18
Sep
Gwamnatin Ƙasar Congo Brazzaville ƙarƙashin jagorancin Shugaba Denis Sassou Nguesso ta ƙaryata yunƙurin juyin mulki a ƙasar. Ta bayyana haka ne cikin wani saƙo da ta wallafa a Tiwita a ranar Lahadi. Kafafen yaɗa labarai da dama sun ruwaito ranar Lahadi cewar sojoji ana yunƙurin kifar da gwamnatin ƙasar a yayin da Shugaban Ƙasar yi tafiya. Saƙon X (Tiwita) da Ministan Sadarwa da Yaɗa Labarai na Ƙasar, Thierry Moungalla, ya wallafa a shafinsa ya ƙaryata haka. “Gwamanati ta ƙaryata rahoton. Muna sake jaddada wa al'umma zaman lumanar da ke akwai a ƙasar, muna kira ga jama'a kowa ya ci gaba…