Ra’ayi

Ya kamata gwamnonin Arewa su ɗauki matakai na bunƙasa yankin

Ya kamata gwamnonin Arewa su ɗauki matakai na bunƙasa yankin

Daga JABIRU HASSAN Duk da irin ƙoƙarin da gwamnonin arewacin ƙasar nan ke yi, akwai buƙatar su ƙara himma wajen ɓullo da shirye-shirye waɗanda za su bunƙasa yankin ta fannoni daban-daban. Yanzu lokaci ya yi da gwamnoninmu za su zamo masu ƙoƙarin kafa managarcin ginshiƙin farfaɗo da yankunansu bisa la'akari da buƙatun kowane ɓangare kamar yadda muke gani a ƙasashen da suka ci gaba. A yankinmu na arewacin ƙasar nan, akwai mabambantan buƙatu da ke kowane sashe da kuma kowane ɓangare waɗanda idan aka sami nasarar aiwatar da su za a kasance cikin yanayi na zaman lafiya da kwanciyar hankali. Akwai abubuwa da…
Read More
Hanyoyin magance faɗan daba da matsalar ‘yan Sara-Suka a Jos

Hanyoyin magance faɗan daba da matsalar ‘yan Sara-Suka a Jos

Daga HASSAN IMRAN  Ranar ƙarshe ta watan Maris da ya gabata wacce ta yi daidai da ranar da al'ummar Musulmi suka gudanar da murnar bikin ƙaramar Sallah, bayan kammala azumin watan Ramadan. Wani abin takaici da ban haushi ya faru a garin Jos, musamman a unguwannin cikin gari inda Hausawa suka fi rinjaye. Wasu matasa 'yan daba waɗanda aka fi sanin su da ’yan Sara-Suka suka ɗauki makamai irinsu wuƙaƙe suke yaƙar junansu. ’Yan dabar unguwar A suna yaƙar ’yan dabar unguwar B. Abin ya yi muni ta yadda har ta kai ga wani a cikinsu bai isa ya shiga…
Read More
Buɗaɗɗiyar wasiƙa zuwa ga rundunar ‘yan sandan Nijeriya

Buɗaɗɗiyar wasiƙa zuwa ga rundunar ‘yan sandan Nijeriya

Cikin girmamawa da kuma nuna kishin ƙasa, da son a kawo gyara ga hukumar tsaro ta jami'an 'yan sanda nake rubuta wannan wasiƙa. Aikin samar da tsaro al'amari ne mai matuƙar muhimmanci a kowacce aasa, kuma musamman ma aikin ɗan sanda. ɗan sanda shi ne jami'in tsaro na farko da ke da alhakin ganin al'umma sun zauna lafiya, cikin kariya da mutuntawar samun kyakkyawar kulawa ga fararen hula. Shi yasa aikin jami'in ɗan sanda ya ta'alaƙa a kan kare rayuka da dukiyar al'umma. Yana da kyau hukumar 'yan sanda ta nuna wa jama'a tausayawa da kuma mutuntawa, saɓanin yadda a…
Read More
Rikicin Filato: Mu guji tunzura juna da mummunan zargi

Rikicin Filato: Mu guji tunzura juna da mummunan zargi

Daga ABBA ABUBAKAR YAKUBU Sunan Jihar Filato ya sake shiga bakin duniya, musamman bisa lura da irin rahotannin da kafafen watsa labarai daban-daban ke yaɗawa a ciki da wajen ƙasar nan. Wasu rahotanni masu tsoratarwa da ɗaga hankali, ko dai saboda irin munanan hotunan da ake bugawa na gawarwaki da ƙonannun gine-gine, ko kuma irin zafafan kalamai na tsana da nuna ƙiyayya da ake rawaitowa daga mutanen da abin ya shafa, marasa daɗin ji. Ko kuma masu ƙarfafa gwiwa da ke bayyana hanyoyin da za a iya kawo ƙarshen hare-hare da kashe-kashe da ke faruwa a jihar.  A makon da…
Read More
Magance matsalar rashin tsaro a Filato da sauran jihohi

Magance matsalar rashin tsaro a Filato da sauran jihohi

Al'ummar Nijeriya sun shiga wannan mako ne da batun wasu hare-hare da wasu mahara suka kai, inda suka kashe mutum 52 da tarwatsa wasu 2,000 a Jihar Filato. Babu masaniya game da dalilan kai hare-haren a ƙauyuka shida na ƙaramar Hukumar Bokkos, waɗanda su ne mafi muni tun bayan rikicin da ya ɓarke a yankin a watan Disamban 2023, lokacin da aka kashe sama da mutum 100. Harin na baya-bayan nan ya fito fili ne a cikin ƙarshen mako, lokacin da aka kai mutanen da suka jikkata asibiti, kuma tuni shugaban Nijeriya, Bola Tinubu ya bayar da umarnin gudanar da…
Read More
Zubar da jini a Gaza ya dawo sabo

