Ra’ayi

Kalubalen jingine koyarwa a harshen gado a ƙananan makarantun Nijeriya 

Kalubalen jingine koyarwa a harshen gado a ƙananan makarantun Nijeriya 

Daga ABBA ABUBAKAR YAKUBU  Wata sanarwa da Ma'aikatar Ilimi ta Tarayya ta fitar dangane da batun jingine tsarin koyar da yaran makarantun firamare da ƙananan makarantun sakandire, cikin harshen uwa, wanda a baya yake ƙarƙashin Tsarin Ilimi na ƙasa, ta zo wa ’yan Nijeriya da dama a bazata. Ministan Ilimi, Dr. Tunji Alausa ne ya sanar da wannan babban saƙo da kansa a yayin da yake jawabi a wajen taron Majalisar Kula da Harkokin Koyarwa ta ƙasa wanda aka gudanar a birnin Akure na Jihar Ondo. Ministan ya yi bayyanin cewa za a koma amfani da harshen Turanci a matsayin…
Read More
A duba kiran Sarkin Kano kan buƙatar sasancin ECOWAS da ƙasashen Sahel

A duba kiran Sarkin Kano kan buƙatar sasancin ECOWAS da ƙasashen Sahel

Kiran da Mai Martaba Sarkin Kano, Dakta Muhammadu Sanusi II, ya yi ga Ƙungiyar Tarayyar ƙasashen Afrika ta Yamma (ECOWAS) da ta sasanta da ƙasashen Nijar, Burkina Faso da Mali abin dubawar shugabannin yankin ne. Kira ne da aka yi da hikima da hangen nesa a daidai lokacin da yankin Afrika ta Yamma yake fuskantar manyan ƙalubalen tsaro, tattalin arziki da siyasa waɗanda ba a taɓa ganin irin su ba. Maimakon a bar saɓanin ra'ayi ya rikiɗe zuwa rarrabuwar kai ta dindindin, ya kamata ƙungiyar ECOWAS ta yi amfani da kowace dama wajen dawo da aminci da sake gina haɗin…
Read More
’Yan Nijeriya akwai ƙura fa

’Yan Nijeriya akwai ƙura fa

Daga ALI ABUBAKAR SADIQ Makonnin da suka gabata na yi wani rubutu mai taken "Manakisar Amurka Ga Arewa". Abubuwa biyu ne suka faru a wancan lokaci. Na farko shine sanarwar tsagaita wuta tsakanin Amurka da Iran. Na biyu kuma shine bayanin ƙasar Amurka na umarci ma'aikatan jakadanci da ’yan ƙasarta su bar Nijeriya da kuma nesantar jihohin Arewa. Kamar yadda na bayyana a wancan rubutu cewa, tunda Iran ta gagari Amurka, inda ta kasa cimma muradunta da kuma datse mashigin Hormuz da Iran ta yi wanda ya janyo tashin gwauron zabi na farashin mai a duniya, yanzu Nijeriya ce a…
Read More
Trump ya jefar da ƙwallon mangwaro

Trump ya jefar da ƙwallon mangwaro

Daga ALI ABUBAKAR SADIQ To, yau dai 1st ga watan Mayu, 2026 wato bayan kwanaki 60 da shugaba Trump ya biyewa Netanyahu su ka far ma Iran, ya ce yakin da ya yiwa sun "Epic Fury" (Mummunan fushi), ya zo karshe a shari'ance. E, a shari'ance ne saboda dokar Amurka ta yi tanadin cewa shugaban kasa zai iya shiga yaki ba tare da cikakkiyar sahalewar majalisa ba idan ya gamsu da wata barazana ga Amurka. Amma akwai sharadin cewa lallai ne bayan kwanaki sittin ya dawo gaban majalisa ya nemi sahalewar majalisa domin ci gaba da yakin. A yau gwamnatin…
Read More
Iran ta ɗauki numfashin Amurka da Israila 

Iran ta ɗauki numfashin Amurka da Israila 

Daga ALI ABUBAKAR SADIQ Trump ne da kansa ya bayyana wa duniya cewa, sauran awa guda kacal ya rage ya bayar da umarnin kai wa Iran farmaki, amma ya dakatar sakamakon, a cewarsa, ƙasashen yankin Gulf ne suka nemi alfarmar haka, saboda ana samun ci gaba sosai wajen tattaunawar sulhu da Iran. Wasu majiyoyin sun nuna cewa, wannan rabin gaskiyar maganar ce, domin akwai wani bayanin na sirri da ya tilasta wa Amurka dakatawa da kai harin. Iran dai ta yi gum da bakinta, inda kawai abinda ta ce shine, da zarar an kai mata hari za ta mayar da…
Read More
Matsalar tsaro: Yadda ra’ayoyi suka bambanta kan tasirin jami’an tsaron gandun daji

