Ra’ayi

Farkar da zaɓaɓɓun shugabanni kafin zaɓe na gaba

Farkar da zaɓaɓɓun shugabanni kafin zaɓe na gaba

Daga ABBA ABUBAKAR YAKUBU A duk lokacin da aka ce kakar zaɓe ta tsaya, ’yan siyasa da masu goyon bayansu na fitowa su bayyana manufofin su da buƙatar a zaɓe su a muƙamai daban-daban. Yayin da suke alƙawura iri-iri ga jama'a don samun amincewa da goyon baya. Wani lokaci ma har da alƙawuran abubuwan da ba za su iya ba, ko kuma ya wuce ikon kujerar da suke nema, duk dai domin jan ra'ayin jama'a da masu faɗa a ji. Gwamnoni da dama a Nijeriya suna daf da cika shekara biyu da zaɓen da aka yi musu, tare da ’yan…
Read More
Matsalar tsaro da tattalin arzikin Dala Tiriliyan 1

Matsalar tsaro da tattalin arzikin Dala Tiriliyan 1

Manufar Gwamnatin Tarayya na samar da Dala Tiriliyan 1 na tattalin arzikin ƙasa ba zai yiwu ba idan har aka cigaba da samun taɓarɓarewar matsalar rashin tsaro a ƙasar. Mafita ita ce jami’an tsaro su gaggauta ɗaukar mataki tare da tabbatar da cewa an fatattaki ’yan bindiga da sauran miyagun da ke ta’addanci a ƙasar. Shugaba Bola Tinubu ya bayyana haka ne a lokacin da yake jawabi ga hafsoshin tsaro da shugabannin hukumomin leƙen asiri a wani taron tsaro da shugaban ƙasa ya gudanar kwanan nan a fadar shugaban ƙasa da ke Abuja. A cewar shugaban, yayin da ake samun…
Read More
Me dawowar Trump karo na biyu ke nufi?

Me dawowar Trump karo na biyu ke nufi?

Zai yi wuya a tarihin ‘yan shekarun da su ka wuce a samu wani tsohon shugaban Amurka da ya sha gwagwarmayar da zaɓaɓɓen shugaban Amurka Donald ya sha. Ya tsallake tarko da kadarko iri-iri kama daga na dakatar da shafin sa a kafar labarun yanar gizo na ɗ zuwa fuskantar tuhuma a kotu. Karshe dai za a rantsar da Trump a ranar 20 ga watan nan na Janairu don fara mulki a wa’adi na biyu kuma na ƙarshe da ya samu bayan faɗuwa zaɓe da ya yi a shekara ta 2020. Yanda jam’iyyar Dimokrats ta ture Trump a zaben baya…
Read More
Wasu na cewa ni ba ɗan Kwankwasiyya ba ne

Wasu na cewa ni ba ɗan Kwankwasiyya ba ne

Daga UNCLE LARABI To, ban san me zanyi na zama ɗan Kwankwasiyya ba. Na san dai tun 1999 nake son Engr. Sanata Rabiu Musa Kwankwaso. Mun haɗu da shi sau uku kacal ido da ido. Biyu a Rumfa Collage a Shekarar 2001 da kuma sanda ya dawo a shekarar 2011. Ina son sa, duk wanda ya san ni a zahiri ya san haka. Kuma duk wanda ya san Facebook Page ɗina, wanda aka yi ‘deactiɓate’ dalilin rubutun da na yi akan shi Engr. Rabi'u Kwankwaso da Tinubu da Peter Obi da Atiku mai taken ‘Komai sanyin tuwo ya fi teba!’ shine…
Read More
Rikicin Masarautar Kano: Saƙon da na tura wa abokina kan hukuncin Kotun ɗaukaka ƙara

Rikicin Masarautar Kano: Saƙon da na tura wa abokina kan hukuncin Kotun ɗaukaka ƙara

Daga IBRAHIM SHEME An Buƙaci na fassarar rubutun da na yi kan saƙon da na tura wa wani aboki na yau da safe a hirar mu ta WhatsApp: 1. Kotun ɗaukaka ƙara ba ta sauke Malam Muhammadu Sanusi II ba, ta soke hukuncin da Babbar Kotun Tarayya ta yi a kan sa ne. Saboda haka har yanzu dai yana nan a matsayin Sarkin Kano. 2. Abin da Kotun ɗaukaka ƙara ta yi kawai shi ne ta umarci Babbar Kotun jiha da ta sake naɗa wani alƙalin wanda zai yi tushin shari'ar. A zahiri, Gwamnatin Jihar Kano ce ke da iko…
Read More
Shirin Mata A Yau na Arewa 24: Shin inganta tarbiyya suke yi ko kuwa rusawa?

