Ra’ayi

Hukunta ‘yan ta’adda 150 cikin kwanaki biyu ya nuna sauyin salo a yaƙi da matsalar tsaro

Hukunta ‘yan ta’adda 150 cikin kwanaki biyu ya nuna sauyin salo a yaƙi da matsalar tsaro

Samun nasarar hukunta mutum 150 da aka samu da laifukan ta'addanci cikin kwanaki biyu kacal ya zama wani babban ci gaba a tsarin shari'ar Nijeriya. Wannan mataki ya nuna cewa Gwamnatin Tarayya ta fara ɗaukar yaƙi da ta'addanci da muhimmanci, tare da ƙoƙarin tabbatar da cewa masu aikata irin waɗannan manyan laifuka sun fuskanci hukunci cikin gaggawa. Babban Lauyan Tarayya kuma Ministan Shari'a, Lateef Fagbemi, ya bayyana cewa a sabon zagayen shari'ar da aka gudanar a Abuja, an saurari shari'o'i kusan 160, inda aka samu hukuncin ɗaurin laifi ga kusan mutum 150. Ya kuma buƙaci al'umma su ci gaba da…
Read More
Tarihin Gobir da yadda Gobirawa suka riski ƙasar Hausa

Tarihin Gobir da yadda Gobirawa suka riski ƙasar Hausa

Masarautar Gobir na ɗaya daga cikin tsofaffin daulolin ƙasar Hausa, kuma tana daga cikin manyan masarautun da suka taka muhimmiyar rawa a tarihin Arewacin Nijeriya da yankin Sahel. A tarihin da aka fi sani, ƙasar Gobir ta yi iyaka da Agades daga arewa, Zamfara daga kudu, Mayali daga gabas, sannan daga yamma ta yi iyaka da Konni. Sai dai, akwai ra'ayoyi mabambanta kan asalin Gobirawa. Wasu masana da masu riƙe da tarihin gargajiya na cewa Gobirawa ba Hausawa ba ne a asali, suna kuma danganta asalinsu da Gabas ta Tsakiya, musamman ƙwasar Masar (Egypt). Haka kuma, akwai masu cewa wasu…
Read More
Fitilar bada hannu: Ma’ana, muhimmancinta da illar rashin amfani da ita

Fitilar bada hannu: Ma’ana, muhimmancinta da illar rashin amfani da ita

Tare da BILKISU YUSUF ALI Gabatarwa A zamanin yau, harkokin sufuri da zirga-zirgar ababen hawa sun zama wani muhimmin ɓangare na rayuwar ɗan adam, musamman a birane. Yawaitar motoci da  babura da masu tafiya a ƙafa ya haifar da buƙatar tsari mai kyau domin tabbatar da tsaro da ingantacciyar zirga-zirga. ɗaya daga cikin manyan hanyoyin da ake amfani da su wajen sarrafa zirga-zirga shine fitilar bada hannu, wato traffic light a turance. Fitilar bada hannu wata na’ura ce da ake sanyawa a hanyoyi domin sarrafa motsin ababen hawa da masu tafiya a kafa ta hanyar amfani da launuka uku: ja,…
Read More
Illar ta’addanci a cikin al’umma

Illar ta’addanci a cikin al’umma

Gwamnati ta fitar da jerin sunayen wasu mutane da ake zargi da hannu a ayyukan ta’addanci. Abin takaici, da yawa daga cikin sunayen da aka bayyana suna daga cikin sunayen da aka fi sani a Musulunci da kuma Arewacin Nijeriya. Muna addu’ar Allah Ya sa wannan ƙoƙari ya kasance na gaskiya wajen bankaɗo asirai da kuma hukunta duk wanda aka tabbatar yana da hannu a irin waɗannan munanan ayyuka. Babu abin da ke ƙara ta’azzara ta’addanci kamar rashin ɗaukar matakin shari’a da kuma gaza aiwatar da hukunci ga waɗanda aka samu da laifi. Haƙiƙa, ta’addanci ba ya tsaya ga hare-haren…
Read More
Amurka na tsaka mai wuya a yaƙin Iran

Amurka na tsaka mai wuya a yaƙin Iran

Daga ALI ABUBAKAR SADIQ Amurka ta fara yakin Iran da tsammanin za ta murkushe su cikin makonni biyu, ko matuka a makonni uku. Ta hanyar muggan hare haren bama bamai a kasar tare da kashe shugabannin Iran, wanda su ke tsammanin zai haifar da tarzomar Iraniyawa ga gwamnatin su wanda zai tilasta su mika wuya. Me ya sa tsarin na Amurka ya kasa wanzuwa cikin nasarar da su ka tsammata? Ku san kowannenmu idan zai tuna yarinyarsa a makaranta ko a unguwa, akasari mun san wani mai cin zali (bully) da ya yi sharafinsa. Shi mai cin zali za ka…
Read More
Canje-canjen da Tinubu zai kawo na canja fasalin aikin NYSC

