Kasashen Waje

‘Ba mu amince da ficewar Burkina Faso, Mali, Nijar ba’ –  ECOWAS

‘Ba mu amince da ficewar Burkina Faso, Mali, Nijar ba’ –  ECOWAS

Daga BASHIR ISAH Kungiyar Bunkasa Tattalin Arzikin Kasashen Afirka ta Yamma (ECOWAS), ta bayyana cewa har yanzu ba ta samu a hukumace sanarwar ficewar kasashen Burkina Faso, Mali da Jamhuriyar Nija daga kungiyar ba, don haka ba ta amince da ficewar da suka ce sun yi daga kungiyar ba. Cikin sanarwar da ta fitar a ranar Lahadi, ECOWAS ta ce “tana aiki tukuru tare da wadannan kasashe domin maido da tsarin mulkin dimokradiyya. "Burkina Faso da Nija da kuma Mali, kasashe ne masu matukar muhimmanci ga Kungiyar, kuma tana ci gaba da kokarin ganin an samu mafita game da tsarin…
Read More
Da Ɗumi-ɗumi: Nijar, Burkina Faso, Mali sun yi adabo da ECOWAS

Da Ɗumi-ɗumi: Nijar, Burkina Faso, Mali sun yi adabo da ECOWAS

Daga BASHIR ISAH Kasashen Burkina Faso da Mali da Nija sun sanar da ficewarsu daga Kungiyar Bunkasa Tattalin Azrzikin Kasashen Yammacin Afirka (ECOWAS). Shugabannin kasashen yankin Sahel ukun sun fitar da wata sanarwa inda suka ce "shawara ce mai cikakken iko" ta barin kungiyar "ba tare da bata lokaci ba". Kasashen masu fama da matsalolin tsaro dtun bayan da sjoji suka karbe mulkin kasashen. Idan dai za a iya tunawa, a watan Yulin Bara ne sojoji suka yi juyin mulki a Nijar, haka ma Burkina Faso 2022, sai kuma Mali a 2020. Duaka kasashen uku ECOWAS ta takatar da su…
Read More
Morocco ta karɓi jagorancin Hukumar Kare Haƙƙin Ɗan Adam ta MDD

Morocco ta karɓi jagorancin Hukumar Kare Haƙƙin Ɗan Adam ta MDD

Morocco ta yi nasarar lashe kujerar shugabancin Hukumar Kare Hakkin Dan Adam ta MDD bayan da ta doke abokiyar hamayyarta a wannan mukami wato Afirka ta Kudu. Bayan da aka bayyana nahiyar Afirka a matsayin wadda za ta shugabancin hukumar a wannan shekara ta 2024, duk da haka kasashen biyu wato Afirka ta Kudu da Morocco sun gaza cimma jituwa a tsakaninsu sai da aka je ga kada kuri’a. A quri’ar da aka kada a asirce ranar Laraba a birnin Geneva, dan takarar Kasar Morocco Omar Zniber ya samu kuri’u 30 yayin da abokin karawarsa Mxolisi Nkosi na Afirka ta…
Read More
Falasɗinawa sun yi zanga-zanga kan ziyarar Blinken a Ramallah

Falasɗinawa sun yi zanga-zanga kan ziyarar Blinken a Ramallah

A ranar Laraba da ta gabata, dubban Falasdinawa sun gudanar da wani gangami a Ramallah don nuna adawarsu da ziyarar sakataren harkokin wajen Amurka Antony Blinken a yankin yayin ziyarar da ya ke kaiwa gabas ta tsakiya dangane da yanqin Isra’ila da zuwa yanzu ya kashe Falasdinawa fiye da dubu ashirin da uku. Galibin Falasdinawan sun rike allunan da ke dauke da rubutun ‘‘ba ma maraba da zuwanka Blinken’’ sun yi dafifi akan tituna gabanin jami’an tsaro su tarwatsa su. Wannan ne ziyara ta biyu da Blinken ke kaiwa gabas ta tsakiya tun bayan faro yaqin na Isra’ila a Gaza…
Read More
Hajjin 2024: Nijeriya da Saudiyya sun rattaba hannu kan yarjejeniyar fahimtar juna

Hajjin 2024: Nijeriya da Saudiyya sun rattaba hannu kan yarjejeniyar fahimtar juna

Daga BASHIR ISAH An cimma yarjejeniyar aikin Hajjin bana tsakanin Gwamnatin Nijeriya da takwararta ta kasar Saudiyya. A ranar Lahadin da ta gabata bangarorin biyu suka rattaba hannu kan yarjejeniyar a Jedda, kasar Saudiyya, inda Ministan Harkokin Wajen Nijeriya, Ambasada Yusuf Maitama Tuggar ya wakilci Gwamnatin Nijeriya. Yayin wani taron ban gishiri, in ba ka manda da suka yi tare da Ministan Hajji da Umarah na Saudiyya, Dokta Taofiq bin Fawzan AlRabiah, Tuggar ya bayyana cewa ayyukan Hajjin 2024 za su gudana ne bisa sabbin dokokin da aka gindaya domin tabbatar da komai ya gudana a kan lokaci. Tattaunawar tasu…
Read More
Amurka da Birtaniya sun ƙara wa Hamas takunkumai

