07
Mar
Amurka ta sanar da sanya ƙungiyar 'yan tawayen Houthi na Yemen a matsayin 'yan ta’adda, matakin da ake ganin baya rasa nasaba da yadda ƙungiyar wadda a baya aka sani da Ansarullah ta yi uwa da makarɓiya wajen tsunduma rikicin Falasɗinawa da Isra’ila. Sanarwar ma’aikatar harkokin wajen Amurkan ta ce ayyukan 'yan tawayen na Houthi na barazana ga rayuwar Amurkawan da ke zaune a yankin gabas ta tsakiya. Sakataren harkokin wajen Amurka Marco Rubio ya bayyana cewa Amurka za ta lafta takunkumi kan duk wata ƙasa ko ƙungiya ko kuma ɗaiɗaikun mutane da suka tallafa 'yan tawayen na Houthi ta…