Adabi

Tasgaron zuwan Turawa Ƙasar Hausa

Tasgaron zuwan Turawa Ƙasar Hausa

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Duk da irin alfanu da muka zayyana waɗanda suka samu a Ƙasar Hausa sakamakon zuwan Bature, ba kuma za a rasa tasgaro, cigaban mai haƙar rijiya, da kuma koma baya waɗanda zuwan Turawa ya haifar ba. Tabbataccen abu ne a tsarin rayuwa, cewa, duk lokacin da aka samu sauyi ko cuɗanya da wasu baƙin jama’a, waɗanda tasirinsu ya kai ga wata jama’ar ta sauya salon yadda take gudanar da rayuwarta, babu makawa, sai an samu abubuwan da za su saɓa da abin da yake karɓaɓɓe a tafarkin rayuwar waɗannan jama’a da aka zo aka taras. Zuwan…
Read More
Yana da kyau marubuta su ƙirƙiro da hanyar mayar da rubutunsu kan sauti – Farfesa Sufyan Wase

Yana da kyau marubuta su ƙirƙiro da hanyar mayar da rubutunsu kan sauti – Farfesa Sufyan Wase

"Ya kamata marubuta su riƙa tafiya da zamani" Daga ABBA ABUBAKAR YAKUBU Marubuta sun kasu kashi daban-daban. Akwai marubutan labaran hikaya, akwai marubutan tarihi, akwai marubutan faɗakarwa, akwai kuma na ilimi. Sufyanu Adamu Yakubu mai laƙabi da Farfesan Marubuta, marubucin kalmomin hikima ne da faɗakarwa, musamman abin da ya shafi zamantakewa da tarbiyya. Kasancewarsa malamin makaranta, hakan ya taimaka masa wajen yin rubuce-rubuce da suka shafi ilimi da cigaban rayuwa. A zantawarsa da Abba Abubakar Yakubu, Farfesan ya bayyana burinsa na zama cikakken Farfesa na gaske, kuma mawallafin littattafan kimiyya. A yi karatu lafiya. MANHAJA: Zan so ka fara gabatar…
Read More
Marubuta sun yi rawar gani cikin Ramadan – Queen Nasmah

Marubuta sun yi rawar gani cikin Ramadan – Queen Nasmah

Daga ABBA ABUBAKAR YAKUBU A cigaba da kawo muku tattaunawar da muka yi da marubuta da ƙungiyoyi game da ayyukan da suka gudanar cikin Ramadan, ƙarƙashin ƙungiyoyi da jagorori daban-daban. A wannan makon muna ɗauke ne da tattaunawar da wakilin Blueprint Manhaja Abba Abubakar Yakubu ya yi da wata marubuciya Asma'u Lawal Liman, wacce aka fi sani da Queen Nasmah, shugabar ƙungiyar Moonlight Writers Association. A zantawar da suka yi Nasmah ta bayyana irin shirye-shiryen da suka gabatar da kuma ayyukan da suke yi na jinqƙai da taimakawa mabuƙata, a lokacin azumi da bayansa. MANHAJA: Mu fara da sanin wacce…
Read More
Alfanun zuwan Turawa ƙasar Hausa

Alfanun zuwan Turawa ƙasar Hausa

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Wannan cigaba ne daga rubutun makon da ya gabata. Duk da cewa, Bature ya zo ya samu Bahaushe da cikakkiyar wayewar addini, sarauta, sutura, karatu da rubutu da kuma wayewar kasuwanci da sauransu. Amma duk da irin wannan cigaba da Bahaushe yake da shi kafin zuwan Turawa, an samu ƙarin cigaba a fannonin da dama sakamakon zuwan nasu. Wannan cigaban kuwa ya sauya yanayin yadda Bahaushe yake gudanar da harkokinsa na rayuwa kusan baki ɗaya sai dai ‘yan abubuwan da ba za a rasa ba. Idan muka kalli yanayin yadda Bahaushe yake gudanar da harkokinsa na…
Read More
Ya kamata marubuta su riƙa taimakawa mabuƙata – Nimcyluv

Ya kamata marubuta su riƙa taimakawa mabuƙata – Nimcyluv

"Na ciyar da mabuƙata fiye da ɗari cikin Ramadan" Daga ABBA ABUBAKAR YAKUBU Tun da watan Ramadan ya kama a wannan shekara, marubutan adabi maza da mata suka shiga cikin hidimar kyautata addininsu da kusancinsu da Allah, ban da shirye-shirye da suke gabatarwa a zaurukansu na Facebook da whatsapp, wasu kuwa har ƙungiyoyi ne da su da suke tallafa wa mabuƙata da ciyar da su abincin buɗe-baki. Na'ima Suleiman Sarauta na daga cikin marubutan da suke gudanar da irin wannan aikin neman lada na ciyarwa da taimakon marayu. A zantawarta da wakilin Blueprint Manhaja, Abba Abubakar Yakubu, Nimcyluv kamar yadda…
Read More
Anka ya zama shugaban ƙungiyar Hausa ta BUK