Canje-canjen da Tinubu zai kawo na canja fasalin aikin NYSC

Daga MAHDI MUSA MUHAMMAD Majalisar Zartarwa ta Tarayyar Nijeriya (FEC), ƙarƙashin jagorancin Shugaban ƙasa, Bola Ahmed Tinubu ta amince da gudanar da garambawul ga tsarin Hukumar Kula da Matasa Masu Yi Wa ƙasa Hidima (NYSC). Ministan Harkokin Matasa, Ayodele Olawande, ne ya bayyana hakan yayin da yake ganawa da manema labarai a Fadar Shugaban ƙasa da ke Abuja ranar Litinin, 29 ga watan Yuni, 2026. Olawande ya bayyana cewa an amince da sake fasalin NYSC ne a taron Majalisar Zartarwa da aka gudanar a Fadar Shugaban ƙasa da ke Abuja ranar Litinin. A cewarsa, garambawul ɗin zai haɗa da cikakken…
Read More
Shirin Labarina da wasiƙar Zallawa!

Shirin Labarina da wasiƙar Zallawa!

Daga NASIRU ADAMU EL-HIKAYA Ga wanda bai san su waye Zallawa ba to a gurguje gungun mutane ne da ke da’awar kafa ƙungiyar zallar Hausawa. Ba wani ma’auni da ke tabbatar da mutanen Hausawa ku kuwa akasin hakan. Haƙiƙa babban abin da akasarin ‘yan wannan gungun su ka shahara a kai shi ne ayyana dukkan Fulani a matsayin ‘yan ta’adda, kushe jihadin Shehu Usmanu Danfodio da nuna jidali ne maimakon jihadi har ma da yayata cewa Sir Ahmadu Bello Sardauna shi ya ja wa kansa fushin su Chukwuma Nzeogwu da su ka yi ma sa kisan gilla. An sha jan…
Read More
Kalubalen jingine koyarwa a harshen gado a ƙananan makarantun Nijeriya 

Kalubalen jingine koyarwa a harshen gado a ƙananan makarantun Nijeriya 

Daga ABBA ABUBAKAR YAKUBU  Wata sanarwa da Ma'aikatar Ilimi ta Tarayya ta fitar dangane da batun jingine tsarin koyar da yaran makarantun firamare da ƙananan makarantun sakandire, cikin harshen uwa, wanda a baya yake ƙarƙashin Tsarin Ilimi na ƙasa, ta zo wa ’yan Nijeriya da dama a bazata. Ministan Ilimi, Dr. Tunji Alausa ne ya sanar da wannan babban saƙo da kansa a yayin da yake jawabi a wajen taron Majalisar Kula da Harkokin Koyarwa ta ƙasa wanda aka gudanar a birnin Akure na Jihar Ondo. Ministan ya yi bayyanin cewa za a koma amfani da harshen Turanci a matsayin…
Read More
A duba kiran Sarkin Kano kan buƙatar sasancin ECOWAS da ƙasashen Sahel

A duba kiran Sarkin Kano kan buƙatar sasancin ECOWAS da ƙasashen Sahel

Kiran da Mai Martaba Sarkin Kano, Dakta Muhammadu Sanusi II, ya yi ga Ƙungiyar Tarayyar ƙasashen Afrika ta Yamma (ECOWAS) da ta sasanta da ƙasashen Nijar, Burkina Faso da Mali abin dubawar shugabannin yankin ne. Kira ne da aka yi da hikima da hangen nesa a daidai lokacin da yankin Afrika ta Yamma yake fuskantar manyan ƙalubalen tsaro, tattalin arziki da siyasa waɗanda ba a taɓa ganin irin su ba. Maimakon a bar saɓanin ra'ayi ya rikiɗe zuwa rarrabuwar kai ta dindindin, ya kamata ƙungiyar ECOWAS ta yi amfani da kowace dama wajen dawo da aminci da sake gina haɗin…
Read More
’Yan Nijeriya akwai ƙura fa

’Yan Nijeriya akwai ƙura fa

Daga ALI ABUBAKAR SADIQ Makonnin da suka gabata na yi wani rubutu mai taken "Manakisar Amurka Ga Arewa". Abubuwa biyu ne suka faru a wancan lokaci. Na farko shine sanarwar tsagaita wuta tsakanin Amurka da Iran. Na biyu kuma shine bayanin ƙasar Amurka na umarci ma'aikatan jakadanci da ’yan ƙasarta su bar Nijeriya da kuma nesantar jihohin Arewa. Kamar yadda na bayyana a wancan rubutu cewa, tunda Iran ta gagari Amurka, inda ta kasa cimma muradunta da kuma datse mashigin Hormuz da Iran ta yi wanda ya janyo tashin gwauron zabi na farashin mai a duniya, yanzu Nijeriya ce a…
Read More