Ra’ayin Manhaja

Nijeriya a matsayin ƙasar da ke fama da yunwa a duniya

Nijeriya a matsayin ƙasar da ke fama da yunwa a duniya

Rahotanni daga Majalisar Ɗinkin Duniya sun nuna cewa sama da mutane miliyan 113 a faɗin ƙasashe 53 ne suka fuskanci matsananciyar yunwa a shekarar da ya gabata a sanadiyyar yaƙe-yaƙe, annoba da kuma matsalolin tattalin arziki wanda ke haddasa ƙarancin abinci. Aqalla ’yan Nijeriya miliyan 25 ne ke fama da yunwa, yayin da mutane miliyan 9.3 ke fama da matsanancin ƙarancin abinci, wanda hakan ya sa ake ta samun zanga-zanga da fasa rumbunan adana abinci a wasu sassan ƙasar, daidai lokacin da ƙasar ke tsaka da fama da tashen-tashen hankula na masu ɗauke da makamai. Nijeriya na fuskantar rikici daga…
Read More
Batun aiwatar da rahoton ‘Oransaye’

Batun aiwatar da rahoton ‘Oransaye’

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya amince a aiwatar da rahoton kwamitin Stephen Oransaye. Wannan na daga cikin abubuwan da aka cimmawa a taron Majalisar Zartarwar Tarayya na ranar Litinin 26 ga watan Fabrairu, wanda shugaba Tinubu ya jagoranta a Abuja. Rahoton Stephen Oransaye na shekarar 2012 ya bayar da shawarar haɗe wasu ma'aikatu da hukumomin gwamnati waɗanda ayyukan su ke da alaqa da juna, a wani mataki na rage kuɗin da ake kashewa wajen tafiyar da gwamnati. Bayan taron Majalisar Zartarwar ne hukumomi suka fitar da sanarwa inda suka ce an yanke hukuncin aiwatar da rahoton Steve Oronsaye domin…
Read More
Kawo ƙarshen satar ɗanyen mai a Nijeriya

Kawo ƙarshen satar ɗanyen mai a Nijeriya

A kwanakin baya ne wata babbar kotun tarayya da ke zamanta a garin Fatakwal ta Jihar Ribas ta samu wasu mutane biyar da laifin satar man fetur da kuma safarar man fetur ba bisa ƙa’ida ba kuma ba tare da lasisin da ya dace ba sannan ta yanke musu hukunci daban-daban. Wannan dai na ɗaya daga cikin yawaitar satar mai da ake tafkawa a harkar mai da iskar gas wanda bisa ga dukkan alamu hakan ba wai a fannin mai kaɗai ya ke kawo cikas ba, har ma da ƙasa baki ɗaya. Tony Elumelu, Shugaban Kamfanin Bankin UBA kuma Shugaban…
Read More
Batun matsalar damfara a yanar gizo

Batun matsalar damfara a yanar gizo

Babu makawa ga duk mai mu'amala da yanar gizo (Internet) ko wayar salula ya san matakan kariya game yadda wadansu vata gari ke baza tarko ta ko wacce irin dama su ka samu don su damfari jama'a. Idan muka ce yanar gizo to anan mu na nufin Ko wanne fanni na yanar gizo. Shin kai ma'abocin burauzin ne don karanta labarai, ko mai binciken ilmi, ko ma'abocin kafofin sada zumunci da dai sauran su. Yau za mu kawo hanyoyin da su ka fi shahara wajen yin damfara a yanar gizo, kuma sanin su zai taimaka ma wajen tsallake tarkon su,…
Read More
Fargabar matsalar tattalin arzikin Nijeriya

Fargabar matsalar tattalin arzikin Nijeriya

A makon da ya gabata, Bankin Duniya ya fitar da rahotonsa kan tabarberewar tattalin arzikin Nijeriya. Rahoto a karkashin duba irin cigaban da Nijeriya ta samu, Cibiyar Hada-hadar Kudi Ta Duniya ta bayyana cewa, tabarbarewar yanayin tattalin arzikin Nijeriya na kara jefa al'ummar kasar cikin wani hali. Rahoton ya nuna cewa, hauhawar farashin kayayyaki ya zama annoba ga rayuwar ’yan Nijeriya wanda dole ne hukumomi su yi yaki da hakan. Habakar hauhawar farashin kayayyaki da ke fitowa daga matsalar rashin tsaro, Bankin ya ce, zai iya jefa karin 'yan Nijeriya miliyan daya cikin matsanancin talauci. Tabbas tashe-tashen hankulan da hauhawar…
Read More
Dole ne a ɗore da ya ƙi da cin hanci da rashawa a Nijeriya

