Adabi

Labarin littafin ‘A Gentle Breeze” ya sa ni kuka ya sa ni dariya – Kabiru Musa Jammaje

Labarin littafin ‘A Gentle Breeze” ya sa ni kuka ya sa ni dariya – Kabiru Musa Jammaje

DAGA MUKHTAR YAKUBU  Idan ana magana a game da marubuta da suka bayar da gudunmawa a ƙasar Hausa musamman ta fuskar matasa, to Malam Kabiru Musa Jammaje yana cikin sahun gaba.  Duk da kasancewar sa marubucin harshen Turanci ne shi, amma gudunmawar da ya bayar ta zarta ta wasu marubutan Harshen Hausa ne ba kusa ba. Domin kuwa kasancewar sa malami a harshen Turanci, ta sa ya rinƙa buga littattafai domin koyon harshen Turanci a tsakanin matasan mu, wanda hakan ya sa matasa da dama suka koyi yaren Turanci cikin sauƙi kuma har suka zama abin alfahari a gare mu.…
Read More
Gudunmawar da marubuta suka bai wa duniya da alƙaluman su

Gudunmawar da marubuta suka bai wa duniya da alƙaluman su

Daga JUBRIN YUSUF KAILA Ranar Marubuta ta Duniya, wanda aka fi sani da "World Writers' Day," rana ce da aka ware domin yabawa da kyakkyawar gudunmawar marubuta ga al'umma da al'adun duniya. Wannan rana tana nuni da muhimmancin rubuce-rubuce wajen inganta tunani, ilimi, da kuma kawo canji mai kyau a cikin al'umma. Ta kuma zama wata hanya ta kawo kyakkyawar fahimta game da rawar da marubuta ke takawa a cikin al'adunmu, musamman wajen yaɗa labarai, ilimantarwa, da kuma samar da damar tattaunawa tsakanin al'ummomi daban-daban. An ƙaddamar da wannan rana ne a shekarar 1999, lokacin da Majalisar ɗinkin Duniya ta…
Read More
Ban taɓa sayar da littafina ba – Khadija Ɗahiru

Ban taɓa sayar da littafina ba – Khadija Ɗahiru

"Da ana duba rubutu kafin fitar da shi, da an rage ɓarnar da ake yaɗawa a littafan Hausa" Daga AISHA ASAS  Rubutu a yanar gizo wani abu ne da zamani ya zo da shi, don haka ba shi muhalli da wasu daga cikin marubuta suka yi bai taɓa zama laifi ba, domin idan ba su bi ba, zai kasance an yi tafiyar ba tare da su ba. A wani ɓangaren kuwa, za mu iya kiran rubutun yanar gizo sauƙi ga masu baiwar ta rubutu, kasancewar ya ba wa kowa damar baje fasahar sa, ma'ana mai kuɗin iya buga littafi da…
Read More
Rubutu mai inganci ba ya buƙatar gaggawa – Ado Bala

Rubutu mai inganci ba ya buƙatar gaggawa – Ado Bala

"Karatu na sanya mutum ya kasance mai nagarta da kyautata ɗabi'a" Ba na damuwa da jigon labari fiye da yadda nake damuwa a kan taurarin labarin Daga ABBA ABUBAKAR YAKUBU Malam Ado Bala, marubucin littafin, 'Husufin Farinciki', wanda ya yi nasarar zama na uku a Gasar Tsangayar Gusau na shekarar 2019, irin marubutan nan ne da ake ce wa taurarin ɓoye, waɗanda ba su cika bayyana kansu ko su kururuta basirar da Allah ya yi musu ba, sai ga wanda ya gano su ko ya kusance su. Alhalin kuwa, Malam Ado tauraro ne na nuna wa Sarki, saboda baiwar da…
Read More
Rayuwar marubuta littattafai na cikin haɗari a Isra’ila 

Rayuwar marubuta littattafai na cikin haɗari a Isra’ila 

Daga ABBA ABUBAKAR YAKUBU  Ýansandan Isra'ila sun kai samame wani kantin sayar da littattafai mallakin wasu Falasɗinawa da ke Gabashin Birnin Jerusalem, da Isra'ila ta mamaye, tare da kama masu kantin su biyu, abin da masu nazarin harkokin adabi, ýanjarida da masu nazarin zamantakewa ke kallo a matsayin zalunci ne da shigar da batun ilimi cikin harkar siyasa.  Mahmoud Muna da ɗan uwansa Ahmad, sun kasance a tsare a hannun 'yansanda tun bayan kamun da aka yi musu ranar Lahadi da ta gabata, yayin da lauyansu Nasser Odeh, ke cewa ana tsare da su ne cikin wani mawuyacin yanayi da…
Read More
Littafin ‘Wasa Da Rayuwa’: Ya bankaɗo tushen ƙalubalen tsaro a jihohin Arewa

