Kasashen Waje

Amurka za ta dakatar da ayyukan bada biza a Abuja daga watan Agusta

Amurka za ta dakatar da ayyukan bada biza a Abuja daga watan Agusta

Daga MAHDI MUSA MUHAMMAD Gwamnatin Amurka ta sanar da cewa daga ranar 1 ga Agustan 2026, za ta dakatar da ayyukan karɓa da sarrafa buƙatun bizar yau da kullum a Ofishin Jakadancinta da ke Abuja, tare da wasu ofisoshin jakadanci guda 24 da ke faɗin nahiyar Afirka. A cewar Ma’aikatar Harkokin Wajen Amurka, matakin na daga cikin wani sabon shiri na sake fasalin ayyukan ofisoshin jakadancinta a ƙasashen waje, domin tattara ayyukan sarrafa biza a wasu cibiyoyi na yankuna. Hakan, a cewarta, zai taimaka wajen ƙarfafa tsaron ƙasa, rage kuɗaɗen gudanarwa, tare da tabbatar da daidaito wajen tantance masu neman…
Read More
Houthi ta sauya akalar safarar man Saudiyya yayin da yaƙin Amurka da Iran ke ƙara tsananta

Houthi ta sauya akalar safarar man Saudiyya yayin da yaƙin Amurka da Iran ke ƙara tsananta

Rikicin da ke tsakanin Amurka da Iran ya sake ɗaukar sabon salo bayan ƙungiyar Houthi ta Yemen ta buɗe wani sabon fagen matsin lamba ta hanyar kakaba takunkumin ruwa kan Saudiyya, matakin da ya fara girgiza harkokin safarar mai da zirga-zirgar jiragen ruwa a yankin Gabas ta Tsakiya. Sabon matakin ya tilasta wasu manyan jiragen dakon danyen man Saudiyya guda biyu da suka nufi kasuwannin Chana da Indiya sauya alkibla a Tekun Bahar Maliya, domin kauce wa mashigin Bab el-Mandeb bayan Houthi ta yi barazanar kai hari kan duk wani jirgin da zai dauki ko sauke man Saudiyya. Masana harkokin…
Read More
Cutar Ebola: Hukumar CDC ta Afirka ta buƙaci Amurka ta janye takunkumin tafiye-tafiye kan Uganda

Cutar Ebola: Hukumar CDC ta Afirka ta buƙaci Amurka ta janye takunkumin tafiye-tafiye kan Uganda

Babban daraktan Hukumar Yaki da Cututtuka ta Afirka (Africa CDC), Jean Kaseya, ya buƙaci gwamnatin Amurka da ta janye takunkumin tafiye-tafiye da ta kakaɓa wa Uganda sakamakon ɓarkewar cutar Ebola, yana mai cewa babu wani dalili da zai sa a ci gaba da ɗaukar irin wannan mataki bayan ƙasar ta shafe kusan wata guda ba tare da samun sabon mai ɗauke da cutar ba. Kaseya ya bayyana hakan ne a wani taro da aka gudanar a Accra, babban birnin Ghana, inda ya ce ya aike wa Sakataren Lafiya na Amurka, Robert F. Kennedy Jr., wasiƙa yana rokon a soke takunkumin.…
Read More
Mutane 144 sun mutu a tekun Mauritania yayin ƙoƙarin tsallakawa Turai

Mutane 144 sun mutu a tekun Mauritania yayin ƙoƙarin tsallakawa Turai

Hukumar Kula da 'Yan Gudun Hijira ta Majalisar Dinkin Duniya (UNHCR) ta ce akalla mutum 144 ne aka tabbatar sun mutu ko kuma suka ɓace a gabar tekun Mauritania yayin da suke ƙoƙarin tsallakawa zuwa Turai ta ruwa. A cewar hukumar, adadin ya biyo bayan wasu ayyukan ceto uku da aka gudanar tsakanin 14 zuwa 18 ga Yuli, inda aka kuɓutar da daruruwan mutane daga jiragen da suka shiga mawuyacin hali a teku. Mummunan haɗarin ya fi shafar wani jirgin ruwa da ya tashi daga Bufaloto a ƙasar Gambia. Jirgin ya shafe kwanaki 25 yana yawo a teku kafin a…
Read More
Andy Burnham ya kama aiki a matsayin firaministan Birtaniya

Andy Burnham ya kama aiki a matsayin firaministan Birtaniya

Andy Burnham ya zama Firaminista na shida da ya shiga gidan gwamnati da ke layin Downing a ranar Litinin, tun daga shekarar 2016, bayan da Sarkin Birtaniya, Charles na uku, ya ba shi amanar kafa sabuwar gwamnati. Kamfanin dillancin labarai na AFP, kamar yadda Channels TV ya ruwaito, ya ce Burnham mai shekaru 56 zai maye gurbin Keir Starmer, wanda ya yi murabus daga mukamin Firaminista da shugaban Jam’iyyar Labour bayan fuskantar suka da jerin matsalolin siyasa. Ana sa ran Burnham zai gabatar da jawabinsa na farko a gaban gidan gwamnatin Downing Street bayan Keir Starmer ya yi bankwana da…
Read More
Amurka za ta fara karɓar kuɗin amfani da mashigar Hormuz – Trump

