Ra’ayin Manhaja

Tushen Zamfara da Zamfarawa

Tushen Zamfara da Zamfarawa

Daga MAHDI MUSA MUHAMMAD Blueprint Manhaja ta binciko tare da tattaro bayanai daga wuraren daban-daban dangane da asalin Zamfara da Zamfarawa. Zamfara ta kasance ɗaya daga cikin masarautun asali na Hausawa. Ta kasance ana lissafata ɗaya daga cikin Banza Bakwai waɗanda ba Hausawan asali ne ba. Dalilin hakan shi ne, ana ganin Bare-bari ne asalin Zamfara. Sarkin musulmi Muhammadu yana ganin Zamfarawa sun samu asali ne daga uba Bakatsine da uwa Bagobira. To su Zamfarawa sun kafa asalinsu daga Maguzawa maharba waɗanda sun zauna a yankin ƙasar Kano kafin zuwan Bagauda tun kafin zuwan Barbushe a Dutsen Dala. A nan…
Read More
Wacce riba ’yan Nijeriya suka samu daga mulkin dimukraɗiyya?

Wacce riba ’yan Nijeriya suka samu daga mulkin dimukraɗiyya?

Daga ABBA ABUBAKAR YAKUBU Shekaru 26 da kafuwar tsarin mulkin dimukraɗiyya a Nijeriya ba tare da katsewa ba, abin alfahari ne ga kowanne ɗan ƙasa, saboda ko ba komai ’yan Nijeriya suna rayuwa cikin ’yanci da walwala ba tare da ƙuntatawa da danniya irin ta mulkin soja ba. Kamar yadda muka sani shi tsarin shugabanci irin na dimukraɗiyya tsari ne da ke nufin gwamnatin jama'a wacce jama'a ke yankewa kansu shawara kan wanda zai wakilce su ko kuma ya shugabance su. Wannan wani tsari ne da jama'a ke da 'yanci ta fuskar siyasa wanda ya dogara kan tsarin gudanar da…
Read More
Damfara a intanet

Damfara a intanet

Babu makawa ga duk mai mu'amala da yanar gizo (Internet) ko wayar salula ya san matakan kariya game yadda waɗansu ɓata gari ke baza tarko ta ko wacce irin dama su ka samu don su damfari jama'a. Idan muka ce yanar gizo to anan mu na nufin Ko wanne fanni na yanar gizo. Shin kai ma'abocin burauzin ne don karanta labarai, ko mai binciken ilmi, ko ma'abocin kafofin sada zumunci da dai sauran su. Yau za mu kawo hanyoyin da su ka fi shahara wajen yin damfara a yanar gizo, kuma sanin su zai taimaka ma wajen tsallake tarkon su,…
Read More
Barazanar ambaliyar ruwa a Nijeriya

Barazanar ambaliyar ruwa a Nijeriya

A yayin da Nijeriya ke ci gaba da fuskantar barazanar ambaliya ruwa a sassa dabab-daban, gwamnatin ƙasar ta ce ba ta da haufin ingancin madatsun ruwan da Nijeriyar ke da su. Gwamnatin Nijeriya ta jaddada ƙudirinta na daƙile illolin ambaliyar ruwa a faɗin Nijeriya, domin kare rayuka da dukiyoyin ’yan ƙasar. Sakataren gwamnatin tarayya, Sanata George Akume ne ya bayyana hakan a wani taro da ministoci da manyan jami’an ma’aikatu da hukumomin da abin ya shafa kan rigakafin magance illar ambaliyar ruwa a Nijeriya. Akume, wanda ya samu wakilcin babban sakatariyar ayyuka, Dr Nnamdi Maurice Mberi, ya yaba wa ƙoƙarin…
Read More
Hanyoyin magance hatsarin tankuna mai a hanyoyinmu

Hanyoyin magance hatsarin tankuna mai a hanyoyinmu

Daga HASSAN IMRAN  A makon da ya gabata, aka samu wani hatsarin tankar man fetur da ta kife a kan hanyar Dikko da ke Ƙaramar Hukumar Gurara a Jihar Neja. Tashar Talabijin ta Channel ta rawaito cewa an yi asarar rayuka saba'in da bakwai. Haka zalika, wasu da suka raunata an garzaya da su zuwa asibitin gwamnati da ke Suleja a inda ake jinyarsu. Harwayau, an sake wata gobarar tankar mai a ranar Asabar da ta wuce a garin Inugu a yayin da aka rawaito cewa an yi asarar rayuka sha takwas kuma an samu damar kuɓutar da mutane goma…
Read More
Me ya bambanta mu da dabba?

