Babaji

5132 Posts

Garkuwar Woro: Mutane 146 sun koma cikin iyalansu bayan wata bakwai

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja A ranar Juma'a Mazauna yankunan Woro da Kaiama a Jihar Kwara suka yi cincirindo domin tarbar mutanen Woro 146 da aka yi garkuwa da su, inda suka shiga rawa, kiɗa da murna yayin sake haɗuwa da su. Jama'a da dama sun yi maraba lale da ganin 'yan uwa da abokansu tare da zubar da ƙwallar farin ciki. Rahotanni sun bayyana cewa, gwamnatin Jihar Kwara ta ba wa waɗanda abin da ya shafa tallafin Naira miliyan 80 bayan kwana 21 ana duba lafiyarsu. An ba wa kowane ɗaya daga cikinsu N200,000 zuwa miliyan N1, inda…
Read More

An halaka ‘yan ta’adda 26, sojoji huɗu sun jikkata yayin da dakaru suka daƙile hari a Borno

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Dakarun tsaro na Atisayen Haɗin Kai a Arewa maso Gabas, sun yi nasarar halaka 'yan ta'adda guda 26 yayin daƙile wani hari a Jihar Borno, kamar yadda masanin harkar tsaro, Zagazola Makama ya bayyana a wani rahoto. Al'amarin ya faru ne a yankin ƙauyen Kadiya da ke Ƙaramar Hukumar Kukawa a daren Juma'a wayewar Asabar. A cewar rahoton, 'yan ta'addan sun yi arangama ne da dakarun tsaron Bataliya ta 101 sojoji na musamman da misalin ƙarfe 10:45 na daren yayin yunƙurin kai wa yankin farmaki. Wasu majiyoyin soji sun shaida wa Makama cewa sojojin…
Read More

Rasha ta taka gagarumar rawa yayin da sabon yunƙurin juyin mulkin Nijar ya tada ƙura

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Al'amarin rikicin sojojin Nijar ya sa an samu sabon yunƙuri dagula lamuran ƙasar, inda sojojin Rasha suke cigaba da taka muhimmiyar rawa, shekaru uku bayan Janar Abdourahamane Tchiani ya haye kan karagar mulki a wani juyin mulki. Gwamnatin ƙasar ta ce sojojinta sun yi nasarar daƙile wani hari da aka kai kan sansanin sojoji na Diori Hamani International Airport, Air Base 101 da ke birnin Niamey da wasu muhimman wurare a babban birnin kasar a ranakun 28 da 29 ga Agusta. Wannan al'amari ya janyo fargabar yunƙurin samun wani juyin mulki, yayin da wasu…
Read More

Gwamnatin Nijar ta ce an samu kwanciyar hankali bayan boren sojoji a Niamey

Gwamnatin Nijar ta ce dakarun tsaron ƙasar sun daƙile wani hari da aka kai kan sansanin sojoji na Base 101 da ke birnin Niamey da wasu muhimman wurare a babban birnin kasar. Ministan tsaron ƙasar, Janar Salifou Modi, ya ce maharan sun kai hari ne a wasu wurare masu muhimmanci a birnin Niamey, amma jami'an tsaro sun yi gaggawar mayar da martani. A wata sanarwa da ya fitar a ranar Asabar, Janar Modi ya ce: “Gaggawar martanin jami’an tsaro da na tsaron kasa ya taimaka wajen dakile wannan yunkuri, tare da dawo da iko da wurin sannu a hankali.” Ministan…
Read More

Da Ɗumi-Ɗumi: Tinubu ya tafi Turai hutun mako uku yayin yaƙin neman zaɓen 2027

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja A yau Lahadi Shugaba Bola Ahmed Tinubu zai bar Abuja domin zuwa Nahiyar Turai don fara hutunsa na shekara mai tsawon sati uku. Shugaban zai yada zango ne a Landon, Birtaniya, inda zai gudanar da wani kaso na hutun nasa. Kakakinsa Bayo Onanuga ne ya faɗi haka a wata takarda da ya fitar a ranar Lahadi, 30 ga Agusta, 2026. A cewar sanarwar, shugaban ƙasar zai dawo Nijeriya ne bayan kammala hutun domin cigaba da yaƙin neman zaɓen shugaban ƙasa da za a fafata a Junairun 2027. Ya ce, Landon ne birni na farko…
Read More

