Ra’ayi

Zuwa ga masu shirin aure (I)

Zuwa ga masu shirin aure (I)

A yau zan yi wasiƙa ne a kan zaɓin ma'aurata, domin shi ne babban abin da ke ci wa kowa tuwo a ƙwarya a halin yanzu. Wanda kuma hakan ke jawo yawan mace-macen aure, domin ana auren ne kawai barkatai ba tare da sanin wa ya kamata a aura ba. Babban hadafin da ya ke sanya mu zaɓar wanda zamu rayuwa da shi ko wacce zamu rayu da ita a matsayin rayuwar aure shi ne samun nutsuwar rayuwa, shi kuwa samun nutsuwar ruhi da abokiyar zama ba ya yiwuwa sai ta hanyar auratayya, domin idan zaman rayuwar tare ya kasance…
Read More
Malam Ibrahim Shekarau: Goga ka san hanya

Malam Ibrahim Shekarau: Goga ka san hanya

Daga BIKISU YUSUF ALI Me ya sa wasu ke ganin gogaggen ɗan siyasa ne ya dace da Majalisar Dattawa? Nazari ta fuskar Malam Ibrahim Shekarau Majalisar Dattawa ce babbar Majalisar Dokoki ta Nijeriya mai wakiltar mazabun sanatoci 109. Babbar aikinta ita ce kirƙirar dokoki, sa ido kan ayyukan gwamnati, wakiltar muradun al'umma da kuma tantance wasu muƙaman gwamnati kamar yadda Kundin Tsarin Mulkin Najeriya ya tanada. Saboda muhimmancin wannan majalisa, masu nazarin siyasa sukan yi la'akari da gogewa ta ilimi da tarihin shugabanci lokacin nazarin cancantar 'yan takara.Haka ana bukatar mai baki da kishi da iya magana cikin mutane da…
Read More
Rarara annoba ne ga Kano da Arewa?

Rarara annoba ne ga Kano da Arewa?

Daga ALI ABUBAKAR SADIQ A baya, ban taba bata lokaci don yin rubutu game da Rarara ba, amma a wannan lokaci ya zama wajibi ga duk mai kishin Arewa da Musulmi ya yi Allah wadai da irin halayya da wakokin Rarara. Komai kiyayyarka da Rarara dole ka sallama wajen yarda da cewa hakika Allah ya ba shi ni'ima ta basirar waka. Ita kuma waka, ko su mawaka, Allah ya sanar da mu cikin suratul Shu'ara cewa kashi biyu ne: Q22:226 "Kuma mawãƙa, halakakku ne ke bin su. Shin, ba ku ga cewa, lalle ne sũ, cikin kõwane rango sunã yin…
Read More
Nazari kan matsalolin noma a daminar bana

Nazari kan matsalolin noma a daminar bana

Daga ABBA ABUBAKAR YAKUBU  Wani rahoto da jaridar Manhaja Blueprint ta wallafa game da matsalolin da manoma ke fuskanta a daminar bana, dangane da ƙalubalen noma da tsadar abinci ya ja hankalina sosai, musamman ganin cewa jama'a da dama na sa ran ganin an samu sauƙin farashin kayan abinci a kasuwanni, saboda yanayin da ake ciki na damina, yayin da manoma a wasu sassan arewacin ƙasar nan suka fara fitar da kayan gona zuwa kasuwanni.  Rahoton ya naaalto Babban Sakataren ƙungiyar Manoma ta ƙasa (AFAN), Femi Oke, yana bayyana cewa, har kawo yanzu ana cigaba da samun hauhawar farashin kayayyakin…
Read More
Alhaji Abubakar Alhaji (1937–2026): Dan kishin ƙasa da ya yi wa Nijeriya hidima cikin natsuwa da ƙwarewa 

Alhaji Abubakar Alhaji (1937–2026): Dan kishin ƙasa da ya yi wa Nijeriya hidima cikin natsuwa da ƙwarewa 

A makon jiya, Nijeriya ta yi rashin ɗaya daga cikin fitattun jami'an gwamnati da suka yi wa ƙasa hidima cikin gaskiya da riƙon amana, wato Alhaji Abubakar Alhaji (Sardaunan Sakkwato). Rasuwar wannan dattijo ɗan kishin ƙasa, tsohon Ministan Kuɗi, kuma tsohon Jakaden Nijeriya a Birtaniya, bankwana ce da wani mutum wanda rayuwar sa ta kasance abar koyi ta ladabi, kishin ƙasa, tawali'u da sadaukar da kai wajen bautar ƙasa. Alhaji Abubakar Alhaji ya rasu bayan ya shafe makonni yana fama da rashin lafiya. Da farko an kwantar da shi a Asibitin Koyarwa na Jami'ar Usmanu ɗanfodiyo da ke Sakkwato, kafin…
Read More
Sautin Shehu ya taka inda ƙafarsa ba ta taka ba!

