29
Jan
Daga BASHIR ISAH Kungiyar Bunkasa Tattalin Arzikin Kasashen Afirka ta Yamma (ECOWAS), ta bayyana cewa har yanzu ba ta samu a hukumace sanarwar ficewar kasashen Burkina Faso, Mali da Jamhuriyar Nija daga kungiyar ba, don haka ba ta amince da ficewar da suka ce sun yi daga kungiyar ba. Cikin sanarwar da ta fitar a ranar Lahadi, ECOWAS ta ce “tana aiki tukuru tare da wadannan kasashe domin maido da tsarin mulkin dimokradiyya. "Burkina Faso da Nija da kuma Mali, kasashe ne masu matukar muhimmanci ga Kungiyar, kuma tana ci gaba da kokarin ganin an samu mafita game da tsarin…