Ra’ayi

Shan miyagun ƙwayoyi na neman kassara makomar matasan Nijeriya

Shan miyagun ƙwayoyi na neman kassara makomar matasan Nijeriya

A duk lokacin da aka ambaci manyan matsalolin da suke yi wa Nijeriya barazana, mutane kan fi karkata hankali ga rashin tsaro, talauci, rashin aikin yi da hauhawar farashin kayayyaki. Sai dai akwai wata annoba da ke ci gaba da kutsawa cikin al'umma cikin shiru, tana lalata rayuwar dubban matasa, tana rusa iyalai, tana haddasa aikata manyan laifuka, kuma tana kassara makomar ƙasa. Wannan annoba ita ce shan miyagun ƙwayoyi da kuma fataucin su. A yau, shan miyagun ƙwayoyi ya zama wani babban ƙalubale da ya wuce matsalar mutum ɗaya ko iyali ɗaya. Matsala ce da ta shafi lafiyar jama'a,…
Read More
Farashin mai a mizani: Rijiyata ta bada ruwa guga ta hana?

Farashin mai a mizani: Rijiyata ta bada ruwa guga ta hana?

Abin mamaki da takaici ne yadda farashin man fetur ya ragu ƙwarai, amma har yanzu wasu dillalan mai sun ƙi sauke farashinsa. Sun ƙi bin sauyin da ya faru, suna ci gaba da sayar da mai yadda suka ga dama. Abin lura shi ne, idan farashin mai ya tashi, ba sa ɓata lokaci wajen ƙara farashi. Amma idan ya sauka, sai su yi kunnen uwar shegu, kamar ba su san abin da ke faruwa ba. Mu dai addu'armu ita ce Allah Ya hana duk wanda yake son ganin mun shiga ƙunci cimma burinsa. Tashin farashin da aka sha fama da…
Read More
Ko akwai waɗanda ƙasa ba ta cin jikinsu bayan binnewa?

Ko akwai waɗanda ƙasa ba ta cin jikinsu bayan binnewa?

Daga ALI ABUBAKAR SADIK Shin ko akwai waɗanda ƙasa ba ta cin jikinsu bayan binnewa? Tambayar da Shehil Islami Malam Aminu Bello ya jeho kenan. Da farko akwai bukatar a fahimci fadar Allah cikin Suratul Al Rahman cewa; "Dukkan abinda ke kanta (Duniya) mai ƙãrewa ne. Kuma Fuskarar Ubangijinka, Mai girman Jalala da karimci, ita ce take wanzuwa." Wannan aya cike ta ke da kimiyya da tauhidi. A kimiyance babu wata halitta da ta ke dorewa a Doron Duniya, domin Allah ya tsara duniyar yadda komai na cakuduwa da sabuntawa da karewa. Daga kasa aka halicci duk masu Rai Kuma…
Read More
Hukunta ‘yan ta’adda 150 cikin kwanaki biyu ya nuna sauyin salo a yaƙi da matsalar tsaro

Hukunta ‘yan ta’adda 150 cikin kwanaki biyu ya nuna sauyin salo a yaƙi da matsalar tsaro

Samun nasarar hukunta mutum 150 da aka samu da laifukan ta'addanci cikin kwanaki biyu kacal ya zama wani babban ci gaba a tsarin shari'ar Nijeriya. Wannan mataki ya nuna cewa Gwamnatin Tarayya ta fara ɗaukar yaƙi da ta'addanci da muhimmanci, tare da ƙoƙarin tabbatar da cewa masu aikata irin waɗannan manyan laifuka sun fuskanci hukunci cikin gaggawa. Babban Lauyan Tarayya kuma Ministan Shari'a, Lateef Fagbemi, ya bayyana cewa a sabon zagayen shari'ar da aka gudanar a Abuja, an saurari shari'o'i kusan 160, inda aka samu hukuncin ɗaurin laifi ga kusan mutum 150. Ya kuma buƙaci al'umma su ci gaba da…
Read More
Tarihin Gobir da yadda Gobirawa suka riski ƙasar Hausa

Tarihin Gobir da yadda Gobirawa suka riski ƙasar Hausa

Masarautar Gobir na ɗaya daga cikin tsofaffin daulolin ƙasar Hausa, kuma tana daga cikin manyan masarautun da suka taka muhimmiyar rawa a tarihin Arewacin Nijeriya da yankin Sahel. A tarihin da aka fi sani, ƙasar Gobir ta yi iyaka da Agades daga arewa, Zamfara daga kudu, Mayali daga gabas, sannan daga yamma ta yi iyaka da Konni. Sai dai, akwai ra'ayoyi mabambanta kan asalin Gobirawa. Wasu masana da masu riƙe da tarihin gargajiya na cewa Gobirawa ba Hausawa ba ne a asali, suna kuma danganta asalinsu da Gabas ta Tsakiya, musamman ƙwasar Masar (Egypt). Haka kuma, akwai masu cewa wasu…
Read More
Fitilar bada hannu: Ma’ana, muhimmancinta da illar rashin amfani da ita

