Editor

9513 Posts
Tinubu ya buƙaci gwamnonin Arewa ta tsakiya su kasance tsinsiya baɗaurinki guda DAGA JOHN D. WADA, a Lafiya

Tinubu ya buƙaci gwamnonin Arewa ta tsakiya su kasance tsinsiya baɗaurinki guda DAGA JOHN D. WADA, a Lafiya

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya ƙalubalanci masu ruwa da tsaki da duka mambobin jam’iyyarsu ta APC maici a yankin Arewa ta tsakiya a ƙasar nan su tabbatar sun ci gaba da kasancewa tsintsiya maɗaurinki ɗaya. Wannan kiran haɗin kai Shugaban Ƙasar ya yi ne a lokacin wani gagarumin taron masu ruwa-da-tsakin jam’iyyar APC ɗin a Arewa ta tsakiya wanda aka gudanar a birnin Lafiya, fadar gwamnatin jihar Nasarawa. Shugaba Tinubu wanda Sakataren Gwamnatin Tarayya, Sanata George Akume ya wakilce shi a wajen taron, ya jaddada mahimmancin haɗin kai don cigaban jam’iyyar ta APC da ma ƙasa baki ɗaya. Ya…
Read More
Yadda za a samu maslaha tsakanin surukai

Yadda za a samu maslaha tsakanin surukai

Tare da AMINA YUSUF ALI Barkanmu da jimirin karatun jaridarku mai farin jini ta Manhaja. Za mu ci gaba daga inda muka tsaya a kan dalilan da suke kawo lalacewar alaƙa tsakanin surukai. Ta yadda surukuta a ƙasar Hausa ta zama kamar gaba a tsakaninsu. Kowa kishi da hassada yake wa ɗanuwansa. Ga rainin wayo, abin ba a magana. A wani lokaci a baya mun kawo wasu daga cikin dalilan da suka sa hakan take faruwa domin masu karatu su yi alƙalanci su gano wai shin ma laifin wanene? To a yanzu za mu ci gaba da kwararo muku bayani…
Read More
CJN ya sammaci manyan alƙalan kotunan Kano kan ba da umarni masu karo da juna

CJN ya sammaci manyan alƙalan kotunan Kano kan ba da umarni masu karo da juna

Babban Alƙalin Ƙasa (CJN), Justice Olukayode Ariwoola, sammaci Babban Alƙalin Kotun Tarayya da takwaransa na Babban Kotun Jihar Kano, kan su zo don ya ji yadda aka yi suka bayar da umarni masu cin karo da juna game da dambarwar sarautar Kano wanda hakan ya haifar da rashin tabbas. Babbar Kotun Tarayya a Jihar Kano ƙarƙashin jagorancin Alƙali S. A. Amobeda, ta ba da umarnin fitar da Muhammadu Sanusi II daga Fadar Ƙofar Kudu, tare da buƙatar a mai da Sarkin Kano na 15, Aminu Ado Bayero, kan kujerar Sarkin Kano. A hannu guda, ita ma Babbar Kotun Jihar Kano…
Read More
Tinubu ya rattaɓa hannu kan tsohon Taken Ƙasa ya zama doka

Tinubu ya rattaɓa hannu kan tsohon Taken Ƙasa ya zama doka

Shugaban Ƙasa Bola Tinubu ya sanya ya rattaɓa hannu kan Dokar Taken Ƙasa inda a yanzu za a koma amfani da tsohon taken ƙasa wanda Turawan mulkin mallaka suka samar. Tuni dai wannan al'amari ya haifar da ce-ce-ku-ce a tsakanin 'yan ƙasa. Shugaban Majalisar Dattawa, Godswill Akpabio ne ya sanar da hakan yayin zaman da Majalusar ta yi a ranar Laraba. Haka nan, Akoabio ya ce Shugaba Tinubu ba zai yi wa Majalisar jawabi ba illa iyaka ya ƙaddamar da sabon taken na Nijeriya. Kakakin Majalisar Wakilai, Tajudeen Abbas, ya ce Tinubu ya soke gabatar da jawabin ne kasancewar Ranar…
Read More
Gwamna Abba ya haramta zanga-zanga a faɗin Kano

Gwamna Abba ya haramta zanga-zanga a faɗin Kano

Daga IBRAHIM HAMISU a Kano Gwamnatin Jihar Kano ƙarƙashin jagorancin Injiniya Abba Kabir Yusif, ta haramta shirya kowane nau'in zanga-zanga a faɗin jihar. Gwamna Abba ya sanar da hakan ne ta cikin wata sanarwa da Kakakinsa, Sanusi Bature Dawakin Tofa ya fitar a safiyar Laraba. Ya ce, ɗaukar wannan matakin ya biyo bayan bayanan sirri da suka samu a kan cewa wasu maƙiya jihar sun shirya yin zanga-zangar nuna goyon baya ga Sarkin Kano na 15, Alhaji Aminu Ado Bayero. Hakazalika, Gwamnan ya umarci dukkan hukumomin tsaron jihar da su tabbatar da kama dukkan waɗanda suka samu sun gudanar da…
Read More
MƊD ta yi alƙawarin tallafa wa Nijeriya kan shirin samar da mafita a Arewa rewa maso-Gabas da aka ƙaddamar