Matsalar tsaro: Yadda ra’ayoyi suka bambanta kan tasirin jami’an tsaron gandun daji

Daga MAHDI MUSA MUHAMMAD Masana harkokin tsaro da shugabannin al’umma a Jihar Kwara sun bayyana ra’ayoyi mabambanta kan shirin ɗaukar jami’an tsaron gandun daji, domin kare yankunan da gwamnati ba ta da cikakken iko a kansu, a wani yunƙuri na daƙile matsalar rashin tsaro da ke ƙara ta’azzara a sassan Nijeriya. Wani tsohon jami’in tallafa wa ayyukan ’yan sanda na al’umma a Birtaniya, ɗan asalin birnin Ilorin mai suina Taiwo Hanbali AbdulRaheem, ya bayyana cewa, ɗaukar jami’an tsaron gandun daji mataki ne mai kyau da ya dace a wannan lokaci. Sai dai ya yi gargaɗin cewa jami’an ba su da…
Read More
Kalubalen samar da ’yan sandan jihohi ga tsaro 

Kalubalen samar da ’yan sandan jihohi ga tsaro 

Daga ABBA ABUBAKAR YAKUBU A yayin da nake wannan rubutu Majalisar Dattawa ta kammala aiki akan ƙudirin dokar da za ta bayar da damar kafa rundunar ‘yan sandan jihohi bayan an yi wa ƙudirin dokar karatu na uku, lamarin da ya kawo ƙarshen muhawarar da aka ɗibi tsawon shekaru ana gudanarwa akan tsarin ‘yan sandan jihohi, domin warware matsalolin taɓarɓarewar tsaro a Nijeriya. Rahotanni sun tabbatar da cewa, an cimma nasarar hakan ne bayan dogon nazari da kuma amincewa da ƙudirin a dokance daga biyu bisa uku na majalisar. Haka kuma, an amince da ƙudirin a zaman majalisar ne bayan…
Read More
Allah-wadai da kisan Ummulkhairi

Allah-wadai da kisan Ummulkhairi

Daga NASIRU ADAMU EL-HIKAYA Duk fa shi ne illar kamfen ɗin nan na ‘yan ikira irin gayawa jini na wuce kan Umummlkhairi a Marabar Jos duk miyagu sun yi gum kan kisan don haka su ke so Arewa ta zama. Duk ƙoƙarin nunawa mutane muhimmancin bincike da bin doka da oda, ya zama abin zagi da sharri daga Zallawa don burinsu birane da ƙauyuka su zama dandalin ɗaukar doka a hannu tamkar dai yadda ya auku ga Malamar Islamiyya Umumulkhairi a Marabar Jos a Kaduna inda daga tambaya ba wata shaida kawai mutane su ka zartar da hukuncin kisa har…
Read More
Kisan Maraban Jos da hatsarin al’adar ɗaukar doka a hannu

Kisan Maraban Jos da hatsarin al’adar ɗaukar doka a hannu

Kisan gilla da aka yi wa wata matar aure a garin Maraban Jos da ke ƙaramar Hukumar Igabi a Jihar Kaduna ya sake fito da wata babbar matsala da ta daɗe tana addabar al’ummomin Nijeriya – wato al’adar ɗaukar doka a hannu. Wannan mummunan lamari, wanda ya ƙare da banka wa wata mata wuta da ranta saboda zargin satar yara da ba a tabbatar ba, ya kamata ya zama abin da zai sa kowa ya tsaya ya yi tunani a kan inda al’umma ke dosa idan aka ci gaba da amincewa da irin wannan ɗabi’a mai haɗari. Rahotanni sun nuna…
Read More
Buɗaɗɗiyar wasiƙa zuwa ga matasanmu kan bangar siyasa

Buɗaɗɗiyar wasiƙa zuwa ga matasanmu kan bangar siyasa

Assalamu Alaikum wa Rahmatullahi wa Barakatuhu. Ya ku matasan Nijeriya, ina rubuto muku wannan wasiƙa ne cikin yanayi na damuwa da kuma fata. Damuwa saboda yadda siyasa ta ci gaba da raba zukata, iyalai, al'ummomi da abokantaka. Fata kuma saboda ku ne ƙashin bayan yau da gobe, kuma ku ne za ku iya sauya alƙiblar siyasar ƙasarmu zuwa hanya mafi kyau. A yau, abin takaici ne yadda wasu matasa ke ɗaukar siyasa a matsayin yaƙi maimakon fafatawar tunani. Bambancin jam'iyya ya zama dalilin gaba, zagi, cin mutunci da ma tashin hankali. Mutum zai ga matashi yana ƙin ɗan uwansa, makwabcinsa…
Read More