Adabi

Ƙagaggen rubutu tamkar ɗa ne wajen mahaifinsa Adabi, shi ko adabi daji ne ba a yi masa ƙyaure- Khalid Imam

Ƙagaggen rubutu tamkar ɗa ne wajen mahaifinsa Adabi, shi ko adabi daji ne ba a yi masa ƙyaure- Khalid Imam

Waka saƙa ta ake yi kamar tabarmar kaba, shi kuma zube gina shi ake kamar yadda ake gida - Khalid Daga AISHA ASAS Shahararre kuma sanannen marubuci da ake alfahari da shi a duniyar Adabin Hausa Khalid Imam, ya samu damar amsa gayyatar jaridar Manhaja inda masu karatu za su ji cikaken tarihi tare da nasarorin da ya samu a duniyar rubutu. An dai ce waƙa a bakin mai ita za ta fi zaƙi, ku biyo mu don jin wane ne Khalid Imam: Masu karatu za su so jin tarihin ka.Suna na Khalid lmam. An haife ni a shekarar 1973…
Read More
Marubuci tamkar wata mikiya ce a cikin al’umma – Lantana Ja’afar

Marubuci tamkar wata mikiya ce a cikin al’umma – Lantana Ja’afar

*Ni ce mace ta farko da ta fara lashe gasar 'Gusau Institute'- Lantana Daga AISHA ASAS A wannan makon jaridar Manhaja ta tattauna da Lantana Ja'afar, mace ta farko da ta taɓa cin gasar rubutun labarai ta cibiyar 'Gusau Institute' da suke shiryawa duk shekara. A wannan hirar masu karatu za su ji yadda Lantana ta fara rubutu da kuma ƙalubalen da ta fuskanta a harkar rubutun tare da wasu batutuwa da idan ku ka biyo mu za ku ji su: Mu fara da jin tarihin ki.Assalamu alaikum. Suna na Lantana Ja'afar, an haife ni a shekarar 1988 a cikin…
Read More
Duk littafin da na rubuta ba ƙagaggen labari ba ne ya faru da gaske – Fatima Ibrahim Garba Ɗanborno

Duk littafin da na rubuta ba ƙagaggen labari ba ne ya faru da gaske – Fatima Ibrahim Garba Ɗanborno

*Zaluncin 'yan kasuwa ne ya durƙusar da marubutan mu - Fatima DAGA AISHA ASAS Fatima Garba Ɗanborno ba za a kira ta ɓoyayya ba musamman a wajen ma'abota karance-karancen littafan Hausa, domin ta yi fice wajen fitar da littattafai masu tarin faɗakarwa gami da ilimintarwa da kuma nuni cikin nishaɗi. Shi ya sa a wannan makon Jaridar Manhaja ta zagaya don zaƙulo wa masu karatu ita don jin wace ce ita? Me ya kai ta ga fara rubutu da shiga harkokin marubuta tsundum? Tare kuma da jin irin nasarori da faɗi-tashin da ta yi kafin ta zama cikakkiyar marubuciya? Duk…
Read More
Gudunmawar harshe da al’ada ga bunƙasa tattalin arziƙi da zaman lafiya (3)

Gudunmawar harshe da al’ada ga bunƙasa tattalin arziƙi da zaman lafiya (3)

Daga FARFESA SALISU AHMAD YAKASAI Mafi kyawun fahimta ita ce abu ya zama da harshen mutum ake yinsa, idan ba haka ba to wasu abubuwa za su shige duhu. Tun kafin zuwan Turawa, a ƙasar Hausa ana amfani da shari’ar Musulunci ne. Wannan tsari na sharia a cikin Larabci yake, wanda ba kowa da kowa ya iya fahimta ba. Don haka da wuya jama’a su san kanta sosai da sosai, musamman ma idan wata matsala ta taso. Da Bature ya zo, shi ma dai ba ta sake zani ba. Ita tasa shariar a cikin Turanci take, ko haifaffen harshen ma…
Read More
Na zama marubuci tun a ranar da na fara iya karatu da rubutu – Abul-Waraƙat

Na zama marubuci tun a ranar da na fara iya karatu da rubutu – Abul-Waraƙat

A yau wannan fili ya yi babban kamu inda ya karɓi baƙuncin fasihi kuma haziƙin marubuci kuma mawaƙi, wato Binyaminu Zakariya, wanda saboda hazaƙar sa da basirar sa ake yi masa laƙabi da Abulwaraƙat, wato baban takarda. Binyamin Zakariyya ya bayyana cewa ya fara rubutu ne tun daga lokacin da ya fara iya rubutu, wato ya na ƙaramin yaro. Haziƙin ya ƙware wajen rubuta waƙa da rubutun hikaya a harshen Larabci da Hausa. Ku biyo mu don jin yadda tattaunawar mu da shi ta kasance. Daga IBRAHIM HAMISU Kano Masu karatun mu za su so sanin taƙaitaccen tarihin ka.Suna na…
Read More
Adabi rayayyar kalma ce wadda ba ta mutuwa – Hauwa Lawal Maiturare