MƊD ta yi alƙawarin tallafa wa Nijeriya kan shirin samar da mafita a Arewa rewa maso-Gabas da aka ƙaddamar

A wani gagarumin yunƙuri na magance matsalar gudun hijira a Jihohin Borno, Adamawa, da Yobe na Nijeriya, Gwamnatin Nijeriya da Majalisar Ɗinkin Duniya sun ƙaddamar da tsare-tsare na jihohi kan mafita mai ɗorewa don magance matsalar ‘yan gudun hijirar cikin gida. Mataimakin Sakatare Janar na Majalisar Ɗinkin Duniya kuma Mai Ba Da Shawara na Musamman Kan Hanyoyin Magance Rarrabuwar Kawuna a Cikin Gida Robert Piper, yayin taron kaddamar da taron a fadar shugaban ƙasa da ke Abuja, ya ce; “Za mu tsaya a bayanku. "Bari in nanata kudurinmu a madadin Majalisar Ɗinkin Duniya: Za mu ci gaba da ba da…
Read More
Sarakunan gargajiya da aka tsige a tarihin Nijeriya

Sarakunan gargajiya da aka tsige a tarihin Nijeriya

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Mutane da dama suna tunanin cewa rikicin masarautar Kano ne karon farko da aka fara tsige sarkin gargajiya a tarihin Nijeriya, amma hakan ba gaskiya ba ne domin kuwa an sha tsige sarakuna a tarihi, wanda ya sa jaridar Blueprint Manhaja ta ga ya dace ya kawo tarhin tsige sarakuna a Nijeriya. Ooni na Ife – Ogboru: Ogboru shi ne aarni na 19 Ooni na Ife wanda sarakunan fadar Ife suka tsige daga gadon sarauta bisa zalunci wanda aka gaji da mulkinsa na shekaru 70. An yaudare shi da dabara ya fito daga wurinsa ya zo…
Read More
Zargin cushen kasafi: Majalisa ta yi wa Sanata Abdul Ningi afuwa

Zargin cushen kasafi: Majalisa ta yi wa Sanata Abdul Ningi afuwa

Majalisar Dattawa ta yi wa Sanata Abdul Ahmed Ningi afuwa tare da kiran sa ya koma bakin aiki bayan da ta dakatar da shi a ranar 12 ga watan Maris, 2024. A ranar Talata Mataimakin Shugaban Masu Rinjaye a Majalisar, Sanata Abba Moro, ya gabatar da buƙata dawo da Ningi tare da yin dama a madadin Ningin kan abin da ya faru. Shugaban Majalisar Dattawa, Godswill Akpabio, shi ne ya ba da sanarwar dawo da Ningi bakin aiki bayan da wasu daga cikin sanatotcin suka ruƙi a yi masa afuwa. Afuwar na zuwa ne makonni biyu kafin ƙarewar wa'din dakatarwa…
Read More
Shekara ɗaya a kan mulki: Gwamna Lawal ya ƙaddamar da wasu manyan ayyuka a Bakura, Maradu

Shekara ɗaya a kan mulki: Gwamna Lawal ya ƙaddamar da wasu manyan ayyuka a Bakura, Maradu

Gwamna Dauda Lawal na Jihar Zamfara ya ƙaddamar da muhimman ayyukan cigaban al'umma a yankunan ƙananan hukumomin Bakura da Maradun da ke shiyyar Zamfara ta yamma. Wannan na zuwa ne a daidai lokacin da Lawal yake cika shekara ɗaya riƙe da ragamar mulkin jihar ta Zamfara. Kakakin Gwamna, Sulaiman Bala Idris, ya bayyana cewa, Gwamna Lawal ya kai ziyara ƙananan hukumomi guda uku da suka haɗa da: Mafara da Bakura da kuma Maradun. Ya ƙara da cewa, yayin ziyarar, Lawal ya nuna damuwa kan halin da ya tarar da Babban Asibitin Ƙaramar Hukumar Talatan Mafara saboda rashin ingnci. Sanarwar da…
Read More
Yadda ta ke wakana a wajen ɗaukar fim ɗin barkwanci na ‘Jikokin Mai Gari’

Yadda ta ke wakana a wajen ɗaukar fim ɗin barkwanci na ‘Jikokin Mai Gari’

Daga IBRAHIM HAMISU a Kano Kamfanin shirya finafinai na M. Soja Concept NIG. LTD yana cigaba da ɗaukar sabon fim ɗin barkwanci mai dogon zango mai suna 'Jikokin Mai Gari'. Fim ɗin wanda yanzu haka ake ɗaukarsa a guraren daban-daban a Jihar Kano, ana sa ran fitowarsa nan ba da daɗewa ba. Mujahid M. Soja wanda shi ne daraktan fim ɗin kuma shi ne ya ƙirƙiro labarin, ya bayyana cewa an gina labarin ne don nishaɗartarwa da faɗakarwa iri-iri. "Jikokin Mai Gari' fim ne da aka gina shi akan wasu yara biyu da suka kasance jikoki ga mai garin garin,…
Read More