Sautin Shehu ya taka inda ƙafarsa ba ta taka ba!

Daga NASIRU ADAMU EL-HIKAYA Sautin Musulunci ya taimaki Shehu Mujaddadi ya kafa daula ba gidan rediyo, talaibijin ko soshiyal midiya ba. Shehu ba ya riƙe takobi ko mashi amma kullum hannunsa rike ya ke da alƙalami da tawada don yaɗa ilimi Idan mu ka duba rayuwar Shehu Mujaddadi daga 1754-1817 ba kafafe na sadarwa ko ɗaya balle a je ga maganar wayar tarho don sai bayan shekara kimanin 70 bayan rasuwar Shehu a shekarun 1880’s a ka ma fara aiki da sadarwar TELEGRAPH a Nijeriya da kan fidda saƙo na layi 100 a wasiƙance kuma har 1920 da ƙaddamar da…
Read More
Annobar karuwanci a ƙasar Hausa

Annobar karuwanci a ƙasar Hausa

Daga MUKHTAR YAKUBU  Kasuwanci ana nufin saye da sayarwa. Duk wani aikin da mutum zai yi amfani da basirar sa ko kuma abin da ya koya daga wajen wani ko a makaranta ya aiwatar da shi domin neman kuɗi, shi ake cewa wa sana'a a Hausance. Ma'ana duk wata sana'a ta hannu kamar dinki, saka, kitso,kanikanci, tuki da makamantan su, su ake kira sana'ar  hannu. Ita dai kalmar karuwanci, kalma ce da bahuashe ya aro ta daga wajen Babarbare, a kalmar da suke cewa Karuwa, ma'ana mai yawun iska ko kuma iska, inda shi kuma Malam Bahaushe ya mayar da…
Read More
Makarantun tsangaya (almajirci) gyara kaɗan suke buƙata ba haramta su ba

Makarantun tsangaya (almajirci) gyara kaɗan suke buƙata ba haramta su ba

Daga ABUBAKAR SANI (KWAMARED DAN BAHAUSHE) Karatun tsangaya wani irin karatu ne wanda ake yi a makaratun koyar da addinin musulunci a ƙasar Hausa shekaru da dama da suka wuce. Karatun ana yin sa ne ta hanyar yin rubutu a allo da kuma alƙalami. Ma fi yawan waɗanda suke yin wannan karatun su ne suke ciyar da kansu ta hanyar yin bara domin su samu abinci. Masu yin wannnan karatun yawancin su karatun alƙur'ani kaɗai suke yi babu ruwansu da karatun boko. Haka kuma ma fi yawancin su ba su cika yin sana'a ba sai dai bara, wanda ake kira…
Read More
Ayyukan raya ƙasa a Arewa: Tinubu na cika alƙawari

Ayyukan raya ƙasa a Arewa: Tinubu na cika alƙawari

A cikin shekaru uku da suka gabata, gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu ta ƙaddamar da manyan shirye-shiryen raya ƙasa da suka shafi sassa daban-daban na Nijeriya, musamman fannin tsaro, ababen more rayuwa, noma, ilimi da makamashi. Arewacin ƙasar na daga cikin yankunan da ake aiwatar da wasu daga cikin waɗannan ayyuka. A fannin tsaro, gwamnati ta amince da ƙirƙirar sabbin Rukunonin Sojoji (Divisions), tare da sake tsara yankunan aiki domin ƙarfafa yaƙi da ta'addanci, garkuwa da mutane da sauran miyagun laifuka. Haka kuma an amince da ƙarin kayan aiki da gina sabbin barikoki domin inganta ayyukan jami'an tsaro. A ɓangaren…
Read More
Zuwa gare ku ma’abota haƙuri

Zuwa gare ku ma’abota haƙuri

Assalamu alaikum wa rahmatullahi wa barakatuh. Zuwa gare ku, ya ma’abota haƙuri, ku da kuka zaɓi ku tsaya daram a kan gaskiya duk da tsanani, ku da kuka rungumi haƙuri a lokacin jarrabawa, ku da kuka yi imani cewa duk wani raɗaɗi da zubar hawaye ba zai tafi a banza ba a wajen Allah Maɗaukaki. Wannan wasiƙa an rubuta ta ne domin girmama ku, domin tunatar da ku darajar haƙuri a Musulunci, da kuma ƙarfafa zuciyarku da kalaman Alƙur’ani da hadisai, waɗanda suka nuna cewa haƙuri ita ce hanya zuwa ga nasara ta gaskiya. Haƙuri ba kawai jurewa ba ne.…
Read More