Fitilar bada hannu: Ma’ana, muhimmancinta da illar rashin amfani da ita

Tare da BILKISU YUSUF ALI Gabatarwa A zamanin yau, harkokin sufuri da zirga-zirgar ababen hawa sun zama wani muhimmin ɓangare na rayuwar ɗan adam, musamman a birane. Yawaitar motoci da  babura da masu tafiya a ƙafa ya haifar da buƙatar tsari mai kyau domin tabbatar da tsaro da ingantacciyar zirga-zirga. ɗaya daga cikin manyan hanyoyin da ake amfani da su wajen sarrafa zirga-zirga shine fitilar bada hannu, wato traffic light a turance. Fitilar bada hannu wata na’ura ce da ake sanyawa a hanyoyi domin sarrafa motsin ababen hawa da masu tafiya a kafa ta hanyar amfani da launuka uku: ja,…
Read More
Illar ta’addanci a cikin al’umma

Illar ta’addanci a cikin al’umma

Gwamnati ta fitar da jerin sunayen wasu mutane da ake zargi da hannu a ayyukan ta’addanci. Abin takaici, da yawa daga cikin sunayen da aka bayyana suna daga cikin sunayen da aka fi sani a Musulunci da kuma Arewacin Nijeriya. Muna addu’ar Allah Ya sa wannan ƙoƙari ya kasance na gaskiya wajen bankaɗo asirai da kuma hukunta duk wanda aka tabbatar yana da hannu a irin waɗannan munanan ayyuka. Babu abin da ke ƙara ta’azzara ta’addanci kamar rashin ɗaukar matakin shari’a da kuma gaza aiwatar da hukunci ga waɗanda aka samu da laifi. Haƙiƙa, ta’addanci ba ya tsaya ga hare-haren…
Read More
Amurka na tsaka mai wuya a yaƙin Iran

Amurka na tsaka mai wuya a yaƙin Iran

Daga ALI ABUBAKAR SADIQ Amurka ta fara yakin Iran da tsammanin za ta murkushe su cikin makonni biyu, ko matuka a makonni uku. Ta hanyar muggan hare haren bama bamai a kasar tare da kashe shugabannin Iran, wanda su ke tsammanin zai haifar da tarzomar Iraniyawa ga gwamnatin su wanda zai tilasta su mika wuya. Me ya sa tsarin na Amurka ya kasa wanzuwa cikin nasarar da su ka tsammata? Ku san kowannenmu idan zai tuna yarinyarsa a makaranta ko a unguwa, akasari mun san wani mai cin zali (bully) da ya yi sharafinsa. Shi mai cin zali za ka…
Read More
Canje-canjen da Tinubu zai kawo na canja fasalin aikin NYSC

Canje-canjen da Tinubu zai kawo na canja fasalin aikin NYSC

Daga MAHDI MUSA MUHAMMAD Majalisar Zartarwa ta Tarayyar Nijeriya (FEC), ƙarƙashin jagorancin Shugaban ƙasa, Bola Ahmed Tinubu ta amince da gudanar da garambawul ga tsarin Hukumar Kula da Matasa Masu Yi Wa ƙasa Hidima (NYSC). Ministan Harkokin Matasa, Ayodele Olawande, ne ya bayyana hakan yayin da yake ganawa da manema labarai a Fadar Shugaban ƙasa da ke Abuja ranar Litinin, 29 ga watan Yuni, 2026. Olawande ya bayyana cewa an amince da sake fasalin NYSC ne a taron Majalisar Zartarwa da aka gudanar a Fadar Shugaban ƙasa da ke Abuja ranar Litinin. A cewarsa, garambawul ɗin zai haɗa da cikakken…
Read More
Shirin Labarina da wasiƙar Zallawa!

Shirin Labarina da wasiƙar Zallawa!

Daga NASIRU ADAMU EL-HIKAYA Ga wanda bai san su waye Zallawa ba to a gurguje gungun mutane ne da ke da’awar kafa ƙungiyar zallar Hausawa. Ba wani ma’auni da ke tabbatar da mutanen Hausawa ku kuwa akasin hakan. Haƙiƙa babban abin da akasarin ‘yan wannan gungun su ka shahara a kai shi ne ayyana dukkan Fulani a matsayin ‘yan ta’adda, kushe jihadin Shehu Usmanu Danfodio da nuna jidali ne maimakon jihadi har ma da yayata cewa Sir Ahmadu Bello Sardauna shi ya ja wa kansa fushin su Chukwuma Nzeogwu da su ka yi ma sa kisan gilla. An sha jan…
Read More