Ra’ayi

Asalin Masarautar Pindiga

Asalin Masarautar Pindiga

Daga MAHDI MUSA MUHAMMAD Pindiga, ita ce helikwatar mulkin masarautar Pindiga, wacce kuma ɗaya ce daga cikin masarautun Jihar Gombe. Wannan gari mai daɗaɗɗen tarihi, Jukunawa suka kafa shi a tsakankanin ƙarni na goma sha shida zuwa ƙarni na goma sha bakwai. Garin ya fara daga ɗan ƙaramin matsugunni na wasu jama’a a kan dutse har zuwa bunƙasarsa kamar yadda yake a yau a matsayin masarautar sarkin yanka mai daraja ta biyu a cikin Jihar Gombe. Asali: Pindiga, gari ne mai tsohon tarihi, asalin kafuwar wannan gari yana farawa daga lokacin da Jukunawa suka shigo yankunan baƙaƙe daga ƙasar Yamen,…
Read More
Shugabannin Nijeriya suna tunanin akwai hisabi kuwa?

Shugabannin Nijeriya suna tunanin akwai hisabi kuwa?

Daga ABDULLAHI JIBRIL DANKANTOMA LARABI Yau kwana uku babu wutar lantarki a Kano. Na yi amanna babu wani shugaba da zai kwana uku a gidansa ko ofis ɗinsa ba tare da wutar lantarki ba kuma ya ci gaba da rayuwa ‘normal’ irin yadda talaka ke rayuwa babu wuta. Shin malamai ba ku ba su labarin irin mulkin adalci da sahabbai suka yi ne? Sayyadina Umar (RA) ba ya iya barci face sai ya tabbatar da talakawan da yake mulki sun ci abinci sun ƙoshi kuma sun tabbatar da sun aminta da irin adalcin da ya ke yi musu. Na taɓa karanta…
Read More
Inganta zaɓen ƙananan hukumoni da ƙirƙiro hukumar zaɓen baiɗaya ne mafita 

Inganta zaɓen ƙananan hukumoni da ƙirƙiro hukumar zaɓen baiɗaya ne mafita 

Daga SANI DAN AUDI Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta ƙasa (INEC) ita ce hukumar zaɓen Nijeriya da ta ke da alhakin gudanar da zaɓukan tarayya.  A ɗaya ɓangaren kuma, hukumomin zaɓe masu zaman kansu ta jihohi (SIEC) ce ke da alhakin gudanar da zaɓukan jihohi da ƙananan hukumomi. Yayin da INEC ta samu gagarumin ci gaba wajen inganta sahihancin tsarin zaɓe, SIEC na fuskantar suka kan rashin nuna son kai da ’yancin kai. Babban hasashe shi ne cewa, Hukumar INEC ta fi cin gashin kanta da rashin son kai idan aka kwatanta da hukumomin zaɓe na jihohi (SIECs). Wannan hasashe…
Read More
Muhimmancin taimako

Muhimmancin taimako

Assalamu alaikum! Godiya ga Allah Maɗaukakin sarki, da ya sake ba ni damar aika wasiƙa na zuwa ga al’umma, ta wannna jarida(Manhaja) albarka. A matsayinmu na mutane masu hankali, abu ne da ya kamata kowa ya gane cewa, duk wani ɗan Adam, komai muƙaminsa, komai ƙarfin arzikinsa, komai ƙarfin jikinsa, yana buƙatar taimako. Idan ba ya buƙatar tallafin dukiya, to yana buƙatar wani, idan bai buƙatar wani tallafin, to ala tilas ɗinsa, yana da wata buƙatar daga ɗan uwansa mutum. Kamar yadda al’amarin yake, Allah Ya halicci ɗan Adam ne a matsayin mai kasawa, wanda dole ne ya zama yana…
Read More
Babu alamar kasafin kuɗin 2025 zai taimaki talaka

Babu alamar kasafin kuɗin 2025 zai taimaki talaka

Assalamu alaikum, Blueprint Manhaja. Haƙiƙa mun yi farin ciki da sake ba mu dama wurin bayyana abubuwan da suke mana kaikayi a rai tare da isar da saƙon da muke son isarwa ga shugabanni da sauran al’ummar ƙasa. Muna muku addu’ar Allah ya ƙara muku hikima da basirar aiki da kuma bunƙasar wannan jarida mai farin jini baki ɗaya. Abin kunya ne kwarai da gaske a irin halin da wannan ƙasa tamu da ma al’umma musamman ma’aikata ke rayuwa cikin ƙunci a ce shugaba Tinubu ya ware wasu kuɗaɗe domin amfanin kansa da kansa, wanda kuɗin abincinsa kaɗai na rana…
Read More
Masu dukan mata ku tuba ku daina

