26
Apr
Ƙungiyoyin fararen hula da jam’iyyun siyasa a Mali sun buƙaci kotun ƙoli kan ta umarci gwamnatin sojin ƙasar da ta dakatar da haramcin da ta yi game da gudanar da harkokin siyasa. A wata sanarwa da suka fitar, ƙungiyoyin fararen hular da jam’iyyun siyasa da ke adawa da umarnin Sojojin, sun yi ƙorafi ga babbar kotun ƙasar ta Mali, suna neman a soke hukuncin da suke ganin take haƙƙin ɗan adam ne. Tun a shekarar 2021 ne sojoji a Mali suka yi juyin mulki karo na biyu, inda suka yi alƙawarin gudanar da zaɓe a watan Fabrairun da ya gabata…