Ra’ayin Manhaja

Za mu daɗe muna yabon auren ƙabilu muna kushe namu

Za mu daɗe muna yabon auren ƙabilu muna kushe namu

Daga UNCLE LARABI Mata sun fi son a yi musu ƙarya, ko na kalamai ne, a neman aure, amma idan an yi aure cefane da neman abinci ba zai bayar da damar wannan yin ƙaryar ba tunda komai na zahiri ya gama bayyana. To, shi ya sa ake shan wahalar zamantakewa a gidajen Bahaushe na aure, saboda ba ma amfani da zahiri da gaskiya wajen neman auren. Mun fi son ƙarya da burgewa. Za mu daɗe muna cewa auren wasu ƙabilun yafi ƙarko. Misali; idan ku ka ɗauki ƙabilar Edo, Musulmai, ba Kirista ba, idan namiji zai yi aure sai…
Read More
’Yan Nijeriya akwai ƙura fa

’Yan Nijeriya akwai ƙura fa

Daga ALI ABUBAKAR SADIƙ Kimanin sati biyu da suka gabata na yi wani rubutu mai taken "Manaƙisar Amurka Ga Arewa." Abubuwa biyu ne suka faru a wancan lokaci. Na farko shine, sanarwar tsagaita wuta tsakanin Amurka da Iran. Na biyu kuma shine, bayanin ƙasar Amurka na umarta ma'aikatan jakadanci da ’yan ƙasarta su bar Nijeriya da kuma nesantar jihohin Arewa. Kamar yadda na bayyana a wancan rubutu cewa, tunda Iran ta gagari Amurka, inda ta kasa cimma muradinta da kuma datse mashigin Hormuz da Iran ta yi, wanda ya janyo tashin gwauron zabi na farashin mai a duniya, yanzu Nijeriya…
Read More
Shekaru 12 bayan Chibok: Har yanzu Nijeriya na fama da matsalar sace ɗalibai

Shekaru 12 bayan Chibok: Har yanzu Nijeriya na fama da matsalar sace ɗalibai

Shekaru goma sha biyu bayan mummunan harin da ya girgiza duniya a garin Chibok da ke Jihar Borno, al’amarin sace ɗalibai a Nijeriya ya ci gaba da zama babban ƙalubale ga tsaro da ilimi, tare da barin tambayoyi masu nauyi kan yadda za a dawo da amincewar jama’a ga tsarin kariya da gwamnati ke da shi. A daren 14 ga Afrilu, 2014, mayaƙan ƙungiyar Boko Haram sun kai hari makarantar sakandiren mata ta gwamnati da ke Chibok, inda suka yi awon gaba da ɗalibai 276 masu shekaru tsakanin 16 zuwa 18. Duk da cewa wasu 57 sun samu tserewa nan…
Read More
Barazanar da rigakafin cutar shan inna ke fustanta a Nijeriya

Barazanar da rigakafin cutar shan inna ke fustanta a Nijeriya

A shekarar 2020, Nijeriya ta rubuta tarihi da ruwan zinariya bayan da Hukumar Lafiya ta Duniya (WHO) ta tabbatar da cewa an kawar da cutar shan inna (wild poliovirus) daga ƙasar gaba ɗaya. Amma shekaru kaɗan bayan haka, wannan nasara mai girma na fuskantar barazana — ba daga ƙwayar cutar kanta ba, sai dai daga ƙin amincewar jama’a da rigakafi sakamakon rashin gaskatawa da yaɗuwar bayanan ƙarya. ƙididdiga daga bikin Tanar Yaƙi da Cutar Shan Inna ta Duniya na baya-bayan nan sun nuna gagarumin koma baya: sama da gidaje 3,000 a jihohin Sakkwato, Kebbi da Zamfara sun ƙi bari a…
Read More
Tsaron makarantun Nijeriya: Wajibi ne a ɗauki matakin gaggawa

Tsaron makarantun Nijeriya: Wajibi ne a ɗauki matakin gaggawa

Maganar Babban Kwamandan Hukumar Sibil Difens (NSCDC), Ahmed Audi, cewa sama da makarantu 60,000 daga cikin 81,000 a faɗin Nijeriya ba su da isasshen tsaro, lamari ne da ya girgiza zukata kuma ya kamata ya tayar da hankalin duk masu ruwa da tsaki. Wannan ba ƙididdiga ce kawai ba; alama ce ta giɓin da ke barazana ga rayuka da makomar yara miliyoyi. Audi ya bayyana hakan ne yayin karɓar baƙuncin Ministan Ilimi, Dakta Tunji Alausa, a ofishinsa da ke Abuja. Ya yi nuni da cewa yawancin waɗannan makarantu ba su da katanga, ba su da jami’an tsaro, kuma suna buɗe…
Read More
A tanadi hukunci kan sakacin likitoci