Adabi rayayyar kalma ce wadda ba ta mutuwa – Hauwa Lawal Maiturare

Hauwa Lawal Maiturare ba ta da buƙatar doguwar gabatarwa a duniyar rubutu. Sananniya ce ga waɗanda su ka fara karance-karancen littattafan Hausa wuraren 1998. Ta kasance cikin jerin marubuta da su ka shigo duniyar rubutu da ƙafar dama. Masu karatu za su tuna Maiturare da littafin ta na ‘Haske Maganin Duhu’ ko ‘Gobarar Gemu’. Wannan jarida mai farin jini ta yi nasarar kawo maku ita a wannan mako. Ku biyo mu don jin yadda tataunawar ta kasance. Daga AISHA ASAS a Abuja Mu fara da jin cikakken tarihin ki.Suna na Hauwa Lawal Maiturare wacce aka fi sani da Ƙamshi. Ni…
Read More
Gudunmawar harshe da al’ada ga bunƙasa tattalin arziƙi da zaman lafiya (2)

Gudunmawar harshe da al’ada ga bunƙasa tattalin arziƙi da zaman lafiya (2)

Daga FARFESA SALISU AHMAD YAKASAI Harshe ba shi da alaƙa da mutum, wato ba wai haihuwar mutum a awuri ke sa ya ji harshen su mutanen wurin ba, sai dai idan ya tashi da amfani da shi. Saboda haka, duk wanda ya tashi da wani harshe, to lallai harshen zai koya. Jinin mutum ba ya da alaƙa da harshensa, domin sai a samu Baturen Ingila yana Larabci, ko kuwa Bafaranshe yana Hausa. Kenan furucin mutum ba ya nuna qabilarsa, domin furuci ba manunin ƙabila ne ba sai dai idan mutum ya faɗi ƙabilarsa, tun da duk inda mutum ya tashi,…
Read More
Ba a koyon rubutu, ba a sayen sa da kuɗi – Jamila Rijiyar Lemu

Ba a koyon rubutu, ba a sayen sa da kuɗi – Jamila Rijiyar Lemu

Jamila Abdullahi Rijiyar Lemu ƙwararriyar marubuciya ce da ta daɗe tana jan zaren ta a duniyar rubuta littattafan Hausa.  Kuma ta yi zarrar zuwa ta biyu a gasar da sashen Hausa na BBC ke shirya wa mata zalla a duk shekara, wato ‘Hikayata,’ a shekarar 2019. A wannan tattaunawar da wakiliyar Manhaja, za ku ji yadda marubuciyar ta sha gwagwarmaya da faɗi-tashi a harkar rubutu. Daga AISHA ASS Mu fara da jin tarihin ki a taƙaice.Bismillahir Rahmanir Rahim! Suna na Jamila Abdullahi Rijiyar Lemu. An haife ni a shekara ta 1980. Na yi karatu tun daga firamare zuwa Jami’ar Bayero…
Read More
Littafin koyon salatin Annabi cikin sauƙi

Littafin koyon salatin Annabi cikin sauƙi

Daga IBRAHIM SHEME LITTAFI: Salatin Annabi Muhammadu Sallallahu Alaihi Wa Sallam: Matsayinsa Da Fa'idojinsa Da SigoginsaMARUBUCIYA: Hajiya Hajara Muhammad KabirKANFANIN WALLAFA: Goshi Publishers Limited, Kano.SHEKARA: 2018SHAFUKA: 175MAI SHARHI: Ibrahim Sheme TUN a cikin shekarar 2018 ka buga wannan littafin mai suna "Salatin Annabi Muhammadu Sallallahu Alaihi Wa Sallam: Matsayinsa Da Fa'idojinsa Da Sigoginsa", amma waɗansu dalilai su ka sa bai fito ba sai a bana. Marubuciyar littafin, Hajiya Hajara Muhammad Kabir, ta rubuta wasu littattafan a baya, amma wannan shi ne ta yi kacokam kan wani abu da ya shafi addini kai-tsaye. Ta ɗau tsawon shekaru shida ta na bincike a…
Read More
Babban buri na kafin in bar duniya…, inji Bilkisu

Babban buri na kafin in bar duniya…, inji Bilkisu

Daga AISHA ASAS Waɗanda suka daɗe da fara karance-karancen littattafan Adabin Kasuwar Kano tun wuraren 1993 ba shakka zan iya cewa sun sha cin karo da littattafan Hajiya Bilkisu Salisu Ahmed Funtua, wadda ake kira Aunty Bilki Funtua, domin ta kasance a sahun farko kuma tauraruwar da littattafanta ke ja a wancan lokacin. Saboda haka a tashin farko muka samu nasarar shigo muku da ita cikin wannan fili don jin wace ce ita, mene ne kuma burinta a halin yanzu sakamakon rashin jin duriyar littattafan ta a kasuwa na dogon lokaci. Ga dai yadda hirar tamu ta kasance: Masu karatu…
Read More