21
Aug
Matsalolin tsaro da Nijeriya ke fama da su sun kai wani matsayi mai matuƙar tayar da hankali, yayin da illolinsu ke yaɗuwa a sassa daban-daban na ƙasar. Saboda haka, bai kamata ƙasar ta ci gaba da barin bambance-bambancen addini, ƙabila da siyasa su zama abin da ke raba kan al’umma ko ke gurgunta haɗin gwiwar da ake buƙata wajen tunkarar matsalar tsaro ba. A saboda haka ne kiran da Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Mohammed Idris, ya yi na neman ’yan Nijeriya su haɗa kai wajen yaƙi da rashin tsaro ya dace da a mara masa baya sosai.…
