Adabi

An karrama marubuci Abba Abubakar Yakubu

An karrama marubuci Abba Abubakar Yakubu

Daga HABU ƊAN SARKI a Jos Fitaccen marubucin nan kuma jarumin finafinan Kannywood, Ado Ahmad Gidan Dabino (MON) ya taɓa faɗa cewa, 'Duk wani abu mai kyau da ka ke yi duniya tana gani, kuma wata rana za ka samu sakamakonsa.' Wannan bayani nasa ne ya fito a fili jama'a suka shaida, a ƙarshen makon da ya gabata, inda wata cibiya mai koyar da ilimin fasahar sadarwa da kula da adana littattafai, wato Information and Library Science, mai suna Majema College of Advanced Studies Jos ta karrama marubuci kuma ɗan jarida, Abba Abubakar Yakubu, sakamakon jajircewa da gudunmawar da yake…
Read More
Yadda marubutan adabi suka yi bikin Ranar Marubuta ta 2024

Yadda marubutan adabi suka yi bikin Ranar Marubuta ta 2024

Daga ABBA ABUBAKAR YAKUBU Ana gudanar da bikin Ranar Marubuta ta Duniya ne a ranar 3 ga watan Maris na kowacce shekara, domin ƙara zaburar da marubuta a ko'ina a duniya game da gudunmawar da suke bayarwa wajen faɗakarwa da ilimantar da jama'a da suke yi, musamman matasa da ɗaliban ilimi. Tun a shekarar 1986 aka fara bikin ranar a faɗin duniya, bayan shawarwarin da ƙungiyoyin marubuta da mawaqƙa daban-daban suka riƙa bayarwa don ganin an ware wata rana guda da za a riƙa tattauna abubuwan da suka shafi harkar rubutu da basirar ƙirƙira. Sau da dama jama'a sun fi…
Read More
Makaɗin Hausa: Marigayi Alhaji Sa’idu Mai Daji Sabon-Birni

Makaɗin Hausa: Marigayi Alhaji Sa’idu Mai Daji Sabon-Birni

Daga MAHDI M. MUHAMMAD An haifi Alhaji Sa’idu Mai Daji a garin Tara ta sarkin Kwanni, ita kuma Tara tana bin Sabon-Birni ta sarkin Gobir, jihar Sakkwato. Sannan mahaifinsa shi ne Mainasara. Ya kiyasta cewa yana da shekara arba’in da biyar (45), watau ke nan an haife shi a wajejen 1938. Dalilin kiransa Maidaji shi ne, a lokacin rayuwar mahaifinsa suna zaune ne a tsohon garin Tara. Sai wata rigima da faɗace-faɗace ta haddasu tsakanin mutanen Tarar, sai aka yi ta tashi ana barin garin, bayan kuwa har sun yi shuka. Mahaifinsa Mainasara, ya ce shi kam ba zai bar…
Read More
Rashin kiyaye ƙa’idojin rubutu illa ce ga marubuci – Mubarak Jiƙamshi

Rashin kiyaye ƙa’idojin rubutu illa ce ga marubuci – Mubarak Jiƙamshi

"Manazarcin Hausa na samun tagomashi mai tsoka a harkar fashin baƙi ko tambihi" Daga ABBA ABUBAKAR YAKUBU Mubarak Idris Jikamshi, matashin marubuci ne daga Jihar Katsina, duk da kasancewar bai fitar da wasu littattafai masu yawa ba, amma yana da gajerun labarai da dama da ya yi, wasu ma har ya shiga gasannin marubuta da su, a mataki daban-daban. Wani abu da ya bambanta Mubarak da sauran marubuta shi ne kishin da yake da shi a nazarin ilimin harshen Hausa da kula da kiyaye ƙa'idojin rubutu, don yanzu haka yana matakin fara digirinsa na biyu ne a harshen Hausa. Bayan…
Read More
Marigayi Mada Garin Aliyu Babba Ɗan Malam Muhammadu Sambo

Marigayi Mada Garin Aliyu Babba Ɗan Malam Muhammadu Sambo

Daga IBRAHIM MUHAMMAD Asalin su Fulani ne da suka fito daga yankin Ningi ta Jihar Bauchi da zummar za su kai caffa a wajen Mujaddadi Shehu Usman Ɗanfodiyo Tagammadahullahu birahamatihi a Sakkwato domin shiga dumu-dumu a cikin jihadin jaddada addinin Musulunci wanda Mujaddadi Shehu Usman Ɗanfodiyo ya jagoranta. Sun zauna a wurare da dama kamar Ƙiru da Gwarzo (da ke Jihar Kano ta yau) da Matazu da Fawwa ( dake Jihar Katsina a halin yanzu) da kuma Wonaka da ke Jihar Zamfara ta yanzu, kafin daga bisani Malam Muhammadu Sambo ya jagorance su ya zuwa inda suke a halin yanzu.…
Read More
Idan ka ga marubuci yana rubutu ba ya samun kuɗi shi ya so – Sadik Lafazi

