Daga BASHIR ISAH
Kotun Ƙolin Saudiyya ta ce gobe Litinin shi ne zai zama 1 ga watan Ramadan na 1445 biyo bayan ganin jinjirin watan da aka yi da yammacin Lahadi.
Da wannan ake sa ran al’ummar musulmin ƙasar su tashi da azumi a ƙasa kamar yadda jaridar Arab News ta rawaito.