Kasashen Waje

Amurka ta ayyana ‘yan tawayen Houthi na Yemen a matsayin ‘yan ta’adda

Amurka ta ayyana ‘yan tawayen Houthi na Yemen a matsayin ‘yan ta’adda

Amurka ta sanar da sanya ƙungiyar 'yan tawayen Houthi na Yemen a matsayin 'yan ta’adda, matakin da ake ganin baya rasa nasaba da yadda ƙungiyar wadda a baya aka sani da Ansarullah ta yi uwa da makarɓiya wajen tsunduma rikicin Falasɗinawa da Isra’ila. Sanarwar ma’aikatar harkokin wajen Amurkan ta ce ayyukan 'yan tawayen na Houthi na barazana ga rayuwar Amurkawan da ke zaune a yankin gabas ta tsakiya. Sakataren harkokin wajen Amurka Marco Rubio ya bayyana cewa Amurka za ta lafta takunkumi kan duk wata ƙasa ko ƙungiya ko kuma ɗaiɗaikun mutane da suka tallafa 'yan tawayen na Houthi ta…
Read More
Zelensky ya amince Amurka ta jagoranci sulhunta su da Rasha – Trump

Zelensky ya amince Amurka ta jagoranci sulhunta su da Rasha – Trump

Shugaban Amurka Donald Trump ya ce takwaransa na Ukraine Volodymyr Zelensky, ya aike masa da wasiƙa inda ya ke sanar da shi aniyar Kyiv, ta ba da goyon baya don cimma yarjejeniyar zaman lafiya tsakaninta da Rasha, a ƙarƙashin jagorancin Amurka. A lokacin da shugaban na Amurka Donald Trump ke gabatar da jawabi a zauren majalisar dokokin ƙasar, ya ce, a wasiƙar da Zelensky ya aike masa, ya ce, Ukraine ta fi kowa buƙatar cimma yarjejeniyar zaman lafiyar. Wannan dai na zuwa ne sa’oi kaɗan bayan da Amurka, ta sanar da dakatar da bai wa Ukraine duk wani tallafin soji,…
Read More
Babu shaidar USAID na tallafa wa Boko Haram a Nijeriya – Jakadan Amurka

Babu shaidar USAID na tallafa wa Boko Haram a Nijeriya – Jakadan Amurka

*Amurka ta jaddada taimaka wa Nijeirya a yaƙar Boko Haram Daga MAHDI MUSA MUHAMMAD Jakadan Amurka a Nijeriya, Mista Richard Mills, ya yi watsi da zargin da ake yi wa Hukumar Raya ƙasashe ta Amurka (USAID) tana tallafa wa ƙungiyar ta'addancin Boko Haram ko wasu ƙungiyoyin ta’addanci. Mills wanda ya gana da mambobin aungiyar gwamnonin Nijeriya a Abuja ranar Laraba da daddare, ya ce babu wata shaida da ke tabbatar da zargin. Ya bayyana cewa babu wata ƙasa da ta yi Allah wadai da ta'addancin Boko Haram fiye da Amurka, yana mai tabbatar da cewa idan aka samu wata shaida,…
Read More
Karon farko Rasha da Amurka za su zaɓo wakilan da za su tattauna kan yaƙin Ukraine

Karon farko Rasha da Amurka za su zaɓo wakilan da za su tattauna kan yaƙin Ukraine

A karon farko, Amurka da Rasha sun cimma matsayar gaggauta zaɓar tawagogin jami’an da za su tattauna a kan hanyoyin da za a bi wajen kawo ƙarshen yaƙin Ukraine. An cimma matsayar ce yayin ganawar sakataren harkokin wajen Amurka Marco Rubio da ministan harkokin wajen Rasha Sergei Laɓroɓ a Saudiya, zaman da Ukraine da kuma EU ba su samu goron gayyatar halartarsa ba. Ganawar dai ita ce ta farko da aka yi tsakanin jami’an Amurka da Rasha, tun bayan ƙaddamar da mamayar Ukraine da shugaba Putin ya yi a farkon shekarar 2022. Buƙatar sake fasalin yarjeniyoyin tsaron Turai na daga…
Read More
Rikicin kuɗin Kirifto: Shugaban Argentina na fuskantar barazanar tsigewa

Rikicin kuɗin Kirifto: Shugaban Argentina na fuskantar barazanar tsigewa

Shugaban Argentina Javier Milei na fuskantar ƙarar kiraye-kirayen tsigewa da kuma matakin shari'a biyo bayan haɓakar rigima na cryptocurrency wanda ya haifar da asarar kuɗi mai yawa ga masu saka hannun jari. Milei ya wallafa a ɗ, wadda aka fi sani a baya da Twitter, a ranar Juma'a inda ya nuna amincewa da kudin $LIBRA, wanda ya bayyana a matsayin mafita da kuma hanyar tallafa wa ƙananan masu kasuwanci da kuma masu shirin farawa. Amincewarsa ta sa darajar kuɗin ta hauhawa, amma bayan da ya goge saƙon sa'o'i kacan bayan wallafa shi, farashinsa ya faɗi, inda hakan ya haɗiye kuɗaɗen…
Read More
‘Ƴan bindiga sun kashe fararen hula sama da 35 a Gabashin Congo