Littafin ‘Wasa Da Rayuwa’: Ya bankaɗo tushen ƙalubalen tsaro a jihohin Arewa

Daga ABBA ABUBAKAR YAKUBU  Duk wanda Allah Ya nufa da samun damar karanta littafin 'Wasa Da Rayuwa' wanda Zainab Abdullahi Musa, da aka fi sani da Lailat Abdullahi, ta rubuta, kuma littafin da ya zama na uku a Gasar Tsangayar Gusau na shekarar 2024, zai fahimci lallai ana samun cigaba sosai a harkar rubutun adabi na Hausa. Sannan su kansu matasan marubuta na yanzu, musamman waɗanda suka fara rubutu a zamanin rubutun onlayin, suna ƙara samun gogewa da sanin dabarun rubutun labari, wanda zai zama abin misali a ko'ina a duniya.  'Wasa Da Rayuwa', littafi ne da ke ɗauke da…
Read More
Ba don rubutu ba da addini bai zo mana ba – Rahama Sabo Usman

Ba don rubutu ba da addini bai zo mana ba – Rahama Sabo Usman

"Mahaifiyata ce ta sa na fara rubutun littafi" Daga ABBA ABUBAKAR YAKUBU  Tauraruwar adabinmu ta wannan mako ba kowa ba ce face, Malama Rahama Sabo Usman, marubuciya daga Jihar Kano. Wacce ta yi fice a ýan shekarun baya, sakamakon gwagwarmaya da ta yi da yaɗuwar rubutun batsa, wanda har ya kai ga kafa wata babbar ƙungiya da aka yi wa rijista da sunan, Gamayyar ƙungiyoyin Marubutan Jihar Kano (GAMJIK). Rahama ta kasance marubuciya mai baiwa da yawa, bayan kasancewarta mai rubutun labaran hikayoyi da gajerun labarai, tana kuma rubutun wasan kwaikwayo, da ɗora murya a wasannin kwaikwayo na rediyo da…
Read More
Sharhin waƙoƙin korona na Hausa na ‘Corona Blues’

Sharhin waƙoƙin korona na Hausa na ‘Corona Blues’

Daga MURTALA MUHAMMED (PHD) Sunan Littafi: Corona Blues (A bilingual Poetry Collection) Editoci: Isma’il Bala da Khalid Imam  Maɗaba’a: Whetstone Publishers Kano, Nigeria ɗaukan nauyin bugawa: Gidauniyar MacArthur da Cibiyar Ilimtarwa ta ƙasa-da-ƙasa (IIE) Adadin Shafi: 165 Lambar ɗab’i: ISBN 978-978-58335-1-5 Shekarar da aka wallafa: 2020 Sharhi: Murtala Uba Mohammed (PhD) Shimfiɗa: A duk lokacin da mutum ya shiga cikin damuwa da fargaba yakan nemi waraka da samun sauƙi ne ta yin amfani da hayoyin da yake ganin za su iya warware masa irin ƙuncin da ya shiga. Waƙa na ɗaya daga cikin manyan magunguna da akan yi amafani da…
Read More
An bai wa marubuta mata horo kan dabarun inganta rubutunsu

An bai wa marubuta mata horo kan dabarun inganta rubutunsu

Daga ABBA ABUBAKAR YAKUBU  Cibiyar Nazari da Karantar da Harshen Hausa da Al'adu ta ƙasar Togo tare da haɗin gwiwar ƙungiyar Muryar Afirka Midiya sun gudanar da wani taron bita na yini biyu, daga ranakun Asabar 18 da Lahadi 19 ga watan Janairu, 2025 domin koyar da marubutan adabi mata zalla wasu dabaru na yadda za su ƙara inganta ayyukansu na rubuce-rubuce. Taron bitar wanda ya gudana a ɗakin taro na American Space da ke Babban ɗakin Karatu na Murtala Mohammed a Kano, ya samu halartar marubuta mata fiye da talatin da suka fito daga jihohin Kano, Kaduna, Katsina, Kebbi,…
Read More
Littafin ‘Gawa Ta Ƙi Rami’ ya bankaɗo illolin cin amana da rashin gaskiya

Littafin ‘Gawa Ta Ƙi Rami’ ya bankaɗo illolin cin amana da rashin gaskiya

Daga ABBA ABUBAKAR YAKUBU  Lokacin da na kammala karanta littafin Gawa Ta ƙi Rami' na Ayuba Muhammad ɗanzaki, abin da ya fara faɗo min a rai shi ne, 'Ga fa magajin Bala Anas Babinlata da Nazir Adam Salihi!' Na faɗi haka ne kuwa bisa lura da na yi da irin salon labarin da marubucin ya tsara. Labari ne da a turance ake kira da 'thriller' wato salon 'ƙirji-ɗarɗar', kamar yadda aka yi masa fassara da Hausa. Shi wannan salo yana zuwa ne a yanayin labari mai ɗauke da rikita-rikita, tsoratarwa, fargaba, kwamacala, wani lokaci ma har da kashe-kashe.  Littafin Gawa…
Read More