Dole ne a ɗore da ya ƙi da cin hanci da rashawa a Nijeriya

Ranar Alhamis din da ya gabata ne al'ummar duniya suka ware a matsayin ranar yaki da cin hanci da rashawa ta duniya. Majalisar Dinkin Duniya ta kuduri mai lamba 58/4 na ranar 31 ga watan Oktoban shekarar 2003 ta ware ranar na kowace shekara a matsayin ranar wayar da kan jama'a game da laifukan da ke kawo cikas ga cigaba da kuma talauta jama'a. Har ila yau, rana ce ga shugabannin siyasa, gwamnatoci, hukumomin shari'a, kungiyoyin fafutuka da kungiyoyin farar hula don sabunta alkawurran da suka dauka na kawar da wannan abu da aka gano a matsayin wani lamari mai…
Read More
Abin da ’yan Nijeriya ke buƙata a 2024

Abin da ’yan Nijeriya ke buƙata a 2024

Shekarar da ta gabata, 2023, shekara ce da ta zo da kalubale ga 'yan Nijeriya. Ta zo ne da zazzabin gabatowar babban zaben 2023 tare da zuwa karshe da munanan hare-haren ta'addanci a Jihar Filato a lokacin Kirsimeti. Dangane da wahalhalun tattalin arziki da ya biyo bayan matakin farko na tattalin arziki na sabuwar gwamnatin Shugaba Bola Tinubu, gwamnatin ta yi bayanin cewa hakan ne farkon kuma karshen zafin rayuwa ga 'yan kasa a cikin sabon tsarin fatan shugaba Tinubu. Sai dai kuma a wannan shekara ta 2024 akwai wasu abubuwa da ’yan Nijeriya ke son ganin sun faru a…
Read More
Kawar da ciwon hanta kafin 2030

Kawar da ciwon hanta kafin 2030

A baya-bayan nan ne kasashen duniya suka gudanar da bikin ranar yaki da cutar 'Hepatitis' wanda ake kira da ciwon hanta a Hausance, domin kara wayar da kan jama’a game da wannan mummunar cuta da ta yi sanadiyyar mutuwar mutane da dama. Hepatitis ya kasu iri daban-daban har guda biyar, inda suka hada da; Hepatitis A, da Hepatitis B, da Hepatitis C, da Hepatitis D, da kuma Hepatitis E. Hukumar Lafiya ta Duniya ta ce, kimanin mutum miliyan 325 ke fama da ciwon hanta nau'in B da C a duniya. A yayin da ciwon hanta nau'in B kawai ke kashe…
Read More
Lokacin Hunturu: Matakan da suka wajaba a ɗauka don zama lafiya

Lokacin Hunturu: Matakan da suka wajaba a ɗauka don zama lafiya

A duk lokacin da aka shiga hunturu, wato lokacin sanyi da iska, wani lokaci ne da yanayi kan canja, wanda kowa da irin yadda yanayin yake zuwa masa, ta yadda wasu sukan samu kansu cikin wani yanayi na ƙunci, wasu kuma a wannan lokaci ne suka fi samun jin daɗin yanayi ta rayuwarsu gaba ɗayanta. Lokacin hunturu, lokaci ne na tsananin sanyi, iska da kuma ƙura, kuma wannan yanki namu na Arewa ne abin ya fi tsanani, ta yadda wasu lokuta ma hatta yanayin samaniya kan canja, a kan yi hadarin sanyi kamar yadda ake yin hadarin ruwan sama. Lokacin…
Read More
Ƙaruwar matsalar lalata da ɗalibai a jami’o’in Nijeriya

Ƙaruwar matsalar lalata da ɗalibai a jami’o’in Nijeriya

Ga duk mai bibiyar al’amuran da suka shafi shafin yanar gizo, ko kuma mu ce harkar yaɗa labarai a ƙasar nan ya san yadda a ’yan watannin nan ake yawan samun koke-koken game da yadda wasu malaman jami’o’i ke lalata da ɗalibansu don su ba da maki, ko kuma don a kai su inda ba su kai ba a harkar jarrabawa. Ko ba a ce komai ba, wannan wani mummunan abu ne da za a iya cewa bai kama da hakali ba, ko kuma mu ce wani abu ne da ya zama bala’in wanda idan ba a yi hankali ba…
Read More