‘Ƴan bindiga sun kashe fararen hula sama da 35 a Gabashin Congo

Fararen hula fiye 35 ne wasu mayaƙan ƙungiyar CODECO suka kashe, a wani hari da suka kai wasu ƙauyuka da ke lardin Ituri na Jamhuriyar Dimokaraɗiyyar Congo a daren ranar Litinin. Basaraken ƙauyen Djugu, Jean ɓianney ya ce ƴan bindigar sun kai harin ne da misalin ƙarfe 8 na daren Litinin, inda suka kashe mutane tare kuma da ƙona gidaje. Ya ce izuwa safiyar Talatar, sun gano gawarwaki sama da 35, bayaga waɗanda suka samu raunuka da kuma asarar dukiyar da aka tabka. Shugaban wata ƙungiyar farar hula a yankin Jules Tsuba, ya ce izuwa safiyar Talata, sun gano gawarwakin…
Read More
Trump ya lafta harajin kashi 25 kan ƙarafan da ake shigarwa Amurka

Trump ya lafta harajin kashi 25 kan ƙarafan da ake shigarwa Amurka

Shugaban Amurka Donald Trump ya sanar da lafta harajin kashi 25 kan ƙarafai da samfolon ko kuma Alminium da ake shigarwa ƙasar daga ƙetare ba tare da cirewa ko kuma sauƙaƙawa kowacce ƙasa ba. Harajin na Trump kan ƙarafa da Alminium ko kuma Samfolon da ake shigarwa Amurka da zai fara aiki nan take, duk da cewa kai-tsaye shugaban Chana ya nufata da shi amma zai fi illa ga ƙasashen Canada da Brazil da kuma Meɗico waɗanda sune suka fi shigar da kayan cikin Washington. A jawabinsa bayan sanar da lafta harajin, Trump ya bayyana cewa wannan muhimmin lamari ne…
Read More
Falasɗinawa za su yi farin ciki da inda za mu kai su – Trump

Falasɗinawa za su yi farin ciki da inda za mu kai su – Trump

Shugaban Amurka Donald Trump ya sake jaddada aniyarsa ta karɓe Gaza da kuma kwashe Falasɗinawan da ke wurin zuwa ƙasashen Jordan da Masar tare da wasu ƙasashen Larabawa. Yayin ganawa da Sarki Abdallah na Jordan wanda ya ziyarce shi a Washington, Trump ya ce yana da yaƙinin cewar za su samu fili a ƙasashen Jordan da Masar inda za a kai Falasɗinawan da za a kwashe daga Gazar. Shugaban ya ce bayan kammala tattaunawar da suke yi za a samu wurin da za a aje Falasɗinawan da ke Gaza da za su zauna cikin farin ciki. Yayin tsokaci akan matsayin…
Read More
Hamas ta sako fursunonin Isra’ila uku a musayar Falasɗinawa 183

Hamas ta sako fursunonin Isra’ila uku a musayar Falasɗinawa 183

A ranar Asabar ne mayaƙan Hamas ta sako ƙarin wasu fursunonin Isra’ila guda uku akan musayar Palastinawa 183 da Isra’ila ta sako a matsayin wani ɓangare na yarjejeniyar tsagaita wuta a Gaza. An gudanar da waƙoƙi gabannin musayar a birnin Deir Al-Balah a safiyar Asabar da jami’an bada agaji na Red Cross da wasu ƴan Hamas suka jagoranta. Jami’an Red Cross ne suka gabatar da fursunoni ukun ga sojojin Isra’ila a yankin Kudancin ƙasar inda suke karɓar kulawar lafiya a matakin farko. Wata sanarwa da hukumomin tsaro na Isra’ila suka fitar, ta ce sun yi kira ga al’umma da su…
Read More
Ƙasar Rasha ta saki wani malami Ba’amurke da take tsare da shi

Ƙasar Rasha ta saki wani malami Ba’amurke da take tsare da shi

An sako wani malami Ba’amurke, wanda aka yanke wa hukunci bisa kuskure, kuma ake tsare da shi a Rasha, Marc Fogel, a wani abin da fadar White House ta bayyana a matsayin diflomasiyya da ka iya ciyar da tattaunawar kawo ƙarshen yaƙin Ukraine. Steve Witkoff, ɗan aike na musamman daga Shugaba Donald Trump, ya bar filin saukar jirage na Rasha tare da Fogel, wani malamin tarihi daga Pennsylɓania, kuma ana sa ran zai sake haɗuwa da iyalinsa a ƙarshen wannan rana. An kama Fogel a watan Agustan 2021 kuma yana zaman gidan yari na shekaru 14. Iyalinsa da magoya bayansa…
Read More