Masu dukan mata ku tuba ku daina

Daga ABBA ABUBAKAR YAKUBU Kwanaki wata marubuciya ta yi wani rubutu a shafinta na Facebook, inda ta bayyana takaicinta game da halayyar wasu azzaluman maza da ke cin zarafin matansu ta hanyar duka, abin da ya jawo muhawara mai zafi daga ɓangarori daban-daban, sakamakon yadda wannan mummunar halayya ke ci musu tuwo a ƙwarya. Mata da dama, musamman masu aure, suna kokawa da yadda wasu mazan ke kasa daurewa fushi da ɓacin ransu, da zarar matansu sun musu wani kuskure ko laifi sai su hau jibgarsu kamar jakuna, ba mutane ba. Wani lokaci ma idan abin ya zo da tsautsayi…
Read More
Shin mayaƙan Sham tsagera ne?

Shin mayaƙan Sham tsagera ne?

Daga NASIRU ADAMU EL-HIKAYA Ko da kuwa wani zai kira mayaƙan Hayat Tahrir Al-Sham da su ka amshi madafun ikon ƙasar Sham wato Siriya a matsayin tsagera a halin yanzu dai gwamnati na hannun su. Na ga aƙalla ɗaya daga manyan kafafen labaru a gabar ta tsakiya na zayyana su da zama tsagera wanda hakan ya sa a ke ɗari-ɗari  da su a matsayin shugabannin wannan ƙasa mai tarihi. Ba mamaki kamar yadda a kan zayyana gwamnatocin mulkin soja a wasu ƙasashen Afurka da masu mulkin kama-karya ko da ba su karya ƙasashen ba, hakan ya zama suna ga mayaka…
Read More
Zuwa ga masu cin zarafin ’ya’yan riƙo

Zuwa ga masu cin zarafin ’ya’yan riƙo

Assalam Alaikum. Ina miƙa saƙon gaisuwa da ban bajiya ga dukka ma'aikatan jaridar Blueprint Manhaja, Allah Ya albarkaci wannan jarida, Amin. Wata babbar matsala na tasowa da ta shafi yadda wasu mutane ke ɗaukar 'ya'yan da ba nasu ba na cikinsu, a wulakance, musamman ma dai 'ya'yan riƙo da suke ɗauko su daga ƙauye ko gidajen 'yan uwa, don su taimaka musu, ko kuma marayu ne da iyayen su suka rasu. Akwai kuma batun yaran aiki da ake ɗauko su daga ƙauye ko daga gaban iyayen su, don su yi aiki a gidajen masu kuɗi ko ma'aikata, don su taya…
Read More
Me ya sa ‘yan siyasa ke mantawa da mata idan sun samu gwamnati?

Me ya sa ‘yan siyasa ke mantawa da mata idan sun samu gwamnati?

Mata a Nijeriya sun koka da yadda ake mantawa da su bayan ’yan siyasa sun samu gwamnati duk da fitowar da suke ƙwansu da ƙwarƙwata wajen kaɗa ƙuri’a a yayin zaɓe. Wannan koke na matan na zuwa ne a daidai lokacin da ake daf da gudanar da zaɓukan ƙasar na 2023. Wannan matsala ta rashin damawa da mata a siyasa abu ne da ya daɗe yana ciwa wasu mata tuwo a ƙwarya ganin yadda suka ce ana watsi da su a lokacin da siyasa ta yi daɗi. Matan na cewa wataƙila hakan baya rasa nasaba da rashin ba su cikakkiyar…
Read More
An yi bukukuwan Kirsimeti da na Sabuwar Shekara cikin lumana

An yi bukukuwan Kirsimeti da na Sabuwar Shekara cikin lumana

Daga ABBA ABUBAKAR YAKUBU Zan fara da taya mu murna da shiga sabuwar shekarar 2025. Da fatan Ubangiji zai sada mu da dukkan alkhairan da ke cikinta, Ya kuma tsare mu daga dukkan sharrukan da ke cikinta. Allah Ya sa mu shiga wannan shekara da ƙafar dama, kamar yadda Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya jaddada cikin jawabinsa na Sabuwar Shekara, wanda aka watsa ta kafafen watsa labarai, inda ya yi mana albishir da ganin sauye-sauye da kyautatuwar al'amura. Kamar yadda ya faɗa a cikin jawabin nasa cewa, cikin shekarar 2025, Gwamnatin Tarayya za ta himmatu wajen yaƙi da tsadar…
Read More