A tanadi hukunci kan sakacin likitoci

Mutuwar Aisha Umar, uwa ga ’ya’ya biyar, ba abin baƙin ciki kaɗai ba ne; hujja ce mai nauyi da ke tona asirin gazawar tsarin kiwon lafiyar Nijeriya. Rahotanni sun nuna cewa ta rasu ne bayan da asibiti ya bar almakashin tiyata a cikinta bayan an yi mata aiki, kuskure mai muni, mai sauƙin kaucewa, wanda uzurinsa ma yana da wuya a karɓa. Amma abin da ya biyo bayan mutuwarta ya fi tada hankali fiye da sakacin da kansa: an ce mijinta, Aubakar Binji, an shaida masa cewa mutuwarta “ƙaddarar Allah” ce. Wannan furuci ya yi daidai da al’adar kauce wa…
Read More
Kisan uwa da ’ya’ya shida: Kada fa a yi tuya a manta da albasa

Kisan uwa da ’ya’ya shida: Kada fa a yi tuya a manta da albasa

Daga UNCLE LARABI Zuwa ga masu nema wa mijin Fatima, wacce aka kashe tare da ’ya’yanta shida a birnin Kano taimako; wato Barista Abba Hikima, Fauziyya D. Sulaiman, Rahma Abdulmajid da Umma Sulaiman AuntyBaby, ana ta maganar Malam Baba Haruna ana tara masa himilin kuɗi, kada a manta da iyayen matarsa, Fatima. Idan Mahaifiyarta da mahaifinta suna raye, su ma suna cikin sahun farko da ba za su taɓa manta wannan mugun iftila'in ba. Ba za su iya barci mai kyau ba. Ba za su iya cin abinci, don yunwa ba. Kai hatta ’yan uwanta na jini da suke uwa ɗaya uba…
Read More
Taya murnar Kirsimeti da sabuwar shekarar 2026

Taya murnar Kirsimeti da sabuwar shekarar 2026

Bukukuwan Kirsimeti da ma na shigowar sabuwar shekara lokaci ne mai matuƙar muhimmanci ga al’ummar Kiristoci a sassan duniya, lokaci da ke ɗauke da zurfin ma’ana ta godiya, nuna ƙauna da soyayya. Wannan lokaci na musamman na tunatar da Kiristoci haihuwar Annabi Isa Almasihu, wanda rayuwarsa da saƙonsa suka ginu ne a kan ƙauna, yafiya, tausayi da kuma zaman lafiya tsakanin mutane. Kirsimeti ba biki ne na shagali kawai ba, illa wani muhimmin lokaci ne na nazari da waiwayen ɗabi’u da ya kamata su zama tubalin rayuwar al’umma.A haƙiƙanin gaskiya, Kirsimeti ba na Kiristoci kaɗai ba ne. Lokaci ne da…
Read More
Ranar harshen Hausa ba Ranar Hausawa ba!

Ranar harshen Hausa ba Ranar Hausawa ba!

Daga NASIRU ADAMU EL-HIKAYA Haƙiƙa harshen Hausa na daga manyan harsuna a duniya kuma ya yaɗu don yadda ya kan ari kalmomi daga wasu harsuna ya maida su Hausa. Harsunan da Hausa ya fi ɗaukar kalmomin sa shi ne Larabaci don alaƙar addinin Musulunci. Na biyu sai harshen Turancin inigilishi don zuwan Turawan mulkin mallaka. Harshen Hausa ya aro wasu kalmomin daga wasu ƙananan harsuna ko ma manya na Afirka da hakan ya ƙara ba shi tagomashin bunƙasa. Lamuran fatauci sun kai Hausawa wasu ƙasashe kamar Ghana inda harshen Hausa ya yadu a can amma ya samu tasirin sauya salon…
Read More
Yaƙi da bautar da yara ƙanana

Yaƙi da bautar da yara ƙanana

Sanarwar da ƙungiyar ƙwadago ta Majalisar ɗinkin Duniya (ILO) ta yi na baya-bayan nan ya nuna cewa, sama da yara miliyan 152 ko kusan ɗaya cikin yara 10 a duniya na fama da tilastawa wajen aure ko yin aikin ƙwadago wanda hakan ba wai kawai abin baƙin ciki ba ne amma har da nuna rashin mutuntaka. ƙungiyar ta ce, ƙananan yara sama da miliyan 10 ke aiki a matsayin baran gida ko kuma masu hidima a ƙasashen duniya, wanda ake danganta shi da bauta. ƙididigar da hukumar ta bayar cikin makon da ya gabata, ya nuna cewa, cikin adadin kashi…
Read More