07
Jul
Daga ABBA ABUBAKAR YAKUBU Wata sanarwa da Ma'aikatar Ilimi ta Tarayya ta fitar dangane da batun jingine tsarin koyar da yaran makarantun firamare da ƙananan makarantun sakandire, cikin harshen uwa, wanda a baya yake ƙarƙashin Tsarin Ilimi na ƙasa, ta zo wa ’yan Nijeriya da dama a bazata. Ministan Ilimi, Dr. Tunji Alausa ne ya sanar da wannan babban saƙo da kansa a yayin da yake jawabi a wajen taron Majalisar Kula da Harkokin Koyarwa ta ƙasa wanda aka gudanar a birnin Akure na Jihar Ondo. Ministan ya yi bayyanin cewa za a koma amfani da harshen Turanci a matsayin…