‘Yan bindiga sun sace basarake bayan halaka mutum uku da raunata biyar a sabon harin Kano

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja An halaka mutane uku, raunata wasu biyar da kuma garkuwa da Sarkin Noma na Jihar Kano, Alhaji Yusuf Nadabo Chiromawa a lokacin da wasu 'yan bindiga suka kai farmaki a garin Chiromawa da ke Ƙaramar Hukumar Garun Malam da ke jihar. Al'amarin ya faru ne da misalin ƙarfe 11 na daren Asabar wayewar Lahadi, a cewar Shugaban Ƙaramar Hukumar Garun Malam, Alhaji Aminu Salisu Kadawa, wanda ya tabbatar da aukuwar lamarin. Kadawa ya ce, 'yan bindigar sun kai wa yankin farmaki ne, inda suka je gidan sarkin noman kai-tsaye tare da buɗe wa jama'a…
Read More

Matatar Ɗangote ta ƙara farashin fetur karo na uku cikin kwana takwas

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Kamfanin Matatar Ɗangote ya sake ɗaga farashin lita fetur inda ya yi ƙarin Naira 65, kwana uku da ƙarin baya. Rahotanni sun bayyana cewa ƙarin na yanzu ya ɗage farashin matatar daga N1,200 zuwa N1265 ga kowacce lita, wanda zai fara aiki daga yau Lahadi, 30 ga Agusta. Wannan shi ne karo na uku da matatar take ƙara farashi cikin kwana takwas, wato hakan ya nuna cewa an samu karin N100, wanda ke wakiltar kaso 8.6. An bayyana wannan mataki ne a wata sanarwa da matatar ta fitar, wadda jaridar PUNCH ta samo a…
Read More

‘Yan bindiga sun buƙaci fansar miliyan N20 ga kowane ɗan hidimar ƙasa da suka sace a hanyar Abuja

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja 'Yan bindiga da suka yi garkuwa da wasu 'yan hidimar ƙasa (NYSC) kwanaki uku da su gabata sun nemi a biya Naira miliyan 20 ga kowane ɗaya daga cikinsu a matsayin kuɗin fansa, yayin da iyalai suka yi wa Gwamnatin Tarayya da hukumomin tsaro majiyar a ƙoƙarta ceto su. Rahotanni sun bayyana cewa masu hidimar ƙasar suna daga cikin fasinjojin da ke kan hanyar tafiya Abuja daga Jihar Bayelsa bayan kammala karɓar horon sati uku a sansanin NYSC da ke jihar, waɗanda aka yi awon-gaba da su a yankin babban titin Aloma zuwa Eganeda…
Read More

Sarki Sanusi na II ya ƙirƙiri hawan mauludi a masarautar Kano

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja A ranar Asabar Sarkin Kano na 16, Muhammadu Sanusi na II ya jagoranci hawan maulidi karo na farko a tarihin Masarautar Kano, yayin da dubunnan mutane suka taru don bikin murnar haihuwar Annabi Muhammad (SAW). Sarkin ya je wajen taron ne da misalin ƙarfe 4:40 na yamma a sukwane kan dokinsa ta cikin unguwannin daɗaɗɗen birnin yayin da yake karɓar gaisuwa daga mazauna. Sarkin ya fara tattakin nasa ne daga Ƙofar Kwaru sannan ya bi ta hanyar Mandawari zuwa Kwanar Ɗiso da Galadanci kafin zagaye yankunan Gwale, inda aka samu tarin dandazon jama'a na…
Read More

Iƙirarin Tinubu ya kai shekara 90 rashin abin faɗa ne – Fadar Shugaban Ƙasa ga Atiku

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Babban Mashawarcin Shugaban Ƙasa kan Harkokin Yaɗa labarai da Hulɗa da Jama’a, Temitope Ajayi, ya bayyana iƙirarin tsohon Mataimakin Shugaban ƙasa Atiku Abubakar cewa Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya kai shekara 90 a duniya a matsayin "harin ƙarshe na doki mai shure-shuren mutuwa". Ajayi ya bayyana haka ne yayin mayar da martani ga kalaman ɗan takarar shugaban ƙasar na jam'iyyar ADC da ya yi su a wata hira da BBC, inda ya yi zargin cewa Shugaba Tinubu "ɗan shekara 90" ne. Mashawarcin shugaban ƙasar ya bayyana hakan a matsayin zumuɗin son zama shugaban ƙasa…
Read More