Adabi

Ina da burin ganin kasuwar littafai ta dawo hayyacinta – Saliha Abubakar Abdullahi Zaria

Ina da burin ganin kasuwar littafai ta dawo hayyacinta – Saliha Abubakar Abdullahi Zaria

"Rubutu tamkar zazzaɓi ne, duk lokacin da masassarar ta taso, ɗaukar alƙalami da takarda ne magani" Daga AISHA ASAS Waiwaye dai aka ce adon tafiya ne, yayin da rawar 'yan mata kan ƙayatar ne a lokacin da suke yin gaba suna dawowa baya. Idan akayi zancen Adabin Hausa, dole ne a sanya marubuta mata da suka fara rubutu tun lokacin da kai bai waye ba. Su ne marubutan da suka fuskanci ƙalubale masu yawa kasancewar sun fara abin da al'ummar Hausa ba su fara gani ba, don haka suka jahilce shi har ta kai su na masa mummunar fahimta.  Don…
Read More
Jarumi Hanks ya tayar da ƙura bayan fitar bidiyon sa zaune gefen hanya a Abuja 

Jarumi Hanks ya tayar da ƙura bayan fitar bidiyon sa zaune gefen hanya a Abuja 

Daga AISHA ASAS  Sabon bidiyo da ya bazu a kafafen sada zumunta ya sake jefa masoya fina-finan Nollywood cikin damuwa bayan an hango fitaccen jarumi Hanks Anuku zaune shi kaɗai a gefen wata hanya a Abuja. Bidiyon ya fara yaɗuwa ne bayan wani mai amfani da shafin X mai suna Anthony Ehilebo ya wallafa shi, yana mai cewa shi da kansa ya ci karo da jarumin a yankin Wuse 2 da ke Abuja. A cikin bidiyon, an ga Hanks Anuku zaune a kan ciyawa da ke gefen hanya yana riƙe da wani abu mai kama da kofi. Da yake wallafa…
Read More
Fitattun taurarin da suka yi ridda: Mene ne alaƙar dake tsakanin fitattun mutanen da suka bar Musulunci?

Fitattun taurarin da suka yi ridda: Mene ne alaƙar dake tsakanin fitattun mutanen da suka bar Musulunci?

(Ci gaba daga makon jiya) Daga AISHA ASAS A taƙaice dai sauya addini a cikin al'ummar Yarbawa bai zama abin faɗi ba ko bada labari ba, kuma kaso mai yawa daga cikinsu suna canza addinin ne zuwa inda ya fi masu sauƙi ba wai gano gaskiya ba. Ba wai ina nufin al'ummar Yarbawa ba sa riƙo da addini ba, a binciken da aka yi a kwanakin baya ya nuna yadda bayaraben da ya yi riƙo da addini ke zarce kowa wurin iya yi masa sadaukarwa. Akan samu wasu ƙalilan daga Yarbawan da suka ƙiya wa wannan al'ada tasu ta fifita…
Read More
Yadda rubutun Hausa da na Turanci ke bayyana a aikace

Yadda rubutun Hausa da na Turanci ke bayyana a aikace

Daga AISHA ASAS Mai karatu barkanmu da sake kasancewa a shafin Adabi. Sannunku da jimirin bibiyar jaridar al’umma, Blueprint Manhaja. A makon da ya gabata mun gabatar muku da maƙala mai taken 'Me ya bambanta marubutan Hausa da na Turanci?' Inda muka warware muku biri har wutsiya kan bambancin da ke akwai tsakanin rubutun Turanci da na Hausa. A wannan makon ma ba mu gaji ba, domin za mu tattauna kan yadda rubutu kansa ke iya bayyana wa mai karatu bambancin da ke tsakanin rubutun Hausa da na Turanci. Duk da cewa tarihin adabi da ra’ayoyin masana suna taimakawa wajen…
Read More
Me ya bambanta marubutan Hausa da na Turanci?

Me ya bambanta marubutan Hausa da na Turanci?

Shigowar Musulunci ya kawo babban sauyi a adabin Hausa - Masana tarihi  Daga AISHA ASAS Za ka iya gane marubucin Hausa daga shafi guda kacal? Ko kuwa akwai wasu sirrika da ke bambanta shi da marubucin Turanci tun kafin a kai ƙarshen babi na farko? Wannan tambaya ce da masana adabi suka shafe shekaru suna nazari a kanta. Duk da cewa, adabi hanya ce ta bayyana tunani, motsin rai da hangen nesa, masana suna ganin cewa, babu wani adabi da ke tasowa a banza. Kowane adabi yana ɗauke da tarihinsa, al’adunsa, addininsa da kuma tsarin rayuwar mutanen da suka haife…
Read More
Poetic Wednesdays ta yi bikin cika shekaru 10 da fitar da jigo akan harsuna na taron KAPFEST na Uku

Poetic Wednesdays ta yi bikin cika shekaru 10 da fitar da jigo akan harsuna na taron KAPFEST na Uku

