Babaji

4771 Posts

Gbajabiamila ya maka Adeyemi a kotu kan zargin ɓatanci, ya nemi a biya diyyar biliyan N15

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Shugaban Ma'aikatan Fadar Shugaban Ƙasa, Femi Gbajabiamila, ya shigar da ƙara a kotu akan Frins Adeniyi Adeyemi Matthew da ake zargi da bayyana kansa a matsayin Darakta Janar na hukumar bogi ta PFIPC akan zargin sa da yaɗa kalaman ɓata suna. A cikin ƙarar, wadda Gbajabiamila ya shigar a Babbar Kotun Tarayya, ya buƙaci a tilasta wa wanda ake ƙara ya biya shi diyyar Naira biliyan 15.2 na dameji, yana mai cewa zarge-zargen da aka yi masa na neman cin hanci ƙarya ne da ta janyo masa zubewar mutunci da martabarsa a idon al'umma.…
Read More

‎Tsohon Sufeto-Janar na ‘yan sanda, Suleiman Abba ya koma PDP

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja‎‎Tsohon Sufeto-Janar na Rundunar 'Yan Sanda, Suleiman Abba, ya fice daga jam'iyyar APC tare da komawa jam'iyyar adawa ta PDP.‎‎Abba ya sanar da sauya sheƙarsa ne a wani taron siyasa da aka gudanar a Bamaina da ke Jihar Jigawa, inda tsohon gwamnan jihar, Sule Lamido, da shugabannin PDP suka tarbe shi tare da magoya bayansa.‎‎Ya bayyana cewa, ya ɗauki matakin koma wa PDP ne domin neman kujerar Sanatan mazaɓar Jigawa ta Kudu maso Yamma a zaɓen shekarar 2027, yana mai cewa jam'iyyar ce yake ganin za ta ba shi damar wakiltar al'ummar yankin yadda ya…
Read More

Kotu ta umarci a ƙwace kadarorin Aisha Achimugu na biliyoyin naira

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Wata Babbar Kotun Tarayya da ke yankin Apo a Abuja, ta umarci da a karɓe kadarorin da aka danganta su da 'yar kasuwa, Aisha Achimugu tare da damƙa su ga Gwamnatin Tarayya. Rahotanni sun bayyana cewa, ababen da kotun ta umarci a ƙwace sun haɗa da saraƙuna masu darajar Naira biliyan 4.645, motocin alfarma guda 11 masu darajar biliyan N4.293, Dala 50,000 na tsabar kuɗi da kuma ƙarin wasu miliyan N30. Mai Shari'a Jude Onwugbuzie ne ya bayar da umarnin a ranar Alhamis, 16 ga watan Yuli, 2026 yayin gabatar da hukunci akan ƙara…
Read More

Majalisar Dattawa ta tabbatar da Fasina a matsayin jakada duk da bijirewar wasu sanatoci

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Majalisar Dattawa ta tabbatar da Abayomi Sunday Fasina a matsayin jakadan Gwamnatin Tarayya baƙo a fannin jakadanci duk da nuna rashin amincewa daga ɓangaren wasu 'ya'yanta da zanga-zanga daga ƙungiyoyin al'umma kan bayar da sunanansa. An tabbatar da shi ne bayan nazari akan rahoto da amincewar kwamitin majalisar akan harkokin waje ƙarƙashin jagorancin Sanata Sani Bello. Da yake gabatar ta rahoton kwamitin, Sanata Simon Lalong, (APC, Jihar Filato), ya yi kira ga shugabancin majalisar da ya amince da naɗin Fasina a matsayin jakadan kuma babban kwamishina bisa la'akari da bayanan da aka samu a…
Read More

‘Downloading’: Kace-nace ya ɓarke tsakanin Hisbah da hukumar tace finafinai ta Kano

Daga IBRAHIM HAMISU a Kano Hukumar Tace Fina-finai da Ɗab’i ta Jihar Kano ta ce har yanzu ba ta soke ko ta haramta sana’ar downloading a faɗin jihar ba. Hukumar ta bayyana haka ne bayan ