Editor

9256 Posts
Bayan shekara 26, tsohon Gwamnan Imo, Emeka Ihedioha ya fice daga PDP

Bayan shekara 26, tsohon Gwamnan Imo, Emeka Ihedioha ya fice daga PDP

Daga BASHIR ISAH Bayan shafe shekara 26 a matsayin mabiyin jam'iyyar PDP, tsohon Gwamnan Jihar Imo, Emeka Ihedioha, ya sauya sheƙa daga jam'iyyar zuwa wata. Ihedioha ya ce ya fice daga jam'iyyar ta PDP ne bisa ra'ayinsa. A cewarsa, abin takaici ne ganin yadda PDP ta ɗare kan turbar da ta saɓa wa ra'ayinsa. Ya ce, "Duk da ƙoƙarin da na yi na bai wa jam'iyyar shawarwari, jam'iyyar ta kasa samar da sauye-sauyen cigaba a cikin gida, tabbata ra da kiyaye dokokinta, ko kuma zama 'yar hamayya mai ƙarfi ga jam'iyyar APC mai mulki. “Bisa wannan dalili ne na rage…
Read More
Maza masu dukan mata

Maza masu dukan mata

Tare da AMINA YUSUF ALI Masu karatu barkanmu da sake haɗuwa a wani makon a filinmu mai albarka, Zamantakewa na jaridarku mai farin jini ta Blueprint Manhaja. Yanzu za mu ci gaba a kan maudu'in da muka saba kawo muku wato nasiha kan zamantakewa, wato a wani maudu'inmu mai suna Maza masu dukan mata. Mun fara kawo muku wasu daga dalilan da suke jawo maza su yi duka, da muma dalilina na ganin bai kamata a ɗora musu laifi ba. Yanzu za mu ci gaba daga inda muka tsaya. A sha karatu lafiya. To dalilin na biyu da nake ganin…
Read More
Yaƙi da Ta’addanci: Akwai buƙatar samar da dakarun yanki don daƙile safarar makamai — Tinubu

Yaƙi da Ta’addanci: Akwai buƙatar samar da dakarun yanki don daƙile safarar makamai — Tinubu

Daga BASHIR ISAH Shugaban Ƙasa Bola Tinubu, ya jaddada kira kan samar da dakarun yanki masu zamn ko-ta-kwana a matsayin kayan aikin magance dukkan matsalolin tsaron da ake fuskanta a yanzu da ma waɗanda ka iya tasowa a gaba a yankin Afirka Kazalika, ya ce samar da dakarun zai taimaka ainun wajen daƙile safarar makamai a tsakanin ƙasashen Afirka. Tinubu ya bayyana haka ne sa'ilin da yake jawabi a wajen buɗe babban taron yaƙi da ta'addanci a Afirka wanda aka shirya ranar Litinin a Abuja. Shugaban ya ƙara da cewa, ya zama wajibi a kawo ƙarshen ta'addanci a yankin Afirka…
Read More
Gwamnatin Tinubu za ta haramta wa ɗalibai ‘yan ƙasa da shekara 18 neman gurbin karatu a manyan makarantu

Gwamnatin Tinubu za ta haramta wa ɗalibai ‘yan ƙasa da shekara 18 neman gurbin karatu a manyan makarantu

Daga BASHIR ISAH Gwamnatin Tarayya ƙarkashin jagorancin Shugaba Bola Ahmed Tinubu, ta ce tana shirin haramta wa ɗalibai 'yan ƙasa da shekara 18 nan gurbin karatu a jami'o'i da sauran manyan makarantu da ke faɗin Nijeriya. Ministan Ilimi Farfesa Tahir Mamman ne ya bayyana haka a lokacin da yake yi wa manema labarai ƙarin haske a lokacin da yake zagayen duba yadda jarrabawar UTME ta 2024 ke gudana a wasu cibiyoyin rubuta jarrabawar ranar Litinin a Abuja. Ministan ya bayyana rashin jin daɗinsa bisa ƙarancin shekarun wasu daga cikin ɗaliban da ya gani suna rubuta jarrabawar, yana mai cewa shekarunsa…
Read More
Gwamna Lawal ya jaddada buƙatar amfani da fasahar zamani wajen yaƙi da rashin tsaro

Gwamna Lawal ya jaddada buƙatar amfani da fasahar zamani wajen yaƙi da rashin tsaro

Daga NASHIR ISAH Gwamna Dauda Lawal na Jihar Zamfara ya jaddada buƙatar da ke akwai ta amfani da fasahar zamani wajen yaƙi da rashin tsaro a Jihar da ma yankin Arewa baki ɗaya. Lawal ya bayyana haka ne a wajen taron da shi da wasu takwarorinsa suka yi da Mataimakiyar Sakataren Majalisar Ɗinkin Duniya, Amina J. Mohammed, ranar Juma'a a Washington, D.C. Mahalarta taron sun haɗa da gwamnonin Zamfara da Benue da Jigawa da Kaduna da Katsina da Kebbi da kuma Neja, kamar yadda mai magana da yawun Gwamnan Zamfara, Sulaiman Bala Idris, ya bayyana cikin sanarwar da ya fitar…
Read More
Manyan ’yan siyasa sun kira ni sanadin maganata, inji Adam Zango

