, su riƙa guje wa waɗannan ɗabi'un. Rabaran Dakuru ya bayyana haka ne a jawabin sa a lokacin wani taro na musamman don tunawa da mutuwa da kuma tashin Isa Almasihu daga matattu wadda aka gudanar a Cocin na ECWA na 1a Uke. Rabaran Dakuru ya ce, waɗannan munanan ɗabi'u dake…
Read More
Tinubu ya ba da umarnin saka ɗaliban NOUN a tsarin NYSC

Tinubu ya ba da umarnin saka ɗaliban NOUN a tsarin NYSC

Daga BASHIR ISAH Shugaban Ƙasa Bola Tinubu ya umarci Ma'aikatar Ilimi ta Ƙasa da ta saka ɗaliban da suka kammala karatu a Jami'ar National Open University (NOUN) a tsarin yi wa ƙasa hidima da aka fi sani da NYSC a taƙaice. Haka nan, Shugaban ya amince a lamunce wa ɗaliban da suka kammala NOUN halartar Makarantar Lauyoyi, wato Law School domin. Tinubu ya ɗauki wannan mataki ne domin samun daidaito wajen baiwa 'yan ƙasa damar cin gajiyar damammakin da ake da su a ƙasa. Shugaba Tinubu ya bayyana haka yayin da yake jawabi a wajen taron bikin yaye ɗalibai karo…
Read More
An buƙaci Tinubu ya ja kunnen EFCC kan yi wa doka karan-tsaye

An buƙaci Tinubu ya ja kunnen EFCC kan yi wa doka karan-tsaye

Daga BASHIR ISAH An yi kira ga Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu kan ya ja kunnen Hukumar Yaƙi da Rashawa ta Ƙasa (EFCC) bisa karan-tsayen da take yi wa doka wajen gudanar da harkokinta. An buƙaci Tinubu ya taka wa EFCCn burki ne bayan da ta yi yunƙuri cafke tsohon Gwamnan Jihar Kogi, Yahaya Bello, duk da cewa a baya umarnin kotu ta haramta mata hakan. Idan za a iya tunawa, a ranar 9 ga Fabrairu, 2024, Babbar Kotun da ke zamanta a Lokoja, ta yanke hukunci kan ƙara mai lamba HCL/68M/2024 tsakanin Alhaji Yahaya Bello da EFCC, inda ta…
Read More
Mu nemi aure a wajen surukai nagari

Mu nemi aure a wajen surukai nagari

Tare da ABBA ABUBAKAR YAKUBU A duk lokacin da wani batu ya tashi kan matsalar auratayya, wani Hadisi ne yake yawan faɗo min a rai. Mattanin Hadisin na cewa, Ma'aikin Allah Mai Tsira da Aminci ya cewa sahabbansa, 'Ku kiyayi ciyar da dabbobinku da ciyawar da ta fito a kan juji.' Sai sahabbai suka tambaye shi abin da yake nufi da haka, sai Manzon Allah (SAWW) ya qara da cewa, 'Ku guji aurar da ’ya’yanku ga dangin da basu da kyakkyawar shaida, masu munanan halaye.' Saqon da za mu ɗauka daga wannan Hadisi shi ne cewa, idan za mu yi…
Read More
Mun inganta tsarin shugabanci a Zamfara — Lawal

Mun inganta tsarin shugabanci a Zamfara — Lawal

Daga BASHIR ISAH Gwamna Dauda Lawal ya jaddada cewa gwamnatinsa ta inganta tsarin shugabancin Jihar Zamfara da zummar bunƙasa jihar yadda ya kamata. Lawal ya bayyana haka ne yayin taron majalisar zartarwar jihar wanda ya jagoranta ranar Litinin a Fadar Gwamnatin Jihar da ke Gusau, babban birnin jihar. Kakakin Gwmanan Zamfara, Sulaiman Bala Idris, ya bayyana a cikin sanarwar da ya fitar cewa, Gwamnan ya tunatar da mambobin majalisar ƙudurorin da gwamnatinsa ta sanya a gaba don cigaban jihar. Sanarwar ta ƙara da cewa, taron ya tattauna kan muhimman batutuwa bayan da Gwamnan ya gabatar jawabin maraba. Sanarwar ta rawaito…
Read More
Da Ɗumi-ɗuminsa: Kotu ta tabbatar da dakatarwar da aka yi wa Ganduje daga APC