Ƙungiyar Poetic Wednesdays ta gudanar taron Eid Pop-Up a ranar Asabar, 6 ga Yuni, 2026, domin bikin cika shekaru goma da kafuwarta tare da bayyana sabon jigon bikin Kano International Poetry Festival (KAPFEST) karo na uku, mai taken “Reclaiming Languages”, wato ɗabbaka yaruka. An gudanar da taron ne a Alliance Française da ke Kano, inda ya haɗa mawaƙan baka, marubuta, masu sha’awar adabi da sauran jama’a domin tattaunawa, nazari da kuma nishaɗantarwa ta hanyar fasaha. Taron ya kasance wata dama ta waiwayen nasarorin da ƙungiyar ta samu cikin shekaru goma da kuma bayyana shirye-shiryenta na gaba. A yayin taron, an…
Read More
Me ya sa littattafan Hausa suka gaza gogayya da sauran littattafai na harsunan duniya?

Me ya sa littattafan Hausa suka gaza gogayya da sauran littattafai na harsunan duniya?

Daga ZAHARADDEN IBRAHIM KALLAH Bayan wani gajeren rubutu da na yi a kan gasar gajerun labarai ta Bashir Othman Tofa da aka gudanar a Kano, na samu tambayoyi a kan yanayin da littattafan Hausa suke ciki, musamman na rashin ingantattun zarurrukan labarai da kyan bugu littattafai da rashin kyakkyawan tsarin kasuwancin su a Najeriya ta yadda za a yaɗa su a duniya? Akwai waɗanda suke ganin su kansu marubutan ba su samu gudunmawar da ta dace ba, inda sabbin marubuta ma ba sa samun kulawa da gata na horon da ya kamata, kamar yadda takwarorinsu na Turanci suke samu. Tabbas…
Read More
Ba na fuskantar wani ƙalubale a kasuwancin sayar da littattafaina – Fatima AbbaGana 

Ba na fuskantar wani ƙalubale a kasuwancin sayar da littattafaina – Fatima AbbaGana 

"Na ɗauki Alan Waƙa a matsayin ɗan'uwana" (Ci gaba daga makon jiya) Daga ABBA ABUBAKAR YAKUBU  Sunan Fatima Abba Gana ba ɓoyayye ba ne a tsakanin marubutan adabi na Nijeriya, musamman saboda yadda take da zumunci da ilimin zama da jama'a. Bayan kasancewarta marubuciya, Fatima ta kasance tsohuwar ma'aikaciyar banki, ýar kasuwa, kuma ƙwararriya kan binciken shigi-da-ficen kuɗi. Ta rubuta littattafai daban-daban cikin harshen Hausa da Turanci, inda take mayar da hankali kan labaran da suka shafi raya al'ada, inda zamantakewa da kyautata tarbiyya. Ita ce ta rubuta littafi mafi girma da wata marubuciya a Arewa ta wallafa, domin kuwa…
Read More
Rubutun Turanci ya fi min sauƙin rubutawa da sarrafa jigo – Fatima AbbaGana

Rubutun Turanci ya fi min sauƙin rubutawa da sarrafa jigo – Fatima AbbaGana

"Ina ba littafi daraja sosai fiye da yadda a ke zato" Daga ABBA ABUBAKAR YAKUBU  Sunan Fatima Ibrahim AbbaGana ba ɓoyayye ba ne a tsakanin marubutan adabi na Nijeriya, musamman saboda yadda take da zumunci da ilimin zama da jama'a. Bayan kasancewarta marubuciya, Fatima ta kasance tsohuwar ma'aikaciyar banki, ýar kasuwa, kuma ƙwararriya kan binciken shigi-da-ficen kuɗi. Ta rubuta littattafai daban-daban cikin harshen Hausa da Turanci, inda take mayar da hankali kan labaran da suka shafi raya al'ada, inda zamantakewa da kyautata tarbiyya. Ita ce ta rubuta littafi mafi girma da wata marubuciya a Arewa ta wallafa, domin kuwa littafin…
Read More
Dambe wasar maza, kowwayyi hankali ya barka: Waiwaye kan tarihin kiɗan dambe na Dan’anace (5)

Dambe wasar maza, kowwayyi hankali ya barka: Waiwaye kan tarihin kiɗan dambe na Dan’anace (5)

(Karshe) Daga IBRAHIM MUHAMMAD  (Danmadamin Birnin Magaji) Hira da Makaɗa Dan’anace Gandi/'Yartsakkuwa tare da Malam Ahmadu Sakkwato a gidan Rediyon Rima da ke Sakkwato a shekarar 1978 Kiɗa.....Za ni gidan Alhaji Alu Layi, Mai Gabatarwa To madallah Alhaji ɗan’anace, koda yake ka rigani hanzari, to masu saurarenmu, assalamu alaikum, barkan mu da saduwa a wannan shirin namu na daga bakin mai ita. Watau yau kuma, Allah ya kawo mu a wannan fili tare da Alhaji Dan’anace. To idan na ce dai Alhaji Dan’anace, kusan duk masu saurarenmu sun san ko shi wane ne. Alhaji ɗan’anace dai, shahararre ne ƙwarai game…
Read More