26
Jul
Rikicin da ke tsakanin Amurka da Iran ya sake ɗaukar sabon salo bayan ƙungiyar Houthi ta Yemen ta buɗe wani sabon fagen matsin lamba ta hanyar kakaba takunkumin ruwa kan Saudiyya, matakin da ya fara girgiza harkokin safarar mai da zirga-zirgar jiragen ruwa a yankin Gabas ta Tsakiya. Sabon matakin ya tilasta wasu manyan jiragen dakon danyen man Saudiyya guda biyu da suka nufi kasuwannin Chana da Indiya sauya alkibla a Tekun Bahar Maliya, domin kauce wa mashigin Bab el-Mandeb bayan Houthi ta yi barazanar kai hari kan duk wani jirgin da zai dauki ko sauke man Saudiyya. Masana harkokin…