Zubar da jini a Gaza ya dawo sabo

Duk yanda na so kau da ido kan yanda sabon yaƙin da Isra'ila ta ƙaddamar kan Gaza sai na ga ba zai yiwu ba don yadda sojojin ke fakewa da kai hari kan 'yan Hamas amma haƙiƙa jama'a da ba ta yi wa kowa laifi ba harin ke shafa. Mutane na cikin gidajen su sai a jefa mu su bom su mutu. Akwai ma gidan da yara ke wasa a ka harba mu su makami mai linzami shikenan sai gawar su a ka samu. Bayan wasu hare-haren ma sai an tona ƙasa ko ruguzazzun konkere kafin a samo gawar mutane.…
Read More
Dr Idris Dutsen Tanshi ya bi sahu 

Dr Idris Dutsen Tanshi ya bi sahu 

Daga ALI ABUBAKAR SADIQ Kamar yadda ya rayu cikin ‘controɓersy’ sakamakon yadda ya fahimci addini, haka mutuwarsa ta zama da ‘controɓersy’ tsakanin masu ganinsa a kan daidai da waɗanda su ke ganin wabinsa. Duk wani ɗan adam, musamman wanda ya shahara a wani fage na rayuwa, kamar yadda ya ke da masoya da maƙiya haka idan ya mutu za ka ga wannan soyayya ko ƙiyayya ta dada bayyana, hatta annabawa. A cikin al'adu da addinai na ɗan adam, kama daga Kiristanci, ’yan Buddha, ’yan Hindu, Musulmi kai hatta masu addinai na gargajiya za ka samu su na da wata doka…
Read More
To me ya yi zafi ne? Kowa ya tsaya a fahimtarsa mana

To me ya yi zafi ne? Kowa ya tsaya a fahimtarsa mana

Daga ALI ABUBAKAR SADIQ  Akasarin lokatai, fushi sai ya sa mu manta da cikakkiyar koyarwar Manzo (SAW) da Qur’ani. kuma ba mu da shiryarwa da ta wuce su. Idan muka tuna da labarin Ka'ab Bn Zuhayr (Ibn Kathir ya kawo labarinsa), wato wani mashahurin mawaƙin ƙuraishawa kuma ɗan gado, wanda ya yi ta sakin baituka na cin mutuncin Manzo (SAW). Wasu sahabbai su ka yi ta farautar sa. A ƙarshe ya yi ‘disguise’ (ɓadda-bami) ya je fadar Manzo (SAW) ya nemi gafara kai tsaye ga Annabi (SAW). Bayan bayyana kansa, su Sayyadina Umar (RA) suka zare takobi za su kashe…
Read More
Shin taron sauyin yanayi na COP27 zai shafi duniya?

Shin taron sauyin yanayi na COP27 zai shafi duniya?

Assalam alaikum. Nan gaba kaɗan ne cikin watannan shugabannin ƙasashen duniya za su taru domin tattauna matakan kare ɗumamar yanayi a taron Majalisar ɗinkin Duniya kan sauyin yanayi da za a gudanar a ƙasar Masar. Shekara guda bayan da duniya ta fuskanci bala'o'in da ke da alaƙa da sauyin yanayi da ƙaruwar zafin da ba a taɓa gani ba a tarihin duniya. Majalisar ɗinkin Duniya na gudanar da taruka kan sauyin yanayi a kowacce shekara, domin bai wa gwamnatocin duniya damar ɗaukar matakan da suka dace domin rage ƙaruwar ɗumamar yanayi. Ana yi wa tarukan laƙabi da COPs, wadda a…
Read More
Mu taimaka wa jami’an tsaro gano maɓoyar ’yan ta’adda

Mu taimaka wa jami’an tsaro gano maɓoyar ’yan ta’adda

Haɗin gwiwar jami'an ’yan sanda da jama'ar gari ko farar hula wajen inganta aikin samar da tsaro a cikin al'umma ya fara ne tun a shekarar 2004 sakamakon yadda aikata laifuka ya yi tsamari a tsakanin al'umma tun a wancan lokacin. Don haka aka ƙirƙiro da rundunar ’yan banga, waɗanda suke zaɓaɓɓun mutane ne daga cikin al'umma da suka amince su ba da lokacin su da rayuwarsu, don samar da kariya a cikin al'ummarsu. Ba wai don sun zama 'yan sanda ba, amma saboda kusancin su da jama'a, za su iya riga jami'an tsaro saurin samun bayanai da gano maɓoyar…
Read More