06
Mar
Daga BASHIR ISAH A wannan Larabar ƙasar Ghana ke bikin cika shekara 67 da samun 'yancin kai daga Turawan mulkin mallaka. Ghana ta shafe shekara 83 a ƙarƙashin Turawan mulkin mallaka kafin daga bisani ta samu 'yancin kanta. Shugaban ƙasar na farko, Dr Kwame Nkrumah, ya bayyana samun 'yancin ƙasar a matsayin babban cigaba gane da shugabancin ƙasar. Ranar 6 ga Maris ta kowace shekara Ghana ke bikin ranar zagayowar samun 'yancin kai. Bikin wannan karon zai gudana ne a dandalin Youth Resource Centre da ke Koforidua. A 2017 ne Shugaba Nana Addo Dankwa Akufo-Addo ya ɗauki matakin jujjuya in…