31
Jul
Daga MAHDI MUSA MUHAMMAD Gwamnatin Amurka ta sanar da cewa daga ranar 1 ga Agustan 2026, za ta dakatar da ayyukan karɓa da sarrafa buƙatun bizar yau da kullum a Ofishin Jakadancinta da ke Abuja, tare da wasu ofisoshin jakadanci guda 24 da ke faɗin nahiyar Afirka. A cewar Ma’aikatar Harkokin Wajen Amurka, matakin na daga cikin wani sabon shiri na sake fasalin ayyukan ofisoshin jakadancinta a ƙasashen waje, domin tattara ayyukan sarrafa biza a wasu cibiyoyi na yankuna. Hakan, a cewarta, zai taimaka wajen ƙarfafa tsaron ƙasa, rage kuɗaɗen gudanarwa, tare da tabbatar da daidaito wajen tantance masu neman…
