Ra’ayi

Zuwa ga masu shirin aure (III)

Zuwa ga masu shirin aure (III)

Assalamu alaikum. Abu na uku da na ke son nuni da shi, shi ne muhimmancin sassauci da yafe wa juna, duk da cewa sassauci ba abu ne da ke da kyau a dukkan lokuta ba na rayuwa ba, to amma mafi kyawun sassauci da yafuwa akan yi shi ne a rayuwa ta aure. Don kuwa, a matsayinku na sabbin amare da angwaye, za su ci daba da fahimtar junanku da kuma ɗabi'un juna kusan kullum. To lalle kada irin waɗannan sabbin abubuwa su kashe muku gwiwa, don kuwa babu wani mutum a duniyan nan (a halin yanzu) da ya cika…
Read More
Yadda ’yan siyasa ke jefa matasa bangar soshiyal midiya

Yadda ’yan siyasa ke jefa matasa bangar soshiyal midiya

Daga ABBA ABUBAKAR YAKUBU Ana ci gaba da samun sauye-sauye a harkokin siyasa a ƙasar nan, yayin da ake ƙara kusantar Babban Zaɓe na shekarar 2027. 'Yan siyasa, musamman sabbin yanka masu neman a san da su da gwamnoni masu neman tazarce suna ta ƙoƙarin sauyin sheƙa daga wannan jam’iyya zuwa waccan. Mun ga yadda jihohi irin su Kano, Filato, Adamawa, Taraba da Zamfara gwamnoninsu suka yi sauyin jam'iyya zuwa babbar jam’iyya mai mulki ta APC. Matakin da wasu ke kallo a matsayin wayon a ci ne, wato kowa ƙoƙari yake yi a dama da shi a siyasar tarayya, a…
Read More
Nijeriya na buƙatar haɗin kan addinai fiye da kowane lokaci

Nijeriya na buƙatar haɗin kan addinai fiye da kowane lokaci

Matsalolin tsaro da Nijeriya ke fama da su sun kai wani matsayi mai matuƙar tayar da hankali, yayin da illolinsu ke yaɗuwa a sassa daban-daban na ƙasar. Saboda haka, bai kamata ƙasar ta ci gaba da barin bambance-bambancen addini, ƙabila da siyasa su zama abin da ke raba kan al’umma ko ke gurgunta haɗin gwiwar da ake buƙata wajen tunkarar matsalar tsaro ba. A saboda haka ne kiran da Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Mohammed Idris, ya yi na neman ’yan Nijeriya su haɗa kai wajen yaƙi da rashin tsaro ya dace da a mara masa baya sosai.…
Read More
Ranar Hausa yaudara ce!

Ranar Hausa yaudara ce!

Daga NASIRU ADAMU EL-HIKAYA Bikin Ranar Hausa ba shi da asali ko kaɗan kuma waɗanda ke kanbama yin sa ba Hausawa ba ne. Mutane masu sa ka hula hana sallah wai su ne za su yi taron raya al’adun Hausawa! Wannan biki da wasu matasa su ka kirkira ba tare da tuntuɓar dattawa da sauran manyan malaman jami’a ba musamman ABU, BUK da UDUS na nuna yadda tarbiyya ta taɓarɓare a tsakanin matasa da ke yin abun da su ka ga dama don sun ga yadda Dan Daudu ma zai yi ta yin shakiyancinsa amma ba a damu ba, in…
Read More
Ya kamata a yaba wa tawagar tattalin arzikin Tinubu

Ya kamata a yaba wa tawagar tattalin arzikin Tinubu

Gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu ta samu wasu nasarori a fannin tattalin arziki da suka cancanci a yaba mata, musamman yadda wasu daga cikin sauye-sauyen da ta ɓullo da su suka fara bayyana a kasuwannin hada-hadar hannayen jari, harkokin musayar kuɗaɗen waje da kuma fitar da kayayyakin da ba na man fetur ba. Kwanan nan Shugaba Tinubu ya yaba wa tawagar da ke kula da harkokin tattalin arzikin gwamnatinsa bisa hangen nesa, jajircewa da kuma ƙoƙarin da suke yi. Tawagar ta ƙunshi Ministan Kuɗi kuma Mai Kula da Daidaita Tattalin Arziki, Taiwo Oyedele; Ministan Kasafi da Tsare-tsaren ƙasa, Atiku Bagudu;…
Read More
Zuwa ga masu shirin aure (I)

Zuwa ga masu shirin aure (I)

