10
Jul
Samun nasarar hukunta mutum 150 da aka samu da laifukan ta'addanci cikin kwanaki biyu kacal ya zama wani babban ci gaba a tsarin shari'ar Nijeriya. Wannan mataki ya nuna cewa Gwamnatin Tarayya ta fara ɗaukar yaƙi da ta'addanci da muhimmanci, tare da ƙoƙarin tabbatar da cewa masu aikata irin waɗannan manyan laifuka sun fuskanci hukunci cikin gaggawa. Babban Lauyan Tarayya kuma Ministan Shari'a, Lateef Fagbemi, ya bayyana cewa a sabon zagayen shari'ar da aka gudanar a Abuja, an saurari shari'o'i kusan 160, inda aka samu hukuncin ɗaurin laifi ga kusan mutum 150. Ya kuma buƙaci al'umma su ci gaba da…
