Babaji

4993 Posts

Ma’aikatar kuɗi ta ɗora wa NNPCL laifin ɓatan bayanai yayin da majalisa ke binciken aron Dala 3bn da kuɗaɗen NLNG

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Ma'aikatar Kuɗi ta Tarayya ta ɗora wa Babban Kamfanin Man Fetur na Ƙasa (NNPCL) laifi bisa rashin gabatar da rahotannin bayanan da ake buƙata don warware tambayoyin kuɗaɗe da aka yi a rahoton shirin tabbatar da gaskiya da adalci kan kuɗaɗen masana'antun fitarwa (NEITI) na mai da gas na 2021 zuwa 2023. Babban Sakataren ma'aikatar, Raymond Omachi ne ya bayyana haka a ranar Alhamis yayin bayyana a gaban kwamitin binciken kuɗaɗen al'umma na Majalisar Dattawa, inda yake amsa tambayoyi kan rashin fahimtar haƙiƙanin yadda aka sarrafa wasu kuɗaɗe daga rahoton NEITI. Daga cikin ababen…
Read More

NAHCON ta amince da kamfanoni biyar don jigilar hajjin 2027

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Hukumar Jigilar Alhazan Nijeriya NAHCON, ta amince da kamfanonin jiragen sama guda biyar da za su gudanar da jigilar mahajjatan ƙasar yayin harkokin aikin Hajjin shekarar 2027. NAHCON ta sanar da haka ne wata sanarwa da ta fitar a ranar Alhamis. Ta ce, kamfanonin da aka amince da su sun haɗa da Air Peace Limited, Flynas, Max Air Limited, Saudi Air da UMZA Aviation Services Limited. A cewarta, an zaɓi kamfanonin ne bayan tantance su da kwamitin tantance kamfanonin jiragen sama ya gudanar, bisa la’akari da ƙa’idojin tsaro, ƙarfin matakin gudanar da aiki da…
Read More

‘Yan bindiga sun halaka matafiya tara a Neja

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja 'Yan sanda sun gano wasu gawarwaki na mutane guda tara waɗanda ake zargin 'yan bindiga ne suka halaka su a akan hanyar Wawa zuwa Lumma da ke Ƙaramar Hukumar Borgu ta Jihar Neja. Kamfanin Dillancin Labarai (NAN) ya ruwaito cewa jami'an 'yan sanda da sojoji da aka tura yankin sakamakon aun labarin ne suka gano a ranar Talata. Kakakin rundunar 'yan sandan jihar, SP Wasiu Abiodun, ya tabbatar wa NAN a Minna cewajami'an tsaron sun kwashe gawarwakin daga wurin, yayin da aka ƙara tsaurara ayyukan sintiri da bincika wuraren da ake zargin 'yan bindiga…
Read More

‘Yan bindiga sun sace mutum shida bayan halaka biyu a Katsina

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja An halaka mutane biyu sannan an yi garkuwa da wasu guda shida a Unguwar Aminu da ke Gundumar Kandarawa ta Ƙaramar Hukumar Bakori a Jihar Katsina. Haka kuma, wasu mazauna su huɗu sun samu raunukan harbin bindiga yayin harin, wanda ya auku a ranar Talata da dare, kamar yadda wani rahoton Daily Trust ya bayyana. Jaridar ta ce waɗanda aka halaka sune Ibrahim Sama'ila da Mashakuru Isa, inda tuni aka yi musu jana'iza a ranar Laraba kamar yadda addinin Musulunci ya tanada. Waɗanda aka sace a ɗaya gefen sun haɗa da maza uku da…
Read More

Masu haƙar ma’adinai bakwai sun rasu yayin da ƙasa ta rufta a Filato

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja 'Yan aikin haƙar ma'adinai guda bakwai sun rasa rayukansu bayan ƙasa ta haɗe da su a ƙauyen Kassa da ke Ƙaramar Hukumar Barkin Ladi ta Jihar Filato. Wani ɗan yankin mai suna Albert Ɗanlami ya shaida wa manema labarai cewa masu aikin sun haɗu da ajalinsu ne bayan da ƙasar wajen ta rufta akansu, lamarin da ya sa mazauna da sauran abokan aikinsu suka gaggauta yunƙurin ceto su. Ya ce, al'amarin ya haifar da firgici a ƙauyen yayin da mazauna suka gaggauta zuwa yankin domin bayar da agajin gaggawa kan al'amarin, inda a sanadiyyar…
Read More