Me ya bambanta mu da dabba?

Daga ALI ABUBAKAR SADIQ Da ni da kai da sauran dabbobi duk mu na da kwakwalwa, amma abinda ya banbanta mu da dabbobi shine kwakwalwarmu na da hankali, wannan hankali idan muka yi amfani da tunani sai ya banbance mana aya da tsakuwa, fari da baki, mai kyau da mara kyau. Shi yasa Allah ya ce mana cikin Q38:29 "(Wannan) Littãfi ne, Mun saukar da shi zuwa gare ka, yanã, mai albarka, dõmin su lũra da ãyõyinsa, kuma don mãsu hankali su riƙa yin tunãni." Wato duk wani Dan Adam (idan banda maras lafiya - wato mahaukaci, ko yaron da bai…
Read More
Aure da saki a fim: Gangan ko gaske?

Aure da saki a fim: Gangan ko gaske?

Daga ALI ABUBAKAR SADIK Maganar aure ko saki a fina-finan Kannywood ta fara zama abin tattaunawa tsakanin malamai a yan shekarun nan. A bara, wasu malamai sun yi bayanin fatawar cewa Idan ka saki mace a fim ta saku. A bana ma, wannan zance ya sake dawowa ana ta cece-kuce a kansa, har ma da zancen ridda a fim. Na farko dai abinda ya kamata mu fara ganewa shine kamar yadda Manzo ya fada "Haram a bayyane ta ke, haka shi ma halal a bayyane ya ke". Sannan Allah ya bada hukunce-hukunce cikin ƙurani wadanda da su malamai ke gwamutsawa…
Read More
Koyarwar  malaman ƙasar Hausa a da da yanzu

Koyarwar  malaman ƙasar Hausa a da da yanzu

Daga MUBARAK UMAR A shekarun baya, malamai sun fi mayar da hankali kan koyar da al'umma ibada, wadda ita ce tushen addini da za ta tsallakar da mutane ranar lahira. Makarantu Islamiyya da majalisin karatu, za ka samu duk an fi mayar da hankali kan ibada, amma a yanzu, an fi mayar da hankali kan wasu abubuwa da ba su kai ibada muhimmanci ba, matasa da yawa ba su san, ko sun manta yadda ake gyaran sallah idan aka samu akasi ba. A yankin nan namu aka samu yaron da a kotu aka tambaye shi shika-shikan Musulunci, kowa ya ga…
Read More
Guzurin tattaunawar Tinubu da manema labarai

Guzurin tattaunawar Tinubu da manema labarai

A ranar Litinin da ta gabata ne shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya karɓi baƙuncin wasu ’yan jarida a gidansa da ke Legas domin tattaunawa da su wanda ya ɗauki kusan awa ɗaya ana yi. Wannan shi ne karon farko na irin wannan mu’amala da ’yan jarida da ya taɓa yi tun bayan da ya hau kan karagar mulki a ranar 29 ga Mayu, 2023. Tattaunawar shugaban ƙasa da ’yan jarida ya kasance abin da aka saba yi a lokacin mulkin Shugaba Olusegun Obasanjo. Tattaunawar ta ba shi damar yin magana kan wasu muhimman batutuwan ƙasa. Har ila yau, ta…
Read More
Matsalar tsaro da tattalin arzikin Dala Tiriliyan ɗaya

Matsalar tsaro da tattalin arzikin Dala Tiriliyan ɗaya

Manufar Gwamnatin Tarayya na samar da Dala Tiriliyan ɗaya na tattalin arzikin ƙasa ba zai yiwu ba idan har aka cigaba da samun taɓarɓarewar matsalar rashin tsaro a ƙasar. Mafita ita ce jami’an tsaro su gaggauta ɗaukar mataki tare da tabbatar da cewa an fatattaki ’yan bindiga da sauran miyagun da ke ta’addanci a ƙasar. Shugaba Bola Tinubu ya bayyana haka ne a lokacin da yake jawabi ga hafsoshin tsaro da shugabannin hukumomin leƙen asiri a wani taron tsaro da shugaban ƙasa ya gudanar kwanan nan a fadar shugaban ƙasa da ke Abuja. A cewar shugaban, yayin da ake samun…
Read More