14
Jun
Akalla mutum 13 ne suka rasa rayukansu sakamakon sabbin hare-haren sama da Isra'ila ta kai a kudancin Lebanon a ranar Laraba, kamar yadda majiyoyin tsaro na Lebanon suka bayyana, a daidai lokacin da Isra'ila ke ci gaba da matsa kaimi wajen kai farmaki kan kungiyar Hezbollah, yayin da ita kuma ƙungiyar mai samun goyon bayan Iran ke iƙirarin kai sabbin hare-hare kan dakarun Isra'ila a kudancin ƙasar. Rahotannin cikin gida sun nuna cewa cikin waɗanda suka mutu akwai mutum tara da suka rasa rayukansu a ƙauyen Dayr Debba, mai nisan kusan kilomita takwas daga gabashin birnin Tyre. Kamfanin dillancin labarai…
