Ra’ayi

Sautin Shehu ya taka inda ƙafarsa ba ta taka ba!

Sautin Shehu ya taka inda ƙafarsa ba ta taka ba!

Daga NASIRU ADAMU EL-HIKAYA Sautin Musulunci ya taimaki Shehu Mujaddadi ya kafa daula ba gidan rediyo, talaibijin ko soshiyal midiya ba. Shehu ba ya riƙe takobi ko mashi amma kullum hannunsa rike ya ke da alƙalami da tawada don yaɗa ilimi Idan mu ka duba rayuwar Shehu Mujaddadi daga 1754-1817 ba kafafe na sadarwa ko ɗaya balle a je ga maganar wayar tarho don sai bayan shekara kimanin 70 bayan rasuwar Shehu a shekarun 1880’s a ka ma fara aiki da sadarwar TELEGRAPH a Nijeriya da kan fidda saƙo na layi 100 a wasiƙance kuma har 1920 da ƙaddamar da…
Read More
Annobar karuwanci a ƙasar Hausa

Annobar karuwanci a ƙasar Hausa

Daga MUKHTAR YAKUBU  Kasuwanci ana nufin saye da sayarwa. Duk wani aikin da mutum zai yi amfani da basirar sa ko kuma abin da ya koya daga wajen wani ko a makaranta ya aiwatar da shi domin neman kuɗi, shi ake cewa wa sana'a a Hausance. Ma'ana duk wata sana'a ta hannu kamar dinki, saka, kitso,kanikanci, tuki da makamantan su, su ake kira sana'ar  hannu. Ita dai kalmar karuwanci, kalma ce da bahuashe ya aro ta daga wajen Babarbare, a kalmar da suke cewa Karuwa, ma'ana mai yawun iska ko kuma iska, inda shi kuma Malam Bahaushe ya mayar da…
Read More
Makarantun tsangaya (almajirci) gyara kaɗan suke buƙata ba haramta su ba

Makarantun tsangaya (almajirci) gyara kaɗan suke buƙata ba haramta su ba

Daga ABUBAKAR SANI (KWAMARED DAN BAHAUSHE) Karatun tsangaya wani irin karatu ne wanda ake yi a makaratun koyar da addinin musulunci a ƙasar Hausa shekaru da dama da suka wuce. Karatun ana yin sa ne ta hanyar yin rubutu a allo da kuma alƙalami. Ma fi yawan waɗanda suke yin wannan karatun su ne suke ciyar da kansu ta hanyar yin bara domin su samu abinci. Masu yin wannnan karatun yawancin su karatun alƙur'ani kaɗai suke yi babu ruwansu da karatun boko. Haka kuma ma fi yawancin su ba su cika yin sana'a ba sai dai bara, wanda ake kira…
Read More
Ayyukan raya ƙasa a Arewa: Tinubu na cika alƙawari

Ayyukan raya ƙasa a Arewa: Tinubu na cika alƙawari

A cikin shekaru uku da suka gabata, gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu ta ƙaddamar da manyan shirye-shiryen raya ƙasa da suka shafi sassa daban-daban na Nijeriya, musamman fannin tsaro, ababen more rayuwa, noma, ilimi da makamashi. Arewacin ƙasar na daga cikin yankunan da ake aiwatar da wasu daga cikin waɗannan ayyuka. A fannin tsaro, gwamnati ta amince da ƙirƙirar sabbin Rukunonin Sojoji (Divisions), tare da sake tsara yankunan aiki domin ƙarfafa yaƙi da ta'addanci, garkuwa da mutane da sauran miyagun laifuka. Haka kuma an amince da ƙarin kayan aiki da gina sabbin barikoki domin inganta ayyukan jami'an tsaro. A ɓangaren…
Read More
Zuwa gare ku ma’abota haƙuri

Zuwa gare ku ma’abota haƙuri

Assalamu alaikum wa rahmatullahi wa barakatuh. Zuwa gare ku, ya ma’abota haƙuri, ku da kuka zaɓi ku tsaya daram a kan gaskiya duk da tsanani, ku da kuka rungumi haƙuri a lokacin jarrabawa, ku da kuka yi imani cewa duk wani raɗaɗi da zubar hawaye ba zai tafi a banza ba a wajen Allah Maɗaukaki. Wannan wasiƙa an rubuta ta ne domin girmama ku, domin tunatar da ku darajar haƙuri a Musulunci, da kuma ƙarfafa zuciyarku da kalaman Alƙur’ani da hadisai, waɗanda suka nuna cewa haƙuri ita ce hanya zuwa ga nasara ta gaskiya. Haƙuri ba kawai jurewa ba ne.…
Read More
Kalubalen samar da ’yan sandan jihohi ga tsaro 