Amurka da Birtaniya sun ƙara wa Hamas takunkumai

Amurka da Birtaniya sun sanar da ƙara wa Hamas sabbin takunkumai sakamakon harin da ƙungiyar ta kai wa Isra'ila a ranar 7 ga watan Oktoban, inda aka samu salwantar rayuka. Ma'aikatar Baitul Malin Amurka ta ce, wannan matakin ya shafi manyan jami'an da ke ruruta manufar ta'addacin Hamas ta hanyar wakiltar manufofin ƙungiyar a ƙasashen ƙetare tare da kula da asusunta. Tun bayan harin na Oktoba da ƙungiyar ta ƙaddamar da ya kashe kimanin mutane dubu ɗaya da ɗari biyu, akasarinsu fararen hula, tare da garkuwa da mutane 240, Amurka ke matsin lamba kan mayaƙan. Baitul Mali Amurka ya ce,…
Read More
Isra’ila ta kashe Falasɗinawa 17,000 a cikin kwana 62

Isra’ila ta kashe Falasɗinawa 17,000 a cikin kwana 62

Daga BASHIR ISAH Falasɗin ta bayyana cewa, Isra'ila ta kashe sama da mutum 17,000 a Gaza a cikin kwana 62 a ci gaba da gwabza yaƙi a tsakanin ƙasashen biyu. Falasɗin ta ce daga cikin wannan adadi, 7,224 ƙanan yara ne, sai kuma mata 5,818, tsofoffi 478, jami'an kiwon lafiya 281, 'yan jarida 77, sai kuma mutum 46,000 da suka jikkata. Ta ƙara da cewa, a bayyana ne cewa galibin waɗanda faɗan ya fi shafuwa mata da ƙananan yara ne. Waɗannan bayanai na ƙunshe ne cikin sanarwar manema labarai da ƙasar Falasɗin ta fitar mai ɗauke da kwanan wata 11…
Read More
Hamas da Isra’ila sun sake tsawaita yarjejeniyar tsagaita wuta

Hamas da Isra’ila sun sake tsawaita yarjejeniyar tsagaita wuta

Isra’ila da Hamas sun amince da qara tsawaita yarjejeniyar da ke tsakaninsu da aƙalla kwana guda, matakin da ke zuwa mintuna ƙalilan gabanin kawo ƙarshen makamanciyar yarjejeniyar ta kwanaki shida da aka faro. Wannan mataki dai na zuwa ne bayan tsanantar kiraye-kirayen ganin an ɗauki wannan mataki, inda sakatare Janar na Majalisar Ɗinkin Duniya Antonio Guterres ke miqa buƙatar ganin an samar da yarjejeniyar dindindn tsakanin ɓangarorin biyu tare da isar da kayakin agaji cikin gaggawa a Gaza. Sai dai sanarwar ma’aikatar tsaron Isra’ila ta ce an ɗauki matakin ƙara kwana guda a yarjejeniyar ne, don samun damar sakin ƙarin…
Read More
Mutanen Gaza ba su gaza ba bayan kashe dubbai

Mutanen Gaza ba su gaza ba bayan kashe dubbai

Tare da NASIRU ADAMU EL-HIKAYA Fiye da mako 6 kenan sojojin Isra'ila su na ruwan wuta kan Gaza inda Falasɗinawa fiye da miliyan 2 da ke zaune a garin musamman arewacin sa ke zama cikin yiwuwar afkuwar komai a kullum. In za a tuna Isra'ila ta buƙaci Falasɗinawan su kaura zuiwa kudancin Gaza don kare ran su daga boma-bomai. Duk da dai ba lalle ba ne can kuɗin ma tudun mun tsira ne amma ya fi yankin arewaci 'yar sararawar hare-hare, hakan bai sa dubban Falasɗinawa kauracewa gidajen su ba. Wannan akwai abun dubawa a nan don ga gidajen an…
Read More
Shakira ta amince da biyan Ƙasar Sifaniya tarar fam miliyan 6.5

Shakira ta amince da biyan Ƙasar Sifaniya tarar fam miliyan 6.5

Daga AISHA ASAS  Daga ƙarshe dai fitacciyar mawakiyar Colombia, Shakira ta cimma yarjejeniya da masu shigar da ƙara na Ƙasar Sifaniya kan sasantawa dangane da tuhumar almundahanar biyan haraji da ke kanta. Yarjejeniyar na zuwa ne a daidai lokacin da ake shirin fara zaman kotu da ita. Mawakiyar ta biya tarar Yuro miliyan 7.5m, duk da cewa, a buƙatar masu gabatar da ƙara a yanzu sun so a ɗaure ta tsawon shekara takwas, sannan a ci ta tarar Yuro miliyan 23.8, idan aka same ta da laifi.  Kamar yadda Blueprint Manhaja ta ruwaito maku a 'yan watannin baya, mawaƙiyar ta…
Read More