Kasashen Waje

Trump ya sanya hannu kan dokar janye Amurka daga Majalisar ɗinkin Duniya

Trump ya sanya hannu kan dokar janye Amurka daga Majalisar ɗinkin Duniya

Shugaban Amurka Donald Trump a ranar Talata ya rattaba hannu kan wata doka ta zartaswa da ta janye Washington daga wasu hukumomin Majalisar ɗinkin Duniya da suka hada da Hukumar Kare Haƙƙoƙin ɗan Adam (UNHRC), tare da kafa wani bincike kan kuɗaɗen da Amurka ke ba wa ƙungiyoyi da dama. Umurnin ya ce, ya janye Washington daga hukumar ta UNHRC da kuma babbar hukumar kula da Falasɗinawa ta MDD (UNRWA), kuma za ta sake duba shiga lamarin da Hukumar Ilimi Kimiyya da Al'adu Majalisar ɗinkin Duniya, wato UNESCO. An yi wannan yunƙurin ne don nuna adawa da abin da sakataren…
Read More
Shugabannin EU sun sha alwashin mayar da martani idan Trump ya sanya wa ƙungiyar haraji 

Shugabannin EU sun sha alwashin mayar da martani idan Trump ya sanya wa ƙungiyar haraji 

Shugabannin Tarayyar Turai da ke taro a Brussels jiya Litinin sun yi gargaɗin cewa. babu wanda zai yi nasara a yakin kasuwanci da Amurka, inda suka dage cewa za su mayar da martani idan Shugaba Donald Trump ya saka haraji. Shugaban Faransa Emmanuel Macron ya ce, dole ne Tarayyar Turai ta mayar da martani matuƙar shugaban Amurka Donald Trump ya tabbatar da barazanar da ya yi na saka wa ƙungiyar haraji. Macron ya ce, "Idan aka kai mana hari ta fuskar kasuwanci, Turai a matsayinta na mai cikakkiyar ƙarfi da iko dole ne ta tashi tsaye don kare kanta." Shugabannin…
Read More
Trump ya ba da umarnin kai hari na farko a Afirka kwanaki 12 bayan hawansa mulki

Trump ya ba da umarnin kai hari na farko a Afirka kwanaki 12 bayan hawansa mulki

Kwanaki 12 a wa'adin mulkinsa na biyu, Shugaba Donald Trump ya ba da umarnin kai gaggarumin farmakin soji kan ƙungiyar ISIS da Somaliya, a wani mataki da jami'ai suka ce yana nuni da ƙudurinsa na kawar da barazanar ta'addanci. Rundunar sojan Amurka ta Afrika (AFRICOM) a ƙarƙashin jagorancin sabon sakataren tsaron da aka rantsar, Pete Hegseth, ta kai wani harin samame ta sama a tsaunin Golis na Somalia, inda rahotanni suka ce sun kashe wasu mayaƙan ISIS. Jigon ɗaukar matakin na gaggawa dai shi ne yadda shugaba Trump ya mayar da hankali kan barazanar da wungiyar ISIS ke yi, musamman…
Read More
Ƙasashen duniya sun fara mayar da martani kan kalaman Trump na ƙwace Gaza

Ƙasashen duniya sun fara mayar da martani kan kalaman Trump na ƙwace Gaza

Bayan furucin shugaban Amurka Donald Trump da ya sha alwashin ƙwace yankin Gaza na Falasɗinu, tuni ƙasashe duniya da ƙungiyoyin Falasɗinawa suka fara mayar da martani na ƙin amincewa da wannan buƙata. ƙasar Saudiya ta ce ba za ta ƙulla dangantaka da Israila ba idan har babu yankin Gaza, da hakan ke zama martani kan kalaman shugaban Amurka Donald Trump da ya sha alwashin ƙwace Gaza. A wata sanarwa da ma’aikatar harkokin wajen Saudiya ta fitar ranar Laraba, ta yi fatali da duk wani shiri na kwashe Falasɗinawan Gaza zuwa ƙasashe makwafta. Yarima mai jiran gado, Prince Mohammed bin Salman…
Read More
EU ga ECOWAS: Ku nemo sabbin hanyoyin zama tare da Burkina Faso, Mali da Nijar

EU ga ECOWAS: Ku nemo sabbin hanyoyin zama tare da Burkina Faso, Mali da Nijar

Shugaban tawagar Tarayyar Turai a Najeriya da ƙungiyar tattalin arzikin ƙasashen yammacin Afirka, Ambasada Gautier Mignot, ya yi kira ga ƙungiyar ECOWAS da ta ɗauki wani sabon salo wajen mu'amala da Burkina Faso, Mali, da Nijar bakiɗaya. Da yake jawabi a Abuja yayin wani taron manema labarai a ranarTalata, Mignot ya bayyana nadama kan ficewar ƙasashen uku daga ƙungiyar ECOWAS, yana mai jaddada cewa haɗewar yankin na da matuƙar muhimmanci wajen samun wadata da kwanciyar hankali. "Wannan shawara ce da muka yi domin muna matuƙar goyon bayan haɗewar kasashen Afirka ta Yamma. Rabewar bai yi mana kyau ba," inji shi.…
Read More
Trump ya dakatar da dala miliyan 50 da gwamnatin Biden ta ware don raba ‘kwaroron roba a Gaza’