Shirin Mata A Yau na Arewa 24: Shin inganta tarbiyya suke yi ko kuwa rusawa?

Daga  HASSAN IMRAN  Assalamu Alaikum, ‘yan'uwana. Yau na zo da wata taƙaitacciyar nasiha ne akan illolin masu da'awar cewa mace na da hurumi da kuma daidaituwa da maza, da nufin ba da shawarwari da samar da mafita. Daga cikin ƙalubalen dake addabar al'ummar yankin Arewa akwai matsalolin zamantakewar aure. A shekarun baya, mata sun kasance masu biyayya kuma masu kula da tarbiyyar 'ya'yansu wanda hakan ya taimaka wajen gina Ingantacciyar al' umma da 'ya'ya masu albarka. Hakan harwayau ya taimaka wajen inganta cigaban da 'yan Arewa suka riƙa samu a matakai daban-daban, duk da kallon komabayan da ake yi mana.…
Read More
Wane dalili ke sanya mata mantawa da Allah lokacin biki?

Wane dalili ke sanya mata mantawa da Allah lokacin biki?

A halin da ake cikin yanzu, kowa, musamman samari sun tabbatar da cewa galibin mata na shiga wani yanayi na mantawa da ibada lokacin shagulgulan biki, da har ta kan kai su manta yin salla tsawon wuni guda. An gano yadda galibin matan ke ƙin yin sallar saboda dalilan kwalliya, da yanayin hidimar bikin. Sauran dalilan su ne yanayin kayan da matan ke sawa masu kama da tsirara, sai kuma hayaniyar wurin biki, da kuma uwa uba rashin son kada abu ya wuce su ba a yi da su ba. Wasu na ganin cewa, kwalliya ita ce abu na farko…
Read More
Zuwa ga masu shirin aure (I)

Zuwa ga masu shirin aure (I)

Assalam alaikum. Da fatan kowa ya yi sallah lafiya? Allah ya albarkaci jaridar Blueprint. A yau zan yi wasiƙa ne a kan zaɓin ma'aurata, domin shi ne babban abin da ke ci wa kowa tuwo a ƙwarya a halin yanzu. Wanda kuma hakan ke jawo yawan mace-macen aure, domin ana auren ne kawai barkatai ba tare da sanin wa ya kamata a aura ba. Babban hadafin da ya ke sanya mu zaɓar wanda zamu rayuwa da shi ko wacce zamu rayu da ita a matsayin rayuwar aure shi ne samun nutsuwar rayuwa, shi kuwa samun nutsuwar ruhi da abokiyar zama…
Read More
Sabuwar Dokar Haraji: Ƙalubalen da ke gaban gwamnonin Arewa

Sabuwar Dokar Haraji: Ƙalubalen da ke gaban gwamnonin Arewa

Daga ABBA ABUBAKAR YAKUBU Tun bayan da Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya gabatar da buƙatar kafa sabuwar Dokar Haraji, nake ta bibiyar muhawarar da ake tafkawa a kafafen watsa labarai, tsakanin ’yan siyasa, jami'an gwamnati da kuma masana tattalin arziki da sauran su. Ina jin babu wani batu da ya fi ɗaukar hankalin ’yan Nijeriya bayan batun cire tallafin man fetur, sai wannan sabuwar Dokar Haraji, da wasu 'yan Nijeriya ke ganin alheri ce ga tattalin arzikin ƙasar nan, duba da tanade-tanaden da aka yi wa dokar. Amma da dama 'yan Nijeriya, musamman 'yan Arewa na kallon wannan doka…
Read More
Cin gashin kan ƙananan hukumomi: Nasihar Tinubu ga gwamnoni

Cin gashin kan ƙananan hukumomi: Nasihar Tinubu ga gwamnoni

Kalaman da shugaba Bola Tinubu ya yi a baya-bayan nan game da ’yancin cin gashin kan ƙananan hukumomi ya haifar da zazzafar muhawara game da tsarin mulkin Nijeriya da yadda ƙananan hukumomi ke ci gaba da yin biyayya ga gwamnoni. Shugaban ya yi magana kan raɗe-raɗin da ake yaɗawa cewa yana takun saa da gwamnonin jihohi kan ’yancin ƙananan hukumomi. Shugaba Tinubu ya musanta raɗe-raɗin rashin jituwa tsakaninsa da gwamnonin kan yunƙurinsa na samar da ’yancin cin gashin kan ƙananan hukumomi a faɗin ƙasar nan, ya ƙara jaddada ƙudurin da ya yi tun da farko kan tanadin tsarin mulkin ƙananan…
Read More