Kasashen Waje

Ghana na bikin cika shekara 67 da samu ‘yancin kai

Ghana na bikin cika shekara 67 da samu ‘yancin kai

Daga BASHIR ISAH A wannan Larabar ƙasar Ghana ke bikin cika shekara 67 da samun 'yancin kai daga Turawan mulkin mallaka. Ghana ta shafe shekara 83 a ƙarƙashin Turawan mulkin mallaka kafin daga bisani ta samu 'yancin kanta. Shugaban ƙasar na farko, Dr Kwame Nkrumah, ya bayyana samun 'yancin ƙasar a matsayin babban cigaba gane da shugabancin ƙasar. Ranar 6 ga Maris ta kowace shekara Ghana ke bikin ranar zagayowar samun 'yancin kai. Bikin wannan karon zai gudana ne a dandalin Youth Resource Centre da ke Koforidua. A 2017 ne Shugaba Nana Addo Dankwa Akufo-Addo ya ɗauki matakin jujjuya in…
Read More
Afrika ta yi tir da hare-haren Isra’ila a Gaza

Afrika ta yi tir da hare-haren Isra’ila a Gaza

*Falasɗinu ta yi maraba da taron AU Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Shugabannin ƙasashen Africa sun yi Allah wadai da hare-haren da Isra’ila ke ƙaddamarwa kan yankin Gaza da sunan kare kai, yayin da suka buƙaci ƙasar ta dakatar da varin wutar  ba tare da vata lokaci ba. Moussa Faki Mahamat, shugaban majalisar gudanarwar ƙungiyar ta AU ya ce wannan luguden wuta, babu abinda ke cikinsa illa cin zali da cin zarafi, kuma lokaci ya yi da duniya za ta mayar da Isra’ila cikin hayyacin ta. Kalaman na Faki na zuwa ne bayan doguwar maƙala da Prime ministan Falasɗinu…
Read More
Da Ɗumi-ɗumi: Ghazouani ya zama sabon Shugaban AU

Da Ɗumi-ɗumi: Ghazouani ya zama sabon Shugaban AU

Daga BASHIR ISAH Shugabannin ƙasashen Afirka ƙarƙashin Ƙungiyar Haɗi Kan Afirka (AU) sun zaɓi Shugaban Ƙasar Mauritania, Mohamed Ould Ghazouani, a matsayin sabon shugaban AU na 2024. Ghazouani ya gaji wannan kujera ne daga Shugaba Azali Assoumani na ƙasar Comoros, wanda ya yi riƙe shugabancin ƙungiyar a 2023. ’Yan Majalisa Wakilai 60 sun buƙaci a sauya fasalin Nijeriya Bankin Access ya naɗa sabuwar Babbar jamiar zartarwar rukunin bankunan ta riƙon ƙwarya An yi zaɓen a ranar Asabar, 17 ga Fabrairu yayin babban taron ƙungiyar karo na 37 wanda ke gudana a Addis Ababa, babban birnin Habasha.
Read More
Shugaban Ƙasar Namibiya ya rasu yana da shekara 82 a duniya

Shugaban Ƙasar Namibiya ya rasu yana da shekara 82 a duniya

Daga BASHIR ISAH Shugaban Kasar Namibiya, Hage Geingob, ya rasu yana da shekaru 82 a duniya, kamar yadda ofishinsa ya bayyana. Marigayin ya rasu ne sakamakon fama da cutar daji. Geingob ya mutu ne a ranar Lahadi a asibitin Lady Pohamba da ke Windhoek, babban birnin kasar, inda da matarsa ​​da 'ya'yansa suka kasance a gefensa, in ji Mukaddashin Shugaban Kasar, Nangolo Mbumba, a wata sanarwa da aka wallafa a shafin Facebook na Geingob. Mbumba ya ce "Al'ummar Namibiya ta yi rashin wani fitaccen hadimin jama'a, mai fafutukar kwato 'yanci, babban mai tsara tsarin mulkinmu da kuma ginshikin Namibia," in…
Read More
Ukraine na zargin wasu jami’anta da wawushe mata kuɗin makamai

Ukraine na zargin wasu jami’anta da wawushe mata kuɗin makamai

Daga BASHIR ISAH Binciken gwamnatin Ukraine ya bankado cewar wasu jami’an hukumar kula da makaman kasar sun hada baki da takwarorinsu na ma’aikatar tsaro, wajen karkatar da kusan Dala miliyan 40, da aka ware domin sayen makamai. Wannan na zuwa ne a daidai lokacin da kasar ke tsaka da fafata yaki tsakaninta da Rasha. Ya zuwa yanzu an gurfanar da mutum biyar a kotu kan zargin yin rub-da-ciki a kan kudin maka kamar yadda masu gabatar da kara suka bayyana. Kazalika, bayanan gwamnatin Ukraine sun ce ana tsare da wani guda da aka cafke shi a lokacin da yake kokarin…
Read More
‘Ba mu amince da ficewar Burkina Faso, Mali, Nijar ba’ –  ECOWAS

