Adabi

Dambe wasar maza, kowwayyi hankali ya barka: Waiwaye kan tarihin kiɗan dambe na Dan’anace (4)

Dambe wasar maza, kowwayyi hankali ya barka: Waiwaye kan tarihin kiɗan dambe na Dan’anace (4)

Daga IBRAHIM MUHAMMAD  (Danmadamin Birnin Magaji) Manazarta: Bunza, A. (2008) Gadon Feɗe Al’ada, Tiwal Nigerian Limited Lagos Dangambo, A. (2008) Rabe-Raben Adabin Hausa / Sabon Tsari, Amana Publishers, Kano Gusau, S. (1996) Makaɗa da Mawaƙan Hausa, Fisbas Media Serɓices, Kaduna Gusau, S. M. (1995) Dabarun Nazarin Adabin Hausa Fisbas Media Serɓices, Kaduna  Gusau, S. M. (2003) Jagoran Nazarin Waƙar Baka Benchmark Publishers Limited, Kano Gusau, S. M. (2009) Diwanin Waƙoƙin Baka: Zaɓaɓɓun Matanonin Waƙoƙin Baka Na Hausa. Century Research and Publishing Company Limited, Kano. Gusau, S. M. (2011) Tarihi da Hanyar Nazarin Waƙar Baka Bahaushiya. A Cikin Waƙoƙin Baka Na…
Read More
Bayan ƙungiyar Mace Mutum ba a samu ƙungiyar marubuta mata zalla ba sai yanzu – Shugabar WOW 

Bayan ƙungiyar Mace Mutum ba a samu ƙungiyar marubuta mata zalla ba sai yanzu – Shugabar WOW 

Don kawo sauyi a harkar rubutu musamman wanda ya shafi mata muka kafa ƙungiyar WOW" Daga ABBA ABUBAKAR YAKUBU  Fiye da shekara guda kenan da kafa ƙungiyar marubuta ta mata zalla, wacce ake kira da Women of Words Writers Association, mai laƙabi da WOW, kuma kawo yanzu ƙungiyar ta samu cigaba sosai, da ƙaruwar mambobi, waɗanda suke ba a Nijeriya kaɗai ba har da wasu ƙasashen waje. Yadda shugabannin wannan ƙungiya suka samu nasarar haɗo kan marubuta mata na onlayin da masu ɗab'i abin a yaba ne sosai. Sai kuma ga wani abin ƙayatarwa da ƙungiyar ta ɓullo da shi…
Read More
Dambe wasar maza, kowwayyi hankali ya barka: Waiwaye kan tarihin kiɗan dambe na Dan’anace (3)

Dambe wasar maza, kowwayyi hankali ya barka: Waiwaye kan tarihin kiɗan dambe na Dan’anace (3)

Daga IBRAHIM MUHAMMAD  (Danmadamin Birnin Magaji) Waƙoƙin jama'a: Waƙar Sani Kangiwa 1937-2010 (73) Sunan wanda aka yi ma waƙa Alhaji Sani Adamu ɗanbaba Kangiwa Turakin Kebbi / Argungu Shekarar da aka yi waƙa 1978 Muhallin Waƙa  ƙofar Tsohon Gidan Alhaji Sani Kangiwa da ke Sakkwato Saƙon Mawaƙi/Waƙa Yabo da Kambamawa Waƙar Zubairu ƙofar Rini 1940-1993 (53) Sunan wanda aka yi ma waƙa Alhaji Zubairu Tela ɗanmalikin Sakkwato Shekarar da aka yi waƙa 1976 Muhallin Waƙa  ƙofar Gidan Alhaji Zubairu Tela ƙofar Rini Sakkwato Saƙon Mawaƙi/Waƙa ƙauna da Soyayya  Waƙar Aliyu Layi 1934-2002 (68) Sunan wanda aka yi ma waƙa Alhaji…
Read More
Sharhin littafin ‘Sanin Asali Shine Farin Cikin Rayuwa Da Aminci’

Sharhin littafin ‘Sanin Asali Shine Farin Cikin Rayuwa Da Aminci’

Daga ABBA ABUBAKAR YAKUBU  Sunan littafi: Sanin Asali Shine Farin Cikin Rayuwa Da Aminci Mawallafi: Sheikh Abdulƙadir Na'Annabi Mu'azu Shekarar bugawa: 2026 Yawan shafi: 80 Mai sharhi: Abba Abubakar Yakubu Wane ne Sheikh Na'Annabi Mu'azu? Sheikh Abdulƙadir Na'Annabi Mu'azu wani fitaccen malamin addinin Musulunci ne da ke zaune a Jos, Jihar Filato. Allah Ya yi wa wannan malami baiwar sanin ilimin luggar Larabci da Balagha. Sannan malamin gwani ne wajen rubuta waƙoƙin Larabci da na Hausa, masu ƙunshe da darussa iri-iri. Ya kuma rubuta wasan kwaikwayo na Larabci da suka shafi tarihin Musulunci, da wasu fitattun malaman Musulunci. Sanin Asali…
Read More
An ƙalubalanci marubuta kan kula da haƙƙoƙin addini da al’ada a taron marubutan Jos

An ƙalubalanci marubuta kan kula da haƙƙoƙin addini da al’ada a taron marubutan Jos