Da Ɗumi-ɗuminsa: Kotu ta tabbatar da dakatarwar da aka yi wa Ganduje daga APC

Daga IBRAHIM HAMISU a Kano Babbar Kotun Jihar Kano mai Lamba 4 dake zaman ta a kan titin Mila, ta tabbatar da dakatarwar da wasu shugabannin Jam'iyyar APC a Mazaɓar Ganduje suka yi wa Shugaban Jam'iyyar na ƙasa, Abdullahi Umar Ganduje daga jam'iyyar. Alƙalin Kotun, Justice Usman Malam Na'abba ne ya tabbatar da hakan ta cikin wata takardar da masu ƙara suka nema, ba tare da sanar wa ɓangaren waɗanda suke ƙara ba wato (Motion Ex parte). Haladu Gwanjo da Laminu Sani ne suka shigar da ƙarar, inda suka yi ƙarar ɓangarori huɗu waɗanda suka haɗar da Jam'iyyar APC, Kwamitin…
Read More
Marubuta sun yi rawar gani cikin Ramadan – Queen Nasmah

Marubuta sun yi rawar gani cikin Ramadan – Queen Nasmah

Daga ABBA ABUBAKAR YAKUBU A cigaba da kawo muku tattaunawar da muka yi da marubuta da ƙungiyoyi game da ayyukan da suka gudanar cikin Ramadan, ƙarƙashin ƙungiyoyi da jagorori daban-daban. A wannan makon muna ɗauke ne da tattaunawar da wakilin Blueprint Manhaja Abba Abubakar Yakubu ya yi da wata marubuciya Asma'u Lawal Liman, wacce aka fi sani da Queen Nasmah, shugabar ƙungiyar Moonlight Writers Association. A zantawar da suka yi Nasmah ta bayyana irin shirye-shiryen da suka gabatar da kuma ayyukan da suke yi na jinqƙai da taimakawa mabuƙata, a lokacin azumi da bayansa. MANHAJA: Mu fara da sanin wacce…
Read More
Maza masu dukan mata

Maza masu dukan mata

Tare da AMINA YUSUF ALI Masu karatu barkan mu da sake haɗuwa a wani makon a filinmu mai albarka, Zamantakewa na jaridarku mai farin jini ta Blueprint Manhaja.  Fatan kun kammala azumi kuma kun yi sallah lafiya. Mun sani cewa mun tafi hutun maganar zamantakewa ta aure a wannan shafi, saboda zuwan watan Ramadan. Mun yi amfani da lokacin wajen kawo wa mata girke-girke waɗanda za su ƙara ƙawata musu aurensu. To alhamdulillah, mun kammala azumi kuma mun yi sallah lafiya, Allah ya sa karɓaɓɓu ne. Yanzu za mu ci gaba a kan maudu'in da muka saba kaso muku wato…
Read More
Majalisar Dokokin Kaduna ta kama hanyar binciken gwamnatin El-Rufai

Majalisar Dokokin Kaduna ta kama hanyar binciken gwamnatin El-Rufai

Daga BASHIR ISAH Majalisar Dokokin Jihar Kaduna ta kafa kwamiti na musamman domin binciken yadda gwamnatin Nasiru El-Rufai ta gudanar da hada-hadar kuɗi a wancan lokaci. Kwamitin zai binciki yadda tsohuwar gwamnatin ta ciyo bashi da bayar da kwangila da dai sauransu. Yayin wani taron jin ra'ayiyin jama'ar gari da aka shirya a ranar Asabar da ta gabata, an jiwo Gwamna Uba Sani na ƙorafi kan tarin basussukan da ya gada daga gwamnatin El-Rufai tun daga 29 ga Mayun 2023. Gwamnan ya ce abin da ya zo ya tarar bai taka kara ya karya ba don kuwa ko albashin ma'aikata…
Read More
Almundahana: Ana zargin Ganduje da karkatar da N51bn mallakar ƙananan hukumomi

Almundahana: Ana zargin Ganduje da karkatar da N51bn mallakar ƙananan hukumomi

Daga BASHIR ISAH Hukumar Yaƙi da Rashawa da Sauraren Ƙorafe-ƙorafe ta Jihar Kano, ta shigar da sabuwar ƙara kan tsohon Gwamnan Jihar Kano kuma Shugaban Jam'iyyar APC na Ƙasa, Abdullahi Ganduje, inda take zarginsa da karkatar da maƙuden kuɗi Naira Biliyan 51.3 mallakar ƙananan hukumomin jihar. Shugaban Hukumar, Muhuyi Magaji ne ya bayyana haka a cikin wani shirin da tashar Channels Television ta yi da shi a ranar Talata. A cewar Magaji, bincike ya gano wasu kuɗaɗe mallakar ƙananan hukumomi har biliyan N51.3 wanda aka karkatar da su zuwa asusun ajiyar wasu ɗaiɗaikun mutane ba a bisa ƙa'ida ba a…
Read More