06
Aug
“Babu wani abu da nake yi da nake so da ya wuce karatu da rubutu” Daga ABBA ABUBAKAR YAKUBU Marubuciya Na’ima Sulaiman Daƙayyawa ba ɓoyayyiya ba ce tsakanin matasan marubutan Hausa a Jihar Jigawa. Ta fito ne daga ƙaramar Hukumar Kaugama. Tana da gogewa a harshen Larabci da Hausa, inda yanzu haka take karatun digirinta na biyu a Jami'ar Sule Lamiɗo dake Kafin Hausa. Marubuciya ce da ta bambanta da sauran marubutan adabi, saboda ita ta fi mayar da hankali ne kan muhimman abubuwa na tarihi ko al'adu. Akasari rubuce-rubucen da ta yi sun shafi zamantankewar al'umma ne da tarihinsu.…