Daga HABU DAN SARKI Jos Marubuta, manazarta da masu sha'awar rubuce-rubuce cikin harshen Hausa sun gudanar da wani taron ƙara wa juna sani wanda ƙungiyar marubutan Hausa ta Jos Writers Club ta shirya, domin ƙara wayar da kan mambobinta game da yadda za su inganta rubutun su.  A yayin wannan taro wanda aka gudanar a Cibiyar Nazarin Harkokin Sadarwa ta Hamzury Innoɓation Hub dake cikin garin Jos, an tattauna kan yadda marubuci zai isar da saƙon da ke ƙunshe a cikin labarinsa ga mai karatu, wanda shugaban ƙungiyar Abba Abubakar Yakubu ya gabatar, da kuma yadda marubuci zai yi amfani…
Read More
Jaridar New York Times ta bankaɗo yadda mata Hausawa masu rubutun batsa ke bajekolin su

Jaridar New York Times ta bankaɗo yadda mata Hausawa masu rubutun batsa ke bajekolin su

Daga ABBA ABUBAKAR YAKUBU Jos  Wata muhawara ta kaure a zaurukan sada zumunta tsakanin wasu ƴan Nijeriya, musamman ƴan kudancin ƙasar nan, waɗanda ke bayyana ra’ayoyinsu game da wani rahoto na musamman da wata jaridar Turanci ta ƙasar Amurka da ake kira The New York Times ta wallafa, wanda ke bayyana yadda wasu mata ƴan Arewacin Nijeriya suke cin karen su babu babbaka a manhajar WhatsApp ta hanyar sayar da littattafansu masu ɗauke da rubutun batsa. Wata ƴar jarida mai suna Ruth Maclean da taimakon abokin aikinta ɗan Nijeriya Isma'il Auwal sun gudanar da wani bincike game da zaurukan marubuta…
Read More
Dambe wasan maza, kowwayyi hankali ya barka: Waiwaye kan tarihin kiɗan dambe na Dan’anace (1)

Dambe wasan maza, kowwayyi hankali ya barka: Waiwaye kan tarihin kiɗan dambe na Dan’anace (1)

"Waƙa adabi ce, shi kuma adabi al’ada ne" Daga IBRAHIM MUHAMMAD  (Danmadamin Birnin Magaji) 0.0 Shimfiɗa Hausawa musamman mazauna karkara (ƙauyuka) suna wanzar da al’adu da yawa masu sha’awa da adana tarihin wannan al’umma. Waɗannan al’adun su ne taskokin da suka adana tarihinmu. Kuma waɗannan al’adu su ne suka samar da adabimmu. Wajen wanzar da al’adun aure ake samar da waƙoƙin aure. Wajen wanzar da wasanni ake gwada yin salailan maganganun hikima da gwada zalaƙar harshe. A nan salon magana da adon magana da karin magana ke tasowa. A nazarin tarihi da rayuwar wannan bawan Allah an ci karo da…
Read More
Ina son ko bayan raina a rinƙa tunawa da saƙonnin da na isar – Hauwa Shehu

Ina son ko bayan raina a rinƙa tunawa da saƙonnin da na isar – Hauwa Shehu

Daga MUKHTAR YAKUBU  Hauwa Shehu tana ɗaya daga cikin marubuta ƙirƙirarren labarin da a yanzu suke sahun gaba musamman dai a soshiyal midiya. Ta yi rubutu masu yawa da waɗanda aka buga a littafi da kuma na soshiyal midiya. Wannan ya ba ta damar shiga gasanni da dama na ƙirƙirarren labari. Ita ce ta zo ta uku a gasar marubuta ta Hukumar tace finafinai da aka gudanar a shekara ta 2024 da sauran gasar da ake yi ta marubuta. Domin jin ta bakinta, mun tattauna da ita domin jin yadda ta fara rubutun da irin damar da ta samu a…
Read More
Danmadamin Birnin Magaji: Ba don ku ba da ruwa ya ci tarihin adabin baka 

Danmadamin Birnin Magaji: Ba don ku ba da ruwa ya ci tarihin adabin baka 

Daga NASIR WADA KHALIL PhD Wato Mai Girma Alhaji Ibrahim Muhammad ɗanmadamin Birnin Magaji ya wuce a ce masa Malamin Adabi sai dai ko Jami’ar Adabi. Duk inda aka gudanar da bincike akan kiɗa, waƙa ko tarihi daga Arewacin Najeriya zuwa Kudancin Niger sai an samo shi taron zai cika.  Baya mantuwa na shekarar faruwar abu ko sunan muhalli ko jerin yadda abu ya faru sannan kuma baya kiwar rubutu, komai yana ba shi haƙƙinsa.  Ya taimaka wajen buɗe sabon shafi na yadda ake kiran makada ta hanyar jingina  nasabarsu da garinsu misali Salihu Jankidi Rawayya, Musa Dankwairo Maradun, Muhammadu…
Read More
Sai da na jingine rubutana don kula da ƙungiyar marubuta  – Zainab Abdullahi

Sai da na jingine rubutana don kula da ƙungiyar marubuta  – Zainab Abdullahi

"Ya kamata marubuta su tabbatar sun yi amfani da basirarsu wurin ciyar da Musulunci gaba"  Daga ABBA ABUBAKAR YAKUBU  Ci gaba daga makon jiya. A kowacce shekara a lokaci irin wannan na Ramadan, musulmi a ko'ina a duniya na shagaltuwa da ayyukan ibada da neman kusanci da Allah, marubuta adabin Hausa su ma sukan jingine ayyukan rubuce-rubuce na nishaɗi da faɗakarwa da suke yi, zuwa ga tilawar Alƙur'ani, da faɗakarwa kan al'amuran addini, da koyar da girke-girke ga mata. A irin wannan lokaci mambobin ƙungiyar marubuta ta Jajirtattu Writers Association suna ware tsawon watan Ramadan don gudanar da shirye-shirye da…
Read More