03
Jan
A ranar Litinin da ta gabata ne shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya karɓi baƙuncin wasu ’yan jarida a gidansa da ke Legas domin tattaunawa da su wanda ya ɗauki kusan awa ɗaya ana yi. Wannan shi ne karon farko na irin wannan mu’amala da ’yan jarida da ya taɓa yi tun bayan da ya hau kan karagar mulki a ranar 29 ga Mayu, 2023. Tattaunawar shugaban ƙasa da ’yan jarida ya kasance abin da aka saba yi a lokacin mulkin Shugaba Olusegun Obasanjo. Tattaunawar ta ba shi damar yin magana kan wasu muhimman batutuwan ƙasa. Har ila yau, ta…