Kasashen Waje

Harin sama na Isra’ila a Lebanon ya yi sanadin mutuwar mutum 13

Harin sama na Isra’ila a Lebanon ya yi sanadin mutuwar mutum 13

Akalla mutum 13 ne suka rasa rayukansu sakamakon sabbin hare-haren sama da Isra'ila ta kai a kudancin Lebanon a ranar Laraba, kamar yadda majiyoyin tsaro na Lebanon suka bayyana, a daidai lokacin da Isra'ila ke ci gaba da matsa kaimi wajen kai farmaki kan kungiyar Hezbollah, yayin da ita kuma ƙungiyar mai samun goyon bayan Iran ke iƙirarin kai sabbin hare-hare kan dakarun Isra'ila a kudancin ƙasar. Rahotannin cikin gida sun nuna cewa cikin waɗanda suka mutu akwai mutum tara da suka rasa rayukansu a ƙauyen Dayr Debba, mai nisan kusan kilomita takwas daga gabashin birnin Tyre. Kamfanin dillancin labarai…
Read More
Firaministan Isra’ila ya tabbatar da shirin sake tsayawa takara bayan kalaman Trump da suka tayar da ƙura

Firaministan Isra’ila ya tabbatar da shirin sake tsayawa takara bayan kalaman Trump da suka tayar da ƙura

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu zai sake neman wa'adin mulki a zaɓen da ake sa ran gudanarwa a bana, kamar yadda jam'iyyarsa ta Likud ta tabbatar a ranar Laraba, bayan wasu kalamai daga Shugaban Amurka Donald Trump sun haifar da tambayoyi kan ko zai sake shiga takara ko kuwa. A cikin takaitaccen sanarwar da jam'iyyar Likud ta fitar, ta bayyana cewa Netanyahu zai tsaya takara a zaɓen, tare da nuna fatan cewa, da yardar Allah, zai sake samun nasara. Ko da yake har yanzu ba a ayyana ranar gudanar da zaɓen a hukumance ba, dokokin ƙasar sun tanadi cewa dole ne…
Read More
Cutar Ebola ta yi sanadin mutuwar jaririya bayan mutuwar mahaifiyarta a Kongo 

Cutar Ebola ta yi sanadin mutuwar jaririya bayan mutuwar mahaifiyarta a Kongo 

Jamhuriyar Dimokuradiyyar Kongo ta sake tsintar kanta a tashin hankali sakamakon annoba mai tayar da hankali ta sake bayyana a gabashin Kongo bayan wata jaririya mai suna Buswaza ta rasa ranta sakamakon cutar Ebola, lamarin da ya sake fito da irin haɗarin da yara ƙanana da jarirai ke fuskanta a yayin barkewar wannan muguwar cuta. Rahotanni sun bayyana cewa bayan rasuwar mahaifiyarta a karshen watan Mayu, an kai Buswaza zuwa wani gidan marayu da Cocin Kirista ke gudanarwa a garin Bunia. Sai dai ba da jimawa ba limaman mata masu kula da gidan suka lura cewa jaririyar na fama da…
Read More
Yaƙi ya dawo sabo tsakanin Amurka da Iran bayan sabbin hare-hare

Yaƙi ya dawo sabo tsakanin Amurka da Iran bayan sabbin hare-hare

Daga USMAN KAROFI Yaƙi tsakanin Amurka da Iran ya sake ɗaukar wani sabon salo bayan Amurka ta kai hare-hare kan wasu wuraren sojin Iran a ƙarshen mako, yayin da Iran ta mayar da martani da kai hare-hare kan sansanonin sojin Amurka a yankin Gabas ta Tsakiya. Rundunar Amurka ta ce hare-haren nata sun biyo bayan zargin cewa Iran ta harbo jirgin leƙen asirin Amurka mara matuƙi da ke shawagi a sararin samaniyar ƙasa da ƙasa. A cewar CENTCOM, jiragen yaƙin Amurka sun lalata wasu cibiyoyin kariyar sararin samaniyar Iran, cibiyar sarrafa hare-hare da kuma wasu jirage marasa matuƙi da ake…
Read More
Afirka ta Kudu: Johannesburg na fuskantar barazanar katse wutar lantarki saboda bashin biliyoyin kuɗaɗe

Afirka ta Kudu: Johannesburg na fuskantar barazanar katse wutar lantarki saboda bashin biliyoyin kuɗaɗe

Birnin Johannesburg, wanda ake kallonsa a matsayin zuciyar tattalin arzikin South Africa, ya shiga wani sabon yanayi mai tayar da hankali bayan kamfanin samar da wutar lantarki mallakin gwamnati, Eskom, ya yi barazanar rage ko ma katse wutar lantarkin da yake bai wa birnin saboda tarin bashin da ya ce gwamnatin birnin ta kasa biya tsawon lokaci. Kamfanin Eskom ya bayyana cewa birnin Johannesburg tare da kamfanin rarraba wutar lantarki na birnin mai suna City Power suna bin sa bashin rand biliyan 5.26, kwatankwacin dala miliyan 315. Haka kuma akwai wani ƙarin bashin rand biliyan 1.58 da ya kamata a…
Read More
Somaliland na shirin buɗe ofishin jakadanci a Jerusalem bayan Isra’ila ta amince da ita a matsayin ƙasa

