Karon farko cikin shekaru biyu Tinubu zai halarci babban taron Majalisar Ɗinkin Duniya

Spread the love

Shugaba Bola Tinubu ya tabbatar da cewa zai halarci taro Babban Taron Majalisar Ɗinkin Duniya (UN General Assembly) karo na 81 da za a gudanar a watan Satumba.

Ana sa ran Shugaba Tinubu zai gabatar da jawabi a gaban shugabannin ƙasashe da wakilan duniya, inda zai yi bayani kan sauye-sauyen da gwamnatinsa ta aiwatar da kuma irin nasarorin da Nijeriya ta samu a fannonin tattalin arziki, gudanar da mulki da sauran muhimman gyare-gyare.

Taron na ɗaya daga cikin manyan tarukan duniya da ke haɗa shugabannin ƙasashe domin tattauna batutuwan da suka shafi zaman lafiya, tsaro, ci-gaban tattalin arziƙi da haɗin-gwiwa tsakanin ƙasa-da-ƙasa.

Haka kuma, shugaban ƙasar na sa ran amfani da wannan dama wajen bayyana matsayin Nijeriya akan muhimman batutuwan duniya tare da ƙarfafa dangantakarta da sauran ƙasashen duniya.

By Babaji

Leave a Reply