Kasashen Waje

Kotun Koli ta Amurka ta yi fatali da yunƙurin Trump na taƙaita ‘yancin zama ɗan ƙasa ta haihuwa

Kotun Koli ta Amurka ta yi fatali da yunƙurin Trump na taƙaita ‘yancin zama ɗan ƙasa ta haihuwa

A wani hukunci da ake kallonsa a matsayin ɗaya daga cikin mafi muhimmanci a tarihin dokokin Amurka na baya-bayan nan, Kotun Kolin ƙasar ta yi watsi da ƙoƙarin Shugaba Donald Trump na takaita tsarin da ke bai wa duk wanda aka haifa a cikin ƙasar zama ɗan ƙasar Amurka kai tsaye, ba tare da la'akari da matsayin shige da ficen iyayensa ba. Hukuncin, wanda alƙalan kotun shida suka goyi baya yayin da uku suka nuna adawa da shi, ya zo ne a ranar ƙarshe ta wa'adin zaman kotun na wannan shekara, inda ya tabbatar da cewa tanadin Sashe na Bai…
Read More
Tashin hankali ya sake ɓarkewa a Afirka ta Kudu yayin da zanga-zangar ƙyamar baƙi ke ƙara ƙamari

Tashin hankali ya sake ɓarkewa a Afirka ta Kudu yayin da zanga-zangar ƙyamar baƙi ke ƙara ƙamari

Fargabar sake ɓarkewar rikicin kyamar baƙi ta mamaye sassa da dama na Afirka ta Kudu bayan dubban masu zanga-zanga sun mamaye titunan manyan biranen ƙasar ranar Talata, don nuna adawa da ci gaba da zaman baƙin haure ba bisa ƙa'ida ba. Zanga-zangar, wadda ƙungiyoyin masu adawa da shige da fice irin su March and March da Operation Dudula suka shirya, ta zo ne bayan cikar wa'adin da aka bai wa baƙin hauren da ba su da takardun zama su fice daga ƙasar. Lamarin ya haifar da tashin hankali a biranen Johannesburg, Pretoria, Durban da sauran yankuna da dama. Ko da…
Read More
Gobara ta yi ajalin aƙalla mutum biyar a ginin bene mai hawa 10 a Belgium

Gobara ta yi ajalin aƙalla mutum biyar a ginin bene mai hawa 10 a Belgium

Aƙalla mutum biyar ne suka rasa rayukansu bayan wata mummunar gobara ta tashi a wani katafaren ginin bene mai hawa goma da ke birnin Antwerp na ƙasar Belgium a safiyar Laraba, lamarin da ya jefa mazauna yankin cikin firgici wanda cikin ƙanƙanin lokaci aka fara gagarumin aikin ceto. 'Yan sandan Belgium sun tabbatar da faruwar lamarin, sai dai sun bayyana cewa har yanzu ba a iya tantance adadin mutanen da suka jikkata ko kuma gano musabbabin tashin gobarar ba. Tun da farko wasu kafafen yaɗa labarai na cikin gida sun rawaito cewa mutum shida ne suka mutu, bisa bayanan farko…
Read More
Cibiyar Yaɗa ilimin kafafen sada zumunta ta duniya ta ƙaddamar da shirin yaƙi da ƙyamar baƙi a Afirka 

Cibiyar Yaɗa ilimin kafafen sada zumunta ta duniya ta ƙaddamar da shirin yaƙi da ƙyamar baƙi a Afirka 

A wani mataki da ake kallon zai taimaka wajen ƙarfafa haɗin kai da zaman lafiya a nahiyar Afirka, Cibiyar Kasa da Kasa ta Ilimin Kafofin Watsa Labarai da Ilimin Bayani (IMILI), wadda ke daga cikin cibiyoyin da ke aiki ƙarƙashin inuwar UNESCO a matsayin cibiyar Category 2 ta farko a wannan fanni, ta sanar da ƙaddamar da ɗaya daga cikin manyan shirye-shiryenta na nahiyar baki ɗaya mai suna Africa Against ɗenophobia Project (AfAɗ-P), wato Shirin Yaƙi da ƙyamar Baƙi a Afirka. An gudanar da ƙaddamarwar ne ta kafar intanet a ranar Alhamis, 18 ga watan Yuni, 2026, daidai lokacin da…
Read More
Amurka ta yi amai ta lashe kan batun yarjejeniyar nukiliya da kuɗaɗen Iran da aka yi 

Amurka ta yi amai ta lashe kan batun yarjejeniyar nukiliya da kuɗaɗen Iran da aka yi 

Saɓanin bayanai tsakanin Washington da Tehran ya tayar da ƙura kan yarjejeniyar kawo ƙarshen yaƙi, yayin da Majalisar Dattawan Amurka ta kaɗa ƙuri'ar dakatar da yaƙin duk da adawar Trump Daga bayanan da kamfanin dillancin labarai na Reuters ya tattara, wata sabuwar takaddama ta ɓulla tsakanin Amurka da Iran kan muhimman abubuwan da suka shafi yarjejeniyar da aka cimma domin kawo ƙarshen yaƙin da ya ɗauki watanni ana gwabzawa tsakanin ɓangarorin biyu. Shugaban Amurka Donald Trump ya bayyana cewa Iran ta amince a riƙa gudanar da bincike da sa ido kan cibiyoyinta na nukiliya har abada, amma Tehran ta fito…
Read More
Firaministan Birtaniya ya yi murabus ƙasa da shekaru biyu da zaɓen sa

