Kasashen Waje

Yawancin mutanen Amurka suna rayuwar hannu-baka-hannu-ƙwarya, inji mazaunin ƙasar

Yawancin mutanen Amurka suna rayuwar hannu-baka-hannu-ƙwarya, inji mazaunin ƙasar

Daga MAHDI MUSA MUHAMMAD Wani ɗan kasuwar Nijeriya kuma mai harkar bunƙasa gidaje da ke zaune a Amurka, Femi Rogers, ya yi kira ga matasan Nijeriya da ke kallon ƙaura zuwa ƙasashen waje a matsayin mafita ta samun sauƙin rayuwa da su sake nazari, yana mai cewa rayuwa a Amurka ba ta da sauƙin kuɗi kamar yadda mutane da dama ke zato. Rogers ya bayyana hakan ne yayin wata tattaunawa a shirin Frankly Business Podcast, inda ya ce tsadar gidaje, haraji, kuɗin wutar lantarki, ruwa da sauran kuɗaɗen rayuwa na sanya mutane da dama a Amurka rayuwa daga abin da…
Read More
NATO ta zaɓi jiragen leƙen asirin Saab na Sweden, ta yi watsi da tayin Boeing na Amurka

NATO ta zaɓi jiragen leƙen asirin Saab na Sweden, ta yi watsi da tayin Boeing na Amurka

Matakin ya zo ne yayin da Trump ke ci gaba da matsa wa ƙawayen NATO su ƙara kashe kuɗi kan tsaro da kuma sayen makaman Amurka. ƙungiyar tsaron ƙasashen Arewacin Tekun Atlantika (NATO) ta sanar da wani shiri na kusan dala biliyan 4.5 domin sayen sabbin jiragen leƙen asiri da gargaɗin barazana na GlobalEye, waɗanda kamfanin Saab na ƙasar Sweden ta ƙera. Matakin ya nuna cewa ƙungiyar ta fifita fasahar Sweden kan ta kamfanin Boeing na Amurka wajen maye gurbin tsofaffin jiragen AWACS da suka yi shekaru da dama suna aiki. Sanarwar ta fito ne a yayin taron ƙasashen NATO…
Read More
Trump ya soki Firaministar Italiya kan rikicin Iran, duk da cewa ya ce “mutumiyar kirki ce”

Trump ya soki Firaministar Italiya kan rikicin Iran, duk da cewa ya ce “mutumiyar kirki ce”

Gwamnatin Italiya ta zaɓi yin shiru domin kare dangantaka da Amurka, yayin da ake sa ran shugabannin biyu za su haɗu a taron NATO. Sabuwar takun-saƙa ta ɓarke tsakanin Shugaban Amurka, Donald Trump, da Firaministar Italiya, Giorgia Meloni, bayan shugaban na Amurka ya zargi Meloni da ƙin ba Washington goyon baya a rikicin da ake yi da Iran. Duk da cewa Trump ya bayyana Meloni a matsayin "mutumiyar kirki", ya ce rashin amincewarta ta shiga cikin ƙoƙarin da Amurka ke yi game da Iran ya janyo tsaiko a kyakkyawar dangantakar da ke tsakaninsu. Trump ya yi waɗannan kalamai ne yayin…
Read More
Ghana ta ɗage taron haɗin gwiwa da Afirka ta Kudu saboda hare-haren ƙyamar baƙi

Ghana ta ɗage taron haɗin gwiwa da Afirka ta Kudu saboda hare-haren ƙyamar baƙi

Gwamnatocin Ghana da Afirka ta Kudu sun ce dangantakarsu na nan daram duk da jinkirta taron haɗin gwiwa. Gwamnatin ƙasar Ghana ta sanar da ɗage taron haɗin gwiwa da aka shirya gudanarwa da Afirka ta Kudu a watan Agusta, saboda yadda hare-haren da ake kai wa baƙin haure a ƙasar ta Afirka ta Kudu suka ƙara ƙamari a cikin 'yan watannin nan. Mai magana da yawun gwamnatin Ghana, Feliɗ Kwakye Ofosu, ya bayyana cewa idan aka gudanar da taron a halin da ake ciki yanzu, tabbas batun hare-haren ƙyamar baƙi ne zai mamaye tattaunawar, maimakon muhimman batutuwan haɗin gwiwar da…
Read More
Kotun Koli ta Amurka ta yi fatali da yunƙurin Trump na taƙaita ‘yancin zama ɗan ƙasa ta haihuwa

Kotun Koli ta Amurka ta yi fatali da yunƙurin Trump na taƙaita ‘yancin zama ɗan ƙasa ta haihuwa

A wani hukunci da ake kallonsa a matsayin ɗaya daga cikin mafi muhimmanci a tarihin dokokin Amurka na baya-bayan nan, Kotun Kolin ƙasar ta yi watsi da ƙoƙarin Shugaba Donald Trump na takaita tsarin da ke bai wa duk wanda aka haifa a cikin ƙasar zama ɗan ƙasar Amurka kai tsaye, ba tare da la'akari da matsayin shige da ficen iyayensa ba. Hukuncin, wanda alƙalan kotun shida suka goyi baya yayin da uku suka nuna adawa da shi, ya zo ne a ranar ƙarshe ta wa'adin zaman kotun na wannan shekara, inda ya tabbatar da cewa tanadin Sashe na Bai…
Read More
Tashin hankali ya sake ɓarkewa a Afirka ta Kudu yayin da zanga-zangar ƙyamar baƙi ke ƙara ƙamari