Trump ya dakatar da dala miliyan 50 da gwamnatin Biden ta ware don raba ‘kwaroron roba a Gaza’

Gwamnatin Trump ta sanya takunkumi kan tallafin da gwamnatin tarayya ke bayarwa, ciki har da dala miliyan 50 da aka ware tun farko don raba kwaroron roba a Gaza. Sakatariyar yaɗa labaran fadar White House, Karoline Leaɓitt, ta ce an gano kashe kudaden ne a makon farko na Trump ciki har da sabuwar Ma'aikatar Gwamnatin da ke ƙarƙashin jagorancin hamshaƙin attajirin nan na fasaha Elon Musk. Yunƙurin Musk da ofishin kasafin kuɗi sun gano cewa akwai kusan dala miliyan 50 masu biyan haraji da suka fita don ba da tallafin kwaroron roba a Gaza,” Leavitt ta faɗa wa taron manema…
Read More
Mutum 15 sun mutu a turmutsutsun da ya afku a wurin taron addinin Hindu a Indiya

Mutum 15 sun mutu a turmutsutsun da ya afku a wurin taron addinin Hindu a Indiya

Aƙalla mutane 15 daga cikin masu ziyarar addinin Hindu suka mutu sakamakon turmutsutsun da aka samu yau Laraba, yayin da wasu da dama suka samu raunuka. Tuni Firaminista Narendra Modi ya aike da saƙon ta'aziya ga iyalan waɗanda haɗarin ya ritsa da su. Wannan dai ba shi ne karo na farko da ake samun irin wannan turmutsutsun ba a bukukuwan addinin mabiya Hindu da ke gudana a Kumbh Mela ta ƙasar Indiya, wanda ke samun halartar mutane aƙalla miliyan 4 kowaccce shekara. Rahotanni sun ce an samu haɗarin na ranar da asubah lokacin da dubban mutane suka kwarara domin yin…
Read More
Ababen da suka biyo bayan rantsar da Trump 

Ababen da suka biyo bayan rantsar da Trump 

Amurka ta fice daga WHO Dokar zama ɗan ƙasa ta haihuwa Gyaran fuska ga hukumar sojin Amurka  Dokar sauyin yanani ta koma ƙasa Kisa ga baƙin haure da suka yi wasu laifuka Soke manhajar CBP da Biden ya kafa  Trump ya gargadi Rasha kan yaƙinta da Ukraine  Shugaban Amurka ya bada umurnin kai samame Coci da asibiti don kama baƙin haure Daga cikin ababen da zaɓaɓɓen shugaban ƙasar Donald Trump ya yi alƙawarin rattabawa hannu a ranar farko a matsayin rantsatsen shugaban ƙasa suna da yawa, inda shugaban ya faɗi wasu daga ciki kafin zuwan ranar rantsar da shi din.…
Read More
Isra’ila ta amince da yarjejeniyar tsagaita wuta ta Gaza

Isra’ila ta amince da yarjejeniyar tsagaita wuta ta Gaza

Daga BELLO A. BABAJI A ranar Asabar ne jagororin Isra'ila suka amince da yarjejeniyar Gaza ta tsagaita wuta da kuma sako fursunonin da aka tsare, kamar yadda wata sanarwa daga ofishin Firaministan ƙasar Benjamin Netanyahu ta bayyana, wadda ake fatan ta fara aiki nan take. A ranar Lahadi ne ake sa ran tabbatar da tsagaita wutar, wadda za ta bada damar tsayar da kai farmaki da tayar da boma-bomai a tsakanin ƙasashen biyu. Sannan za ta bada damar sako fursunonin yaƙi da Hamas ta kama a lokacin da ta kai wani farmaki a ranar 7 ga watan Oktoban 2023, a…
Read More
Rundunar sojojin ƙasa ta yi naɗe-naɗe ga manyan jami’anta

Rundunar sojojin ƙasa ta yi naɗe-naɗe ga manyan jami’anta

Daga BELLO A. BABAJI Shugaban jami'an sojojin ƙasa (COAS) Laftanal Janar Olufemi Oluyede ya amince da naɗe-naɗen wasu manyan jami'ai a ofisoshi daban-daban na rundunar. Kakakin sojojin ƙasa, Manjo-Janar Onyema Nwachukwu ya faɗi hakan a wata sanarwa da ya fitar a ranar Asabar, inda ya ce shugaban sojojin ya yi hakan ne don inganta harkokin gudanar da ayyukansu. Ya ce an kuma sauya wa waɗansu jami'ai wuraren aiki a ƙoƙarin rundunar na daƙile matsalolin tsaro da ake fuskanta a ƙasar. Jami'an sun haɗa da manyan jami'an hedikwatar rundunar (PSOs), Kwamandodin sansanonin horarwa, Janarorin jami'ai na GOCs, Kwamandodin Birget-Birget da suaran…
Read More