Firaministan Birtaniya ya yi murabus ƙasa da shekaru biyu da zaɓen sa

A wani yanayi da ya girgiza siyasar Birtaniya tare da jefa jam'iyyar Labour cikin sabon yanayin rashin tabbas, Firaministan ƙasar Birtaniya, Keir Starmer, ya sanar da murabus dinsa daga muƙamin Firaminista kasa da shekaru biyu bayan ya yi nasara a babban zaɓen shekarar 2024.  Sanarwar murabus ɗin ta zo ne bayan makonni na rikice-rikicen siyasa, matsin lamba daga 'yan majalisar jam'iyyarsa, da kuma mummunan sakamakon zabukan cikin gida da suka nuna yadda farin jinin gwamnati ke ci gaba da raguwa a tsakanin masu kaɗa kuri'a. A cikin jawabin da ya yi, Starmer ya amince cewa jam'iyyarsa ta shiga wani yanayi…
Read More
Harin sama na Isra’ila a Lebanon ya yi sanadin mutuwar mutum 13

Harin sama na Isra’ila a Lebanon ya yi sanadin mutuwar mutum 13

Akalla mutum 13 ne suka rasa rayukansu sakamakon sabbin hare-haren sama da Isra'ila ta kai a kudancin Lebanon a ranar Laraba, kamar yadda majiyoyin tsaro na Lebanon suka bayyana, a daidai lokacin da Isra'ila ke ci gaba da matsa kaimi wajen kai farmaki kan kungiyar Hezbollah, yayin da ita kuma ƙungiyar mai samun goyon bayan Iran ke iƙirarin kai sabbin hare-hare kan dakarun Isra'ila a kudancin ƙasar. Rahotannin cikin gida sun nuna cewa cikin waɗanda suka mutu akwai mutum tara da suka rasa rayukansu a ƙauyen Dayr Debba, mai nisan kusan kilomita takwas daga gabashin birnin Tyre. Kamfanin dillancin labarai…
Read More
Firaministan Isra’ila ya tabbatar da shirin sake tsayawa takara bayan kalaman Trump da suka tayar da ƙura

Firaministan Isra’ila ya tabbatar da shirin sake tsayawa takara bayan kalaman Trump da suka tayar da ƙura

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu zai sake neman wa'adin mulki a zaɓen da ake sa ran gudanarwa a bana, kamar yadda jam'iyyarsa ta Likud ta tabbatar a ranar Laraba, bayan wasu kalamai daga Shugaban Amurka Donald Trump sun haifar da tambayoyi kan ko zai sake shiga takara ko kuwa. A cikin takaitaccen sanarwar da jam'iyyar Likud ta fitar, ta bayyana cewa Netanyahu zai tsaya takara a zaɓen, tare da nuna fatan cewa, da yardar Allah, zai sake samun nasara. Ko da yake har yanzu ba a ayyana ranar gudanar da zaɓen a hukumance ba, dokokin ƙasar sun tanadi cewa dole ne…
Read More
Cutar Ebola ta yi sanadin mutuwar jaririya bayan mutuwar mahaifiyarta a Kongo 

Cutar Ebola ta yi sanadin mutuwar jaririya bayan mutuwar mahaifiyarta a Kongo 

Jamhuriyar Dimokuradiyyar Kongo ta sake tsintar kanta a tashin hankali sakamakon annoba mai tayar da hankali ta sake bayyana a gabashin Kongo bayan wata jaririya mai suna Buswaza ta rasa ranta sakamakon cutar Ebola, lamarin da ya sake fito da irin haɗarin da yara ƙanana da jarirai ke fuskanta a yayin barkewar wannan muguwar cuta. Rahotanni sun bayyana cewa bayan rasuwar mahaifiyarta a karshen watan Mayu, an kai Buswaza zuwa wani gidan marayu da Cocin Kirista ke gudanarwa a garin Bunia. Sai dai ba da jimawa ba limaman mata masu kula da gidan suka lura cewa jaririyar na fama da…
Read More
Yaƙi ya dawo sabo tsakanin Amurka da Iran bayan sabbin hare-hare

Yaƙi ya dawo sabo tsakanin Amurka da Iran bayan sabbin hare-hare

Daga USMAN KAROFI Yaƙi tsakanin Amurka da Iran ya sake ɗaukar wani sabon salo bayan Amurka ta kai hare-hare kan wasu wuraren sojin Iran a ƙarshen mako, yayin da Iran ta mayar da martani da kai hare-hare kan sansanonin sojin Amurka a yankin Gabas ta Tsakiya. Rundunar Amurka ta ce hare-haren nata sun biyo bayan zargin cewa Iran ta harbo jirgin leƙen asirin Amurka mara matuƙi da ke shawagi a sararin samaniyar ƙasa da ƙasa. A cewar CENTCOM, jiragen yaƙin Amurka sun lalata wasu cibiyoyin kariyar sararin samaniyar Iran, cibiyar sarrafa hare-hare da kuma wasu jirage marasa matuƙi da ake…
Read More