Tashin hankali ya sake ɓarkewa a Afirka ta Kudu yayin da zanga-zangar ƙyamar baƙi ke ƙara ƙamari

Fargabar sake ɓarkewar rikicin kyamar baƙi ta mamaye sassa da dama na Afirka ta Kudu bayan dubban masu zanga-zanga sun mamaye titunan manyan biranen ƙasar ranar Talata, don nuna adawa da ci gaba da zaman baƙin haure ba bisa ƙa'ida ba. Zanga-zangar, wadda ƙungiyoyin masu adawa da shige da fice irin su March and March da Operation Dudula suka shirya, ta zo ne bayan cikar wa'adin da aka bai wa baƙin hauren da ba su da takardun zama su fice daga ƙasar. Lamarin ya haifar da tashin hankali a biranen Johannesburg, Pretoria, Durban da sauran yankuna da dama. Ko da…
Read More
Gobara ta yi ajalin aƙalla mutum biyar a ginin bene mai hawa 10 a Belgium

Gobara ta yi ajalin aƙalla mutum biyar a ginin bene mai hawa 10 a Belgium

Aƙalla mutum biyar ne suka rasa rayukansu bayan wata mummunar gobara ta tashi a wani katafaren ginin bene mai hawa goma da ke birnin Antwerp na ƙasar Belgium a safiyar Laraba, lamarin da ya jefa mazauna yankin cikin firgici wanda cikin ƙanƙanin lokaci aka fara gagarumin aikin ceto. 'Yan sandan Belgium sun tabbatar da faruwar lamarin, sai dai sun bayyana cewa har yanzu ba a iya tantance adadin mutanen da suka jikkata ko kuma gano musabbabin tashin gobarar ba. Tun da farko wasu kafafen yaɗa labarai na cikin gida sun rawaito cewa mutum shida ne suka mutu, bisa bayanan farko…
Read More
Cibiyar Yaɗa ilimin kafafen sada zumunta ta duniya ta ƙaddamar da shirin yaƙi da ƙyamar baƙi a Afirka 

Cibiyar Yaɗa ilimin kafafen sada zumunta ta duniya ta ƙaddamar da shirin yaƙi da ƙyamar baƙi a Afirka 

A wani mataki da ake kallon zai taimaka wajen ƙarfafa haɗin kai da zaman lafiya a nahiyar Afirka, Cibiyar Kasa da Kasa ta Ilimin Kafofin Watsa Labarai da Ilimin Bayani (IMILI), wadda ke daga cikin cibiyoyin da ke aiki ƙarƙashin inuwar UNESCO a matsayin cibiyar Category 2 ta farko a wannan fanni, ta sanar da ƙaddamar da ɗaya daga cikin manyan shirye-shiryenta na nahiyar baki ɗaya mai suna Africa Against ɗenophobia Project (AfAɗ-P), wato Shirin Yaƙi da ƙyamar Baƙi a Afirka. An gudanar da ƙaddamarwar ne ta kafar intanet a ranar Alhamis, 18 ga watan Yuni, 2026, daidai lokacin da…
Read More
Amurka ta yi amai ta lashe kan batun yarjejeniyar nukiliya da kuɗaɗen Iran da aka yi 

Amurka ta yi amai ta lashe kan batun yarjejeniyar nukiliya da kuɗaɗen Iran da aka yi 

Saɓanin bayanai tsakanin Washington da Tehran ya tayar da ƙura kan yarjejeniyar kawo ƙarshen yaƙi, yayin da Majalisar Dattawan Amurka ta kaɗa ƙuri'ar dakatar da yaƙin duk da adawar Trump Daga bayanan da kamfanin dillancin labarai na Reuters ya tattara, wata sabuwar takaddama ta ɓulla tsakanin Amurka da Iran kan muhimman abubuwan da suka shafi yarjejeniyar da aka cimma domin kawo ƙarshen yaƙin da ya ɗauki watanni ana gwabzawa tsakanin ɓangarorin biyu. Shugaban Amurka Donald Trump ya bayyana cewa Iran ta amince a riƙa gudanar da bincike da sa ido kan cibiyoyinta na nukiliya har abada, amma Tehran ta fito…
Read More
Firaministan Birtaniya ya yi murabus ƙasa da shekaru biyu da zaɓen sa

Firaministan Birtaniya ya yi murabus ƙasa da shekaru biyu da zaɓen sa

A wani yanayi da ya girgiza siyasar Birtaniya tare da jefa jam'iyyar Labour cikin sabon yanayin rashin tabbas, Firaministan ƙasar Birtaniya, Keir Starmer, ya sanar da murabus dinsa daga muƙamin Firaminista kasa da shekaru biyu bayan ya yi nasara a babban zaɓen shekarar 2024.  Sanarwar murabus ɗin ta zo ne bayan makonni na rikice-rikicen siyasa, matsin lamba daga 'yan majalisar jam'iyyarsa, da kuma mummunan sakamakon zabukan cikin gida da suka nuna yadda farin jinin gwamnati ke ci gaba da raguwa a tsakanin masu kaɗa kuri'a. A cikin jawabin da ya yi, Starmer ya amince cewa jam'iyyarsa ta shiga wani yanayi…
Read More