Manyan ’yan siyasa sun kira ni sanadin maganata, inji Adam Zango

Daga AISHA ASAS A satuka buyu da suka gabata, fitaccen jarumi a Masa’antar Kannywood, Adam A. Zango ya bayyana a kafar sada zumunta na TikTok da bayyanai da za mu iya kira da tura ta kai bango, duk da cewa wasu da yawa na kallon faifan bidiyon na Zango a matsayin ishara ga abinda zai iya faruwa da shi nan gaba idan ba a ɗauki mataki ba, wanda wannan tunanin ne ya sa hankullan masoyan jarumin suka ta shi, yayin da suka shiga aika masa da saƙon nuna soyayya da goyon baya gare shi. Jarumi Adam ya nuna takaicinsa ta…
Read More
Ina ‘ya’yanku suka je yawon sallah?

Ina ‘ya’yanku suka je yawon sallah?

Daga AISHA ASAS Masu karatu barkanmu da yau, barkanmu da ganin ƙarshen watan alfarma, kuma barkanmu da sallah. Allah Ya karɓi ibadunmu, Ya sa mun dace, Ya kuma maimaita mana. A satin farko na sallah aka samu wata 'yar muhawara game da yawon sallah da yaranmu ke yi musamman ma mata. Inda wani ya yi zancen tururuwar da yara maza da shekarunsu bai haura 17 zuwa 19 ke yi wurin siyan kwararon roba a lokacin abin tayar da hankali ne. Da wannan ne wasu suka yi wa wannan kalaman ca, inda suke ƙaryata shi tare da nisanta yaran da abinda…
Read More
‘Yan sandan Kenyan sun cika hannu da shugaban Binance da ya tsere daga Nijeriya

‘Yan sandan Kenyan sun cika hannu da shugaban Binance da ya tsere daga Nijeriya

Daga BASHIR ISAH 'Yan Yaƙi da Manyan Laifuka na Ƙasa da Kasa, sun damƙe shugaban kamfanin Binance, Nadeem Anjarwalla, a ƙasar Kenya. MANHAJA ta tattaro cewar, 'yan sandan na nan suna shirin miƙa Anjarwalla ga Gwamnatin Nijeriya bayan kammala ɓangarensu. Majiya ta kusa da gwamnati wadda ba ta amnince a ambaci sunanta ba, ita ce ta tabbatar da kama Anjarwalla ran Lahadi da daddare. Idan za a iya tunawa, MANHAJA ta rawaito Gwamnatin Tarayyar Nijeriya ta bayyana cewa ta gano inda tserarren shugaban Binance da ya tsere, Nadeem Anjarwalla ya ɓoye. Gwamnatin ta ce, ta gano Anjarwalla yana ƙasar Kenya…
Read More
Jigawa za ta yi wa yara miliyan ɗaya allurar riga-kafin shan inna

Jigawa za ta yi wa yara miliyan ɗaya allurar riga-kafin shan inna

Daga UMAR AKILU MAJERI a Dutse Gwamnatin Jihar Jigawa ta shirya tsab don yi wa ƙananan yara su miliyan ɗaya da rabi allurar rigakafin shan inna a matsayin ƙoƙarin da gwamnatin jihar ke yi na hana cutar ɓulla a jihar. Darakta a hukumar lafiya matakin farko, Dakta Shehu Sambo, shi ne ya sanar da hakan ga taron manema labarai jim kaɗan bayan ƙaddamar da shirin allurar na bana a fadar Sarkin Dutse, Alhaji Hamim Nuhu Muhammed Sunusi a ranar Litinin. Jami'in ya ce yara miliyan ɗaya da rabi ake sa sunasa ran za su amshi allurar a fadɗn Jihar. Ya…
Read More
Yadda bikin Hawan Daushe ya laƙume rayuka huɗu a Bauchi

Yadda bikin Hawan Daushe ya laƙume rayuka huɗu a Bauchi

Daga BAKURA MUHAMMAD a Bauchi Mutane huɗu ne cikinsu har da ɗan wani fitaccen hakimi aka kashe a wani taho-mugama da ya auku a tsakanin wani gungun abokan adawa biyu yayin da ake yin Hawan Daushe na ƙaramar Salla a garin Bauchi. Taho-mugamar ta kuma haifar da raunuka ga wasu jama'a mabiya tawagar mahaya dawaki dake cikin jerin gwano hawan na daushe, wadda mai Martaba Sarkin Bauchi, Dokta Rilwanu Suleiman Adamu yakan yi kashegarin sallah, walau Eid-el fitr ko Eid-el Kabir na kowace shekara. Gungun abokan adawar biyu sune da ta 'Yan-Babeli, wacce zaunanniya ce dake bayar da gudummawa kan…
Read More