Idan ka ga marubuci yana rubutu ba ya samun kuɗi shi ya so – Sadik Lafazi

"Wasu ƙungiyoyin ba sa son ɗaukar sabon marubuci" Daga ABBA ABUBAKAR YAKUBU Baƙon marubucin mu na wannan mako shi ne Malam Sadik Abubakar Abdullahi, shugaban ƙungiyar Lafazi Writers Association, ɗaya daga cikin fitattun ƙungiyoyin marubuta na onlayin da suke taka rawar gani wajen fitar da littattafai masu ƙunshe da basira da darussa masu yawa, da kuma kiyaye ƙa'idojin rubutun Hausa. Ya kasance daga cikin maza marubuta da suka zama tamkar madubi ko ababen koyi ga matasan marubuta masu tasowa. A zantawarsa da wakilin Blueprint Manhaja Abba Abubakar Yakubu ya bayyana masa yadda yadda shi da wasu marubuta suka kafa ƙungiyar…
Read More
Rayuwar Sarki Haile Selassie na Habasha

Rayuwar Sarki Haile Selassie na Habasha

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Haile Selassie an haifeshi a ranar 23 ga watan Yuli na shekara ta 1892 a kusa da Harar cikin ƙasar Habasha, inda aka raɗa masa suna da Tafari Makonnen. Mahaifinsa amintacce ne kuma na kusa da Sarki Menelik na II. An kira shi zuwa kotu a Addis Ababa lokacin da babansa ya mutu a 1906. A 1916 ya zama mabiyin aqidar Ras Tafari, da ake zaton ya gaji sarauniya Zauditu da ke zaman 'ya ga Menelik na II. A shekara ta 1928 tare da magoya bayansa sun sanya sarauniyar ta ba shi sarauta. A shekara ta…
Read More
Duk waƙar da ta rubutu, babu wanda ba ya iya rera ta – Malumman Matazu

Duk waƙar da ta rubutu, babu wanda ba ya iya rera ta – Malumman Matazu

"Jigon waƙa na cikin ababen da ke ban wahala" (Ci gaba daga makon jiya) Daga AISHA ASAS A satin da ya gabata, shafin Adabi ya samu baƙuncin ƙwararre a ɓangaren rubutacciyar waƙa, Abdulhamid Muh'd Sani Matazu, inda muka faro tattaunawar kan abinda ya shafi ma'anar rubutacciyar waƙa da abinda ya bambanta ta da waƙar baka. Kafin mu kai ga tasirin da shawarwarin da suke bayarwa a waƙe suke yi. A wannan makon za mu ɗora ne daga inda muka tsaya: MANHAJA: Me yafi baka wahala a yayin rubuta waƙa? MALUMMAN MATAZU: Jigo ko dalilin waƙa na cikin abin da ke…
Read More
Makaɗin Hausa: Marigayi Salihu Jankiɗi (1852-1973)

Makaɗin Hausa: Marigayi Salihu Jankiɗi (1852-1973)

Daga MAHDI M. MUHAMMAD An haifi Salihu Jankidi ne a garin Rawayya ta ƙasar Bungudu ne a yanzu cikin Ƙaramar Hukumar Gusau, wajejen shekara ta 1852. Sunan mahaifinsa Alhassan ɗan Giye ɗan Tigari mai abin kiɗi. Salihu shi ne sunansa na yanka, amma ƙanen mahaifiyarsa Kardau ya yi masa laƙabi na Jankiɗi saboda jan da Allah ya ba shi, wanda ya bi shi har bayan rasuwarsa. Alhassan Giye Ɗan Tigari: Mahaifin Jankidi Alhassan Makadi ne na kalangu kuma mai yawan yawace-yawace don kiɗa. Yakan bar garinsu Rawayya ya shiga uwa duniya don sana’arsa ta kiɗa. Shi kuma makaɗi ne na…
Read More
Rubutacciyar waƙa ta masu ilimi ce, waƙar baka kuwa ta kowa ce – Malumman Matazu

Rubutacciyar waƙa ta masu ilimi ce, waƙar baka kuwa ta kowa ce – Malumman Matazu

"Duk wanda yake yin rubutacciyar waƙa zai iya waƙar baka" Daga AISHA ASAS  A wannan satin dai ba bako shafin adabi ya kawo wa masu karatu ba, kasancewar mun saba kawo shi a bangarori da dama na adabi. Don haka za mu wuce kai tsaye ga tattaunawar.  Idan kun shirya Aisha Asas ce tare da Malumman Matazu: MANHAJA: Duk da ba ka kasance bako a jaridar Manhaja ba, za mu so mu ji takaitaccen tarihinka? MALUMMAN MATAZU: Bismillahirrahmanirrahim. Da farko dai cikakken sunana shi ne: Abdulhamid Muh'd Sani Matazu (Malumman Matazu). An haife ni a Gidan marigayi liman Malam Bala…
Read More