07
Feb
Shugaban Amurka Donald Trump a ranar Talata ya rattaba hannu kan wata doka ta zartaswa da ta janye Washington daga wasu hukumomin Majalisar ɗinkin Duniya da suka hada da Hukumar Kare Haƙƙoƙin ɗan Adam (UNHRC), tare da kafa wani bincike kan kuɗaɗen da Amurka ke ba wa ƙungiyoyi da dama. Umurnin ya ce, ya janye Washington daga hukumar ta UNHRC da kuma babbar hukumar kula da Falasɗinawa ta MDD (UNRWA), kuma za ta sake duba shiga lamarin da Hukumar Ilimi Kimiyya da Al'adu Majalisar ɗinkin Duniya, wato UNESCO. An yi wannan yunƙurin ne don nuna adawa da abin da sakataren…