Amurka za ta fara karɓar kuɗin amfani da mashigar Hormuz – Trump

Sabuwar sanarwar da shugaban Amurka, Donald Trump, ya yi na cewa ƙasarsa za ta fara karɓar kuɗin amfani da mashigar ruwan Hormuz ta sake tayar da muhawara kan ko wata ƙasa na da ikon kakaɓa irin wannan haraji a ɗaya daga cikin muhimman hanyoyin ruwa na duniya. Trump ya bayyana cewa idan yarjejeniyar tsagaita wuta da Iran ta rushe, Amurka za ta karɓi kashi 20 cikin ɗari na dukkan kayayyakin da za su ratsa mashigar Hormuz, yana mai cewa hakan zai zama diyya ga rawar da Amurka ke takawa wajen kare tsaron mashigar. Sanarwar ta zo ne bayan yarjejeniyar tsagaita…
Read More
Motocin haya masu amfani da lantarki sun taimaka wa Chana rage tasirin rikicin Hormuz

Motocin haya masu amfani da lantarki sun taimaka wa Chana rage tasirin rikicin Hormuz

Yayin da rikicin mashigar ruwan Hormuz ke haddasa tashin farashin danyen mai da girgiza kasuwannin makamashi na duniya, ƙasar Chana ta samu wata muhimmiyar kariya daga irin wannan matsin lamba ta hanyar faɗaɗa amfani da motocin haya masu amfani da lantarki. Rahotanni sun nuna cewa a faɗin biranen Chana, yawan fasinjojin da ke amfani da tasi da motocin haya ta manhajojin zamani na ci gaba da ƙaruwa, duk kuwa da tashin farashin man fetur. Bayanan gwamnatin ƙasar sun nuna cewa a watan Mayu kadai, an yi sama da tafiye-tafiye biliyan 3.05 ta hanyar motocin haya. Wannan adadi ya ƙaru da…
Read More
Yawancin mutanen Amurka suna rayuwar hannu-baka-hannu-ƙwarya, inji mazaunin ƙasar

Yawancin mutanen Amurka suna rayuwar hannu-baka-hannu-ƙwarya, inji mazaunin ƙasar

Daga MAHDI MUSA MUHAMMAD Wani ɗan kasuwar Nijeriya kuma mai harkar bunƙasa gidaje da ke zaune a Amurka, Femi Rogers, ya yi kira ga matasan Nijeriya da ke kallon ƙaura zuwa ƙasashen waje a matsayin mafita ta samun sauƙin rayuwa da su sake nazari, yana mai cewa rayuwa a Amurka ba ta da sauƙin kuɗi kamar yadda mutane da dama ke zato. Rogers ya bayyana hakan ne yayin wata tattaunawa a shirin Frankly Business Podcast, inda ya ce tsadar gidaje, haraji, kuɗin wutar lantarki, ruwa da sauran kuɗaɗen rayuwa na sanya mutane da dama a Amurka rayuwa daga abin da…
Read More
NATO ta zaɓi jiragen leƙen asirin Saab na Sweden, ta yi watsi da tayin Boeing na Amurka

NATO ta zaɓi jiragen leƙen asirin Saab na Sweden, ta yi watsi da tayin Boeing na Amurka

Matakin ya zo ne yayin da Trump ke ci gaba da matsa wa ƙawayen NATO su ƙara kashe kuɗi kan tsaro da kuma sayen makaman Amurka. ƙungiyar tsaron ƙasashen Arewacin Tekun Atlantika (NATO) ta sanar da wani shiri na kusan dala biliyan 4.5 domin sayen sabbin jiragen leƙen asiri da gargaɗin barazana na GlobalEye, waɗanda kamfanin Saab na ƙasar Sweden ta ƙera. Matakin ya nuna cewa ƙungiyar ta fifita fasahar Sweden kan ta kamfanin Boeing na Amurka wajen maye gurbin tsofaffin jiragen AWACS da suka yi shekaru da dama suna aiki. Sanarwar ta fito ne a yayin taron ƙasashen NATO…
Read More
Trump ya soki Firaministar Italiya kan rikicin Iran, duk da cewa ya ce “mutumiyar kirki ce”

Trump ya soki Firaministar Italiya kan rikicin Iran, duk da cewa ya ce “mutumiyar kirki ce”

Gwamnatin Italiya ta zaɓi yin shiru domin kare dangantaka da Amurka, yayin da ake sa ran shugabannin biyu za su haɗu a taron NATO. Sabuwar takun-saƙa ta ɓarke tsakanin Shugaban Amurka, Donald Trump, da Firaministar Italiya, Giorgia Meloni, bayan shugaban na Amurka ya zargi Meloni da ƙin ba Washington goyon baya a rikicin da ake yi da Iran. Duk da cewa Trump ya bayyana Meloni a matsayin "mutumiyar kirki", ya ce rashin amincewarta ta shiga cikin ƙoƙarin da Amurka ke yi game da Iran ya janyo tsaiko a kyakkyawar dangantakar da ke tsakaninsu. Trump ya yi waɗannan kalamai ne yayin…
Read More