‘Ba mu amince da ficewar Burkina Faso, Mali, Nijar ba’ –  ECOWAS

Daga BASHIR ISAH Kungiyar Bunkasa Tattalin Arzikin Kasashen Afirka ta Yamma (ECOWAS), ta bayyana cewa har yanzu ba ta samu a hukumace sanarwar ficewar kasashen Burkina Faso, Mali da Jamhuriyar Nija daga kungiyar ba, don haka ba ta amince da ficewar da suka ce sun yi daga kungiyar ba. Cikin sanarwar da ta fitar a ranar Lahadi, ECOWAS ta ce “tana aiki tukuru tare da wadannan kasashe domin maido da tsarin mulkin dimokradiyya. "Burkina Faso da Nija da kuma Mali, kasashe ne masu matukar muhimmanci ga Kungiyar, kuma tana ci gaba da kokarin ganin an samu mafita game da tsarin…
Read More
Da Ɗumi-ɗumi: Nijar, Burkina Faso, Mali sun yi adabo da ECOWAS

Da Ɗumi-ɗumi: Nijar, Burkina Faso, Mali sun yi adabo da ECOWAS

Daga BASHIR ISAH Kasashen Burkina Faso da Mali da Nija sun sanar da ficewarsu daga Kungiyar Bunkasa Tattalin Azrzikin Kasashen Yammacin Afirka (ECOWAS). Shugabannin kasashen yankin Sahel ukun sun fitar da wata sanarwa inda suka ce "shawara ce mai cikakken iko" ta barin kungiyar "ba tare da bata lokaci ba". Kasashen masu fama da matsalolin tsaro dtun bayan da sjoji suka karbe mulkin kasashen. Idan dai za a iya tunawa, a watan Yulin Bara ne sojoji suka yi juyin mulki a Nijar, haka ma Burkina Faso 2022, sai kuma Mali a 2020. Duaka kasashen uku ECOWAS ta takatar da su…
Read More
Morocco ta karɓi jagorancin Hukumar Kare Haƙƙin Ɗan Adam ta MDD

Morocco ta karɓi jagorancin Hukumar Kare Haƙƙin Ɗan Adam ta MDD

Morocco ta yi nasarar lashe kujerar shugabancin Hukumar Kare Hakkin Dan Adam ta MDD bayan da ta doke abokiyar hamayyarta a wannan mukami wato Afirka ta Kudu. Bayan da aka bayyana nahiyar Afirka a matsayin wadda za ta shugabancin hukumar a wannan shekara ta 2024, duk da haka kasashen biyu wato Afirka ta Kudu da Morocco sun gaza cimma jituwa a tsakaninsu sai da aka je ga kada kuri’a. A quri’ar da aka kada a asirce ranar Laraba a birnin Geneva, dan takarar Kasar Morocco Omar Zniber ya samu kuri’u 30 yayin da abokin karawarsa Mxolisi Nkosi na Afirka ta…
Read More
Falasɗinawa sun yi zanga-zanga kan ziyarar Blinken a Ramallah

Falasɗinawa sun yi zanga-zanga kan ziyarar Blinken a Ramallah

A ranar Laraba da ta gabata, dubban Falasdinawa sun gudanar da wani gangami a Ramallah don nuna adawarsu da ziyarar sakataren harkokin wajen Amurka Antony Blinken a yankin yayin ziyarar da ya ke kaiwa gabas ta tsakiya dangane da yanqin Isra’ila da zuwa yanzu ya kashe Falasdinawa fiye da dubu ashirin da uku. Galibin Falasdinawan sun rike allunan da ke dauke da rubutun ‘‘ba ma maraba da zuwanka Blinken’’ sun yi dafifi akan tituna gabanin jami’an tsaro su tarwatsa su. Wannan ne ziyara ta biyu da Blinken ke kaiwa gabas ta tsakiya tun bayan faro yaqin na Isra’ila a Gaza…
Read More
Hajjin 2024: Nijeriya da Saudiyya sun rattaba hannu kan yarjejeniyar fahimtar juna

Hajjin 2024: Nijeriya da Saudiyya sun rattaba hannu kan yarjejeniyar fahimtar juna

Daga BASHIR ISAH An cimma yarjejeniyar aikin Hajjin bana tsakanin Gwamnatin Nijeriya da takwararta ta kasar Saudiyya. A ranar Lahadin da ta gabata bangarorin biyu suka rattaba hannu kan yarjejeniyar a Jedda, kasar Saudiyya, inda Ministan Harkokin Wajen Nijeriya, Ambasada Yusuf Maitama Tuggar ya wakilci Gwamnatin Nijeriya. Yayin wani taron ban gishiri, in ba ka manda da suka yi tare da Ministan Hajji da Umarah na Saudiyya, Dokta Taofiq bin Fawzan AlRabiah, Tuggar ya bayyana cewa ayyukan Hajjin 2024 za su gudana ne bisa sabbin dokokin da aka gindaya domin tabbatar da komai ya gudana a kan lokaci. Tattaunawar tasu…
Read More