A yau zan yi wasiƙa ne a kan zaɓin ma'aurata, domin shi ne babban abin da ke ci wa kowa tuwo a ƙwarya a halin yanzu. Wanda kuma hakan ke jawo yawan mace-macen aure, domin ana auren ne kawai barkatai ba tare da sanin wa ya kamata a aura ba. Babban hadafin da ya ke sanya mu zaɓar wanda zamu rayuwa da shi ko wacce zamu rayu da ita a matsayin rayuwar aure shi ne samun nutsuwar rayuwa, shi kuwa samun nutsuwar ruhi da abokiyar zama ba ya yiwuwa sai ta hanyar auratayya, domin idan zaman rayuwar tare ya kasance…
Read More
Malam Ibrahim Shekarau: Goga ka san hanya

Malam Ibrahim Shekarau: Goga ka san hanya

Daga BIKISU YUSUF ALI Me ya sa wasu ke ganin gogaggen ɗan siyasa ne ya dace da Majalisar Dattawa? Nazari ta fuskar Malam Ibrahim Shekarau Majalisar Dattawa ce babbar Majalisar Dokoki ta Nijeriya mai wakiltar mazabun sanatoci 109. Babbar aikinta ita ce kirƙirar dokoki, sa ido kan ayyukan gwamnati, wakiltar muradun al'umma da kuma tantance wasu muƙaman gwamnati kamar yadda Kundin Tsarin Mulkin Najeriya ya tanada. Saboda muhimmancin wannan majalisa, masu nazarin siyasa sukan yi la'akari da gogewa ta ilimi da tarihin shugabanci lokacin nazarin cancantar 'yan takara.Haka ana bukatar mai baki da kishi da iya magana cikin mutane da…
Read More
Rarara annoba ne ga Kano da Arewa?

Rarara annoba ne ga Kano da Arewa?

Daga ALI ABUBAKAR SADIQ A baya, ban taba bata lokaci don yin rubutu game da Rarara ba, amma a wannan lokaci ya zama wajibi ga duk mai kishin Arewa da Musulmi ya yi Allah wadai da irin halayya da wakokin Rarara. Komai kiyayyarka da Rarara dole ka sallama wajen yarda da cewa hakika Allah ya ba shi ni'ima ta basirar waka. Ita kuma waka, ko su mawaka, Allah ya sanar da mu cikin suratul Shu'ara cewa kashi biyu ne: Q22:226 "Kuma mawãƙa, halakakku ne ke bin su. Shin, ba ku ga cewa, lalle ne sũ, cikin kõwane rango sunã yin…
Read More
Nazari kan matsalolin noma a daminar bana

Nazari kan matsalolin noma a daminar bana

Daga ABBA ABUBAKAR YAKUBU  Wani rahoto da jaridar Manhaja Blueprint ta wallafa game da matsalolin da manoma ke fuskanta a daminar bana, dangane da ƙalubalen noma da tsadar abinci ya ja hankalina sosai, musamman ganin cewa jama'a da dama na sa ran ganin an samu sauƙin farashin kayan abinci a kasuwanni, saboda yanayin da ake ciki na damina, yayin da manoma a wasu sassan arewacin ƙasar nan suka fara fitar da kayan gona zuwa kasuwanni.  Rahoton ya naaalto Babban Sakataren ƙungiyar Manoma ta ƙasa (AFAN), Femi Oke, yana bayyana cewa, har kawo yanzu ana cigaba da samun hauhawar farashin kayayyakin…
Read More
Alhaji Abubakar Alhaji (1937–2026): Dan kishin ƙasa da ya yi wa Nijeriya hidima cikin natsuwa da ƙwarewa 

Alhaji Abubakar Alhaji (1937–2026): Dan kishin ƙasa da ya yi wa Nijeriya hidima cikin natsuwa da ƙwarewa 

A makon jiya, Nijeriya ta yi rashin ɗaya daga cikin fitattun jami'an gwamnati da suka yi wa ƙasa hidima cikin gaskiya da riƙon amana, wato Alhaji Abubakar Alhaji (Sardaunan Sakkwato). Rasuwar wannan dattijo ɗan kishin ƙasa, tsohon Ministan Kuɗi, kuma tsohon Jakaden Nijeriya a Birtaniya, bankwana ce da wani mutum wanda rayuwar sa ta kasance abar koyi ta ladabi, kishin ƙasa, tawali'u da sadaukar da kai wajen bautar ƙasa. Alhaji Abubakar Alhaji ya rasu bayan ya shafe makonni yana fama da rashin lafiya. Da farko an kwantar da shi a Asibitin Koyarwa na Jami'ar Usmanu ɗanfodiyo da ke Sakkwato, kafin…
Read More