Kalubalen samar da ’yan sandan jihohi ga tsaro 

Daga ABBA ABUBAKAR YAKUBU A yayin da nake wannan rubutu Majalisar Dattawa ta kammala aiki akan ƙudirin dokar da za ta bayar da damar kafa rundunar ‘yan sandan jihohi bayan an yi wa ƙudirin dokar karatu na uku, lamarin da ya kawo ƙarshen muhawarar da aka ɗibi tsawon shekaru ana gudanarwa akan tsarin ‘yan sandan jihohi, domin warware matsalolin taɓarɓarewar tsaro a Nijeriya. Rahotanni sun tabbatar da cewa, an cimma nasarar hakan ne bayan dogon nazari da kuma amincewa da ƙudirin a dokance daga biyu bisa uku na majalisar. Haka kuma, an amince da ƙudirin a zaman majalisar ne bayan…
Read More
Lokaci ya yi da za a tsabtace rundunar ’yan sandan Nijeriya gaba ɗaya

Lokaci ya yi da za a tsabtace rundunar ’yan sandan Nijeriya gaba ɗaya

A duk ƙasashen da suka ci gaba, babu wata hukuma da ta fi muhimmanci wajen tabbatar da zaman lafiya, kare rayuka da dukiyoyi da kuma tabbatar da bin doka kamar rundunar 'yan sanda. Ita ce fuskar gwamnati da talaka ya fi haɗuwa da ita a rayuwarsa ta yau da kullum. Saboda haka, ingancin aikin rundunar 'yan sanda na da tasiri kai tsaye kan yadda jama'a ke kallon gwamnati da kuma tsarin adalci. A Nijeriya kuwa, duk da irin ƙoƙarin da gwamnati da shugabannin rundunar ke yi wajen sake fasalin aikin 'yan sanda, har yanzu akwai wasu ɓata-garin jami'ai da ke…
Read More
Shawara ga Alhaji Aliko Dangote

Shawara ga Alhaji Aliko Dangote

Ina amfani da wannan dama wajen isar da wata ƙaramar shawara ga mai girma shugaban Rukunin Kamfanonin Dangote, Alhaji Aliko Dangote. Na ji cewa kamfanin ya fito da wata tsari da ke ƙarfafa jama'a su kai rahoton duk direban motar kamfanin da ya karya dokokin hanya, tare da alƙawarin ba da tukuicin har naira dubu d Dari biyar (N500,000) ga wanda ya bayar da sahihin bayani. Wannan tsari abin yabawa ne, domin zai taimaka wajen rage haɗurra da kuma tabbatar da cewa direbobin kamfanin suna bin ƙa'idojin tuƙi. Sai dai ina da wata ƙaramar shawara: ya kamata a yi taka-tsantsan…
Read More
Me yake kawo rashin zuwan yara makaranta a Arewa?

Me yake kawo rashin zuwan yara makaranta a Arewa?

Daga ABBA ABUBAKAR YAKUBU A cikin wannan mako mai ƙarewa na samu damar halartar wani taron masu ruwa da tsaki kan harkokin ilimi, domin tattauna yadda za a ƙarfafa gwiwar iyayen yara, da samar da sabbin dabaru kan yadda za a daina cire yara daga makaranta zuwa aikin gona, ko aikin haƙar ma'adinai da neman kuɗi. Hukumar Kula da Ilimin ƙananan Makarantu ta SUBEB a Jihar Filato tare da haɗin gwiwar UBEC da ke ƙarƙashin gwamnatin tarayya, da Kwamitin Kula da Harkokin Makarantu na SBMC ne suka gudanar da wannan taro, wanda ya tattauna kan muhimman batutuwa da suka shafi…
Read More
Ayyukan Tinubu: Gani ya kori ji

Ayyukan Tinubu: Gani ya kori ji

Kaddamar da shirin Gani Ya Kori Ji da aka yi a makon jiya wata muhimmiyar hanya ce ta inganta ɗaya daga cikin raunin da aka daɗe ana gani a tsarin yadda ake gudanar da mulki a Nijeriya—wato sadarwa da jama'a. Ana auna gwamnati ba kawai da yawan ayyukan da ta aiwatar ba, har ma da yadda take iya isar da bayanan waɗannan nasarori ga al'umma. A wannan fanni, shirin da Mataimaki na Musamman ga Shugaban ƙasa kan Harkokin Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Abdulaziz Abdulaziz, ya ƙaddamar ya cancanci yabo. Manufar shirin na Gani Ya Kori Ji mai…
Read More