Somaliland na shirin buɗe ofishin jakadanci a Jerusalem bayan Isra’ila ta amince da ita a matsayin ƙasa

Somaliland mai neman ɓallewa daga Somalia ta sanar da cewa nan ba da jimawa ba za ta buɗe ofishin jakadancinta a birnin Jerusalem, bayan Israel ta zama ƙasa ta farko da ta amince da ita a hukumance a matsayin ƙasa mai cin gashin kanta. Jakadan Somaliland, Mohamed Hagi, ne ya bayyana hakan cikin wani saƙo da ya wallafa a shafin ɗ, inda ya ce matakin wani ɓangare ne na sabuwar dangantakar diflomasiyya tsakanin ɓangarorin biyu. A cewarsa, Isra’ila ita ma za ta buɗe ofishin jakadancinta a babban birnin Somaliland wato Hargeisa. Tun a watan Disamban bara ne Isra’ila ta sanar…
Read More
Iran ta yi barazanar yaɗa yaƙi fiye da gabas ta tsakiya idan Amurka ta sake kai hari

Iran ta yi barazanar yaɗa yaƙi fiye da gabas ta tsakiya idan Amurka ta sake kai hari

*Rikicin Hormuz na ci gaba da girgiza kasuwar mai ta duniya *Iran na neman a janye takunkumi da kuɗaɗenta da aka daskarar Iran ta yi wata sabuwar barazana mai tayar da hankali inda ta ce idan Amurka ta sake kai mata hari, yaƙin ba zai tsaya a yankin Gabas ta Tsakiya kawai ba, zai bazu zuwa wasu yankuna na duniya. Barazanar ta fito ne bayan shugaban Amurka Donald Trump ya bayyana cewa ya kusa bayar da umarnin sake kai hare-haren bama-bamai kan Iran, amma ya dakatar da shawarar a minti na ƙarshe domin bai wa tattaunawar diflomasiyya damar ci gaba.…
Read More
Yadda shari’ar “Farmgate” ke barazana ga makomar shugaban Afirka ta Kudu

Yadda shari’ar “Farmgate” ke barazana ga makomar shugaban Afirka ta Kudu

A yayin da siyasar Afirka ta Kudu ke ƙara shiga wani sabon yanayi mai cike da tashin hankali, shugaban ƙasar, Cyril Ramaphosa, na fuskantar ɗaya daga cikin manyan ƙalubalen siyasa tun bayan hawansa mulki a shekarar 2018. Wannan na zuwa ne bayan sake farfaɗo da batun tsige shi daga mulki sakamakon wata badaƙala da aka fi sani da “Farmgate” lamarin da ya janyo ce-ce-ku-ce mai girma kan maƙudan kuɗaɗen ƙasashen waje da aka ce an ɓoye a cikin kujera a gonarsa. Rahotanni sun nuna cewa barayin da suka shiga gonar shugaban ƙasar sun yi awon gaba da dubban daloli da…
Read More
Amurka da Iran na shirin komawa teburin tattaunawa duk da killace tashoshin jiragen ruwa

Amurka da Iran na shirin komawa teburin tattaunawa duk da killace tashoshin jiragen ruwa

Rahotanni sun nuna cewa tattaunawar kawo ƙarshen yaƙin Iran na iya sake farawa a ƙasar Pakistan cikin kwanaki biyu masu zuwa, kamar yadda Shugaban Amurka Donald Trump ya bayyana, bayan da zaman sulhun ƙarshen mako ya rushe, abin da ya sa Amurka ta ɗauki matakin killace tashoshin jiragen ruwan Iran. Jami’an diflomasiyya daga Pakistan, Iran da ƙasashen yankin Gulf sun tabbatar da cewa akwai yiwuwar tawagogin Amurka da Iran za su koma Pakistan nan da ƙarshen wannan mako domin ci gaba da tattaunawa, duk da cewa wani babban jami’in Iran ya ce har yanzu ba a tsaida takamaiman ranar ba.…
Read More
Rikicin siyasa tsakanin Amurka da Italiya na ƙara tsananta

Rikicin siyasa tsakanin Amurka da Italiya na ƙara tsananta

*Trump ya soki Meloni, ya ce ya yi mamaki da halinta *Firaministar ta ce ta dawo daga rakiyar Trump kan yaƙi da Iran  Shugaban Amurka Donald Trump ya caccaki Firaministar Italiya Giorgia Meloni, yana mai cewa ta nuna rashin jaruntaka kuma ta ba Amurka kunya, a wani mataki da ya girgiza dangantakar siyasa tsakanin ƙasashen biyu. Meloni, wadda a baya ta kasance mai goyon bayan Trump, ta fara nesanta kanta da shi bayan yaƙin Iran, sannan ta soki kalaman da Trump ya yi kan Paparoma Leo, tana kiran su marasa dacewa. Trump ya mayar da martani cikin hira da jaridar…
Read More