Ra’ayin Manhaja

Canje-canjen da Tinubu zai kawo na canja fasalin aikin NYSC

Canje-canjen da Tinubu zai kawo na canja fasalin aikin NYSC

Daga MAHDI MUSA MUHAMMAD Majalisar Zartarwa ta Tarayyar Nijeriya (FEC), ƙarƙashin jagorancin Shugaban ƙasa, Bola Ahmed Tinubu ta amince da gudanar da garambawul ga tsarin Hukumar Kula da Matasa Masu Yi Wa ƙasa Hidima (NYSC). Ministan Harkokin Matasa, Ayodele Olawande, ne ya bayyana hakan yayin da yake ganawa da manema labarai a Fadar Shugaban ƙasa da ke Abuja ranar Litinin, 29 ga watan Yuni, 2026. Olawande ya bayyana cewa an amince da sake fasalin NYSC ne a taron Majalisar Zartarwa da aka gudanar a Fadar Shugaban ƙasa da ke Abuja ranar Litinin. A cewarsa, garambawul ɗin zai haɗa da cikakken…
Read More
Matsalar tsaro: Yadda ra’ayoyi suka bambanta kan tasirin jami’an tsaron gandun daji

Matsalar tsaro: Yadda ra’ayoyi suka bambanta kan tasirin jami’an tsaron gandun daji

Daga MAHDI MUSA MUHAMMAD Masana harkokin tsaro da shugabannin al’umma a Jihar Kwara sun bayyana ra’ayoyi mabambanta kan shirin ɗaukar jami’an tsaron gandun daji, domin kare yankunan da gwamnati ba ta da cikakken iko a kansu, a wani yunƙuri na daƙile matsalar rashin tsaro da ke ƙara ta’azzara a sassan Nijeriya. Wani tsohon jami’in tallafa wa ayyukan ’yan sanda na al’umma a Birtaniya, ɗan asalin birnin Ilorin mai suina Taiwo Hanbali AbdulRaheem, ya bayyana cewa, ɗaukar jami’an tsaron gandun daji mataki ne mai kyau da ya dace a wannan lokaci. Sai dai ya yi gargaɗin cewa jami’an ba su da…
Read More
Kisan Maraban Jos da hatsarin al’adar ɗaukar doka a hannu

Kisan Maraban Jos da hatsarin al’adar ɗaukar doka a hannu

Kisan gilla da aka yi wa wata matar aure a garin Maraban Jos da ke ƙaramar Hukumar Igabi a Jihar Kaduna ya sake fito da wata babbar matsala da ta daɗe tana addabar al’ummomin Nijeriya – wato al’adar ɗaukar doka a hannu. Wannan mummunan lamari, wanda ya ƙare da banka wa wata mata wuta da ranta saboda zargin satar yara da ba a tabbatar ba, ya kamata ya zama abin da zai sa kowa ya tsaya ya yi tunani a kan inda al’umma ke dosa idan aka ci gaba da amincewa da irin wannan ɗabi’a mai haɗari. Rahotanni sun nuna…
Read More
Makomar Nijeriya na hannun matasa, amma dole a samar musu dama

Makomar Nijeriya na hannun matasa, amma dole a samar musu dama

Saƙon da Shugaban ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, ya gabatar a ranar Dimokuraɗiyya ga matasan Nujeriya ya cancanci zurfin tunani. Lokacin da ya buƙace su da su “ginu a nan, su ƙirƙira a nan, su yi aiki a nan, kuma su kaɗa wuri’a a nan,” ya tabo ɗaya daga cikin manyan ƙalubalen da ƙasar ke fuskanta a yau: ƙara yawaitar ficewar matasa masu ilimi, kuɗi da ƙwarewa zuwa ƙasashen waje domin neman ingantacciyar rayuwa. Furucinsa na cewa “Nijeriya ita ce gidanku kuma makomarku” ya kasance kira ne na kishin ƙasa da kuma ƙalubale ga matasa. Kusan dukkan ƙasashen da suka ci…
Read More
A-Kurkura: Magani ne ko sabuwar annobar da ke barazana ga al’umma?

A-Kurkura: Magani ne ko sabuwar annobar da ke barazana ga al’umma?

A da can, ana kallon A-Kurkura a matsayin wani maganin gargajiya da ake amfani da shi wajen rage ciwon haƙori, mura, gajiya da wasu ƙananan cututtuka. Amma a yau, abin da aka fara da sunan magani ya fara rikiɗewa zuwa wata babbar matsalar zamantakewa da lafiyar jama’a, musamman a Arewacin Nijeriya. Rahotanni daga jihohi daban-daban sun nuna yadda matasa, mata, dattawa har ma da masu sana’o’i suka rungumi amfani da A-Kurkura ba wai don magani kawai ba, har ma domin samun kuzari, nishaɗi ko kuma ƙara ƙarfin jiki. Wasu sun kai matsayin da ba za su iya gudanar da ayyukansu…
Read More
EBOLA: Rigakafi ya fi magani