Super Falcons ta rasa damar shiga gasar Kofin Duniya karo na farko a sama da shekara 30

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Tarihin Nijeriya na shiga kowanne gasar Kofin Duniya ta mata tun da aka fara a 1991 ya haɗu da cikas bayan tawaga Super Falcons ta gaza samu damar shiga na 2027. A daren Alhamis wayewar Juma'a a Casablanca ne Banyana Banyana ta Afirka ta Kudu ta doke Nijeriya da ci 2 da 1, lamarin da ya sa 'yan Super Falcons ɗin suka gaza samun gurbi a gasar 2027 FIFA Women's World Cup. Da fari dai Super Falcons ta yi fatan farfaɗowa daga cire ta da aka yi a zangon wasannin dab da na kusa…
Read More

Ribaɗu ya jagoranci tawagar Nijeriya zuwa Amurka taron tattauna dabarun daƙile matsalolin tsaro

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Mai Bai wa Shugaban Ƙasa Shawara akan Harkar Tsaro (NSA), Nuhu Ribaɗu ya jagoranci wata tawaga da gwamnatin Nijeriya ta shirya domin zuwa ƙasar Amurka halartar taron haɗaka tsakanin ƙasashen biyu, wanda aka gudanar a Birnin Washington D.C. Zaman ya mayar da hankali ne akan haɗin kan lamuran daƙile ayyukan ta'addanci, nasarorin da aka samu zuwa yanzu da matakai na gaba da za ɗauka wajen ƙarfafa alaƙar tsaro tsakanin ƙasashen. An gudanar da taro ne a ranar Alhamis, wanda kuma ya biyo bayan ayyana Nijeriya a matsayin ƙasar da ake damuwa akanta (CPC) da…
Read More

Hukumar alhazan Kano za ta rufe karɓar kuɗin Hajjin 2027 a 25 ga Agusta yayin da ta ƙayyade farashi

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Hukumar Jigilar Alhazai ta Jihar Kano ta sanar da cewa Naira miliyan 7 ne ƙayyadadden farashin aikin Hajjin 2027 ga maniyyata dafa sassan jihar. Darakta-Janar na hukumar, Abubakar Ibrahim Matawalle ne ya sanar da haka a wata takarda, ranar Talata. A cewar hukumar, 25 ga watan Agusta, 2026 na nan a matsayin ranar ƙarshe ta biyan kuɗin rajistar Hajjin na 2027. "Baki ɗaya waɗanda ba su miƙa fasfo ɗinsu na ƙasa-da-ƙasa ba, su yi hakan kafin wa'adin ya cika. Kiyaye wa'adin na da muhimmanci wajen shigar da bayanai yadda ya dace da kuma tabbatar…
Read More

‘Yan sanda ceto ɗan shekara 10 bayan kama mutum biyu bisa zargin garkuwa a Sakkwato

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Rundunar 'Yan sanda a Jihar Sakkwato ta yi nasarar cafko wasu mutum guda biyu bisa zargin su da hannu a ayyukan garkuwa da mutane a tisaye mabambanta da kuma ceto wani yaro ɗan shekara 10 da aka yi zargin an sace shi ne a jihar. Rundunar ta ce ɗaya daga cikin waɗanda ake zargin, mai suna Abdullahi Buba da aka sani da "Osho", mamba ne a wata sananniyar dabar garkuwa a sassan Jihar Sakkwato. Kakakin rundunar, DSP Ahmad Rufa'i, ya ce an kama Buba ne a ranar 8 ga Agusta yayin wani samame da…
Read More

Gwamnan Kebbi ya naɗa shugabanci bayan samar da sabuwar gunduma

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Gwamna Nasir Idris na Jihar Kebbi ya amince da samar da sabuwar gunduma da ta ƙunshi ƙauyuka guda takwas a Ƙaramar Hukumar Dandi da ke jihar. Haka kuma, gwamnan ya amince da samar da sabon jagorancin ƙauye a Ƙaramar Hukumar Augie a matsayin wani ɓangare na ƙarfafa gwamnatin gargajiya da inganta shugabanci daga tushe a jihar. Kwamishinan Harkokin Ƙananan Hukumomin da Sarauta, Alhaji Garba Umar Dutsinmari ne ya sanar da haka a wata takarda a Birnin Kebbi, ranar Alhamis. A cewar kwamishinan, an kafa sabuwar Gundumar Buma ne daga Gundumar Dolekaina ta Ƙaramar Hukumar…
Read More