Anka ya zama shugaban ƙungiyar Hausa ta BUK

Daga ABBA ABUBAKAR YAKUBU Fitaccen marubucin littattafan Hausa da finafinan Kannywood, Malam Kabiru Yusuf Fagge wanda aka fi sani da ANKA ya zama shugaban ƙungiyar Hausa ta Jami'ar Bayero da ke Kano, a wani zaɓe da ƙungiyar ta gudanar ranar Jumma'ar da ta gabata 22 ga watan Maris, 2024 a zangon karatu na 2022/2023. Marubucin wanda yake ɗalibta a Sashin Nazarin Harsunan Najeriya, inda yake karatun digirinsa na farko a fannin Harshen Hausa, ya zama shugaban ƙungiyar ne bayan zaven da aka yi masa tare da wasu masu dafa masa su goma sha ɗaya. Da suka haɗa da shi, Kabiru…
Read More
Ko kun san tarihin fadar Aso Rock Villa?

Ko kun san tarihin fadar Aso Rock Villa?

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Fadar Gwamnatin Tarayya wadda ake kira State House a Turance. Wannan fada, ayari ne na ofisoshi da suka haɗa da Fadar Shugaban Ƙasa wadda ake kira Presidential Villa a Turance; ofishin mataimakin shugaban ƙasa, da sauransu. Haka nan kuma a cikin fadar ta shugaban ƙasa akwai ma’aikatan da suke gudanar da ayyukan da suka shafi ayyukan gudanarwa, tsare-tsare bisa ƙa’ida, harkar tsaron lafiyar shugaban ƙasa da fadar tasa da kuma harkokin yaɗa labarai, waɗanda dukkan su suke ƙarƙashin kulawar shugaban ma’aikatan gidan Gwamnatin Tarayya, wato Chief of Staff kenan, muƙamin da a yanzu haka (2024), Femi…
Read More
Rashin haɗin kai ne ke hana tasirin marubutan Jihar Sakkwato – Zarah BB

Rashin haɗin kai ne ke hana tasirin marubutan Jihar Sakkwato – Zarah BB

"Rubutu madubi ne da ke haska gobe" Daga AISHA ASAS Jihar Sakkwato na ɗaya daga cikin jihohin da ke ɗauke da kwararrun marubuta duk da cewa ba kasafai ake sanin su ba, wataƙila hakan ba ya rasa nasaba da daidaitacciyar Hausa da suke amfani da ita, wadda ke hana a gane su da Hausa irin ta Sakwatawa, har sai dai idan su ne suka faɗa. A yau shafin adabi ya ɗauko ma ku ɗaya daga cikin jajirtattun marubuta da suka fito daga Birnin Shehu, Fatima Bello Bala, wacce aka fi sani da Zarah BB. Matashiyar marubuciya ce da ke bada…
Read More
Ahmed Baba: Shahararren malamin Timbuktu

Ahmed Baba: Shahararren malamin Timbuktu

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Ahmed Baba ya kasance ɗaya daga cikin manyan malamai na Afirka a ƙarni na 16. Marubuci kana masanin addinin Islama, ya yi aiki game da shari'a kan batun bauta da rubuta tarihin mashahuren mutane. Lokacin da Ahmed Baba ya rayu: An haifi Ahmed Baba a shekarar 1556. Wasu majiyoyi sun ce a Araouane, kimanin kilomita 250 Arewa maso Yammacin Timbuktu, birnin da ke arewacin Mali. Akwai kuma yiwuwar an haife shi a Timbuktu lokacin birnin na bunƙasa a matsayin cibiyar binciken addinin Islama da harkokin kasuwanci na yankin Sahara. Baba ya yi karatu a birnin Timbuktu…
Read More
Rubutu ya sauya min rayuwata da duniyata – Ramlat Manga Maidambu

Rubutu ya sauya min rayuwata da duniyata – Ramlat Manga Maidambu

"Na sha wahalar rubuta littafina na farko" Daga ABBA ABUBAKAR YAKUBU Ramlat Abdulrahman Manga, wacce aka fi sani da Maidambu, na daga cikin jajirtattun marubuta onlayin da aka sha gwagwarmaya da su a duniyar marubuta, tun ba a san ko ita wacce ce ba. Ta yi rubuce rubuce da dama, waɗanda suka samu karvuwa a wajen jama'a har kuma ita ma ta yarda cewa ta samu alheri sosai. Tana daga cikin marubutan adabi da suka fito daga Jihar Bauci kuma take bai wa mara ɗa kunya wajen ɗaga sunan jihar a harkar batun rubuce-rubucen Hausa. A zantawarta da Abba Abubakar…
Read More