EBOLA: Rigakafi ya fi magani

Yayin da cutar Ebola (EVD) ke sake ɓulla a Jamhuriyar Dimokuraɗiyyar Kongo (DRC) tare da tabbatar da samun wani mutum da ya shigo da cutar a maƙwabciyar ƙasar Uganda, duniya ta sake shiga yanayin fargaba da taka-tsantsan.  Wannan lamari ya sake tunatar da al’ummar duniya cewa cututtuka masu yaɗuwa ba sa mutunta iyakokin ƙasashe, kuma sa ido da shiri tun kafin matsala ta auku su ne manyan makaman kariya daga annoba. Da take fahimtar girman barazanar da lamarin ke haifarwa, Hukumar Lafiya ta Duniya (WHO) ta ayyana ɓarkewar cutar a matsayin Gaggawar Lafiyar Jama’a Ta Duniya (PHEIC). Ko da yake…
Read More
Karuwar cutar sanƙarau a Arewacin Nijeriya: Lokaci ya yi na ɗaukar matakin gaggawa

Karuwar cutar sanƙarau a Arewacin Nijeriya: Lokaci ya yi na ɗaukar matakin gaggawa

Nijeriya na fuskantar wani sabon ƙalubale mai tsanani a fannin kiwon lafiya, yayin da cutar sanƙarau ke ƙara yaɗuwa a jihohin arewacin ƙasar. Masana kiwon lafiya na gargaɗi cewa alluran rigakafin da ake da su a yanzu ba sa ba da cikakken kariya kan sabon nau’in ƙwayar cutar, wato Neisseria meningitidis nau’i na C, wanda ke bazuwa cikin sauri a yankin. Rahotanni daga Hukumar Daƙile Yaɗuwar Cututtuka ta Nijeriya (NCDC) sun nuna cewa yara masu shekaru tsakanin ɗaya zuwa goma sha biyar ne suka fi kamuwa da cutar. Haka kuma, cunkoson jama’a da ake samu a lokacin zafi, musamman a…
Read More
Yadda Tinubu ke tallata Nijeriya ga masu zuba jari na duniya

Yadda Tinubu ke tallata Nijeriya ga masu zuba jari na duniya

Ministan Kuɗi kuma Mai Kula da Tsare-tsaren Tattalin Arziki na ƙasa, Taiwo Oyedele, ya bayyana abin da mutane da dama suka riga suka fahimta lokacin da ya shaida wa manema labarai a wajen Taron Shugabannin Kamfanoni na Afirka da aka gudanar a Kigali na ƙasar Rwanda cewa Shugaba Bola Ahmed Tinubu na taka rawar gani wajen tallata Nijeriya ga masu zuba jari na duniya. “Abin farin ciki game da Shugaban ƙasa shi ne bai gajiya wajen tallata Nijeriya ba. Shi ne babban mai tallan ƙasar nan,” inji Oyedele. Tun bayan hawansa mulki, Shugaba Tinubu ya ɗauki Nijeriya zuwa gaban masu…
Read More
Manufofin Tinubu kan tsaron abinci da sabuwar Dokar Samar da Abinci ta 2026

Manufofin Tinubu kan tsaron abinci da sabuwar Dokar Samar da Abinci ta 2026

A daidai lokacin da matsalar yunwa da ƙarancin abinci ke ƙara addabar miliyoyin ’yan Nijeriya, gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu ta sake fito da wani sabon shiri da take ganin zai taimaka wajen magance matsalar tamowa da rashin wadataccen abinci a ƙasar nan. Wannan mataki ya zo ne bayan Majalisar ƙasa Kan Samar da Abinci Mai Gina Jiki ta amince da sabuwar Dokar Manufofin Abinci da Gina Jiki ta ƙasa (2026–2035), wadda ake sa ran za ta zama tubalin da za a dogara da shi wajen bunƙasa wadatar abinci da inganta lafiyar al’umma a Nijeriya. A zahiri, wannan mataki ya…
Read More
Rikicin FCCPC da NCC kan ba da rancen kati na haifar da cikas ga tattalin arziki

Rikicin FCCPC da NCC kan ba da rancen kati na haifar da cikas ga tattalin arziki

Rikicin da ke ci gaba tsakanin Hukumar Kula da Kare Haƙƙin Masu Amfani da Kaya ta ƙasa (FCCPC) da Hukumar Sadarwa ta Nijeriya (NCC) ya jefa kasuwar bashin katin kira da intanet wadda ke da darajar kusan Naira biliyan 400 cikin ruɗani, tare da haddasa cikas ga miliyoyin masu amfani da sadarwa a faɗin ƙsar. Saboda wannan saɓani na doka da iko tsakanin hukumomin biyu, wasu manyan kamfanonin sadarwa sun dakatar da tsarin bayar da rancen katin kira ga abokan hulɗarsu na ɗan lokaci. Wannan mataki ya jefa miliyoyin ‘yan Nijeriya cikin wahala, musamman masu ƙaramin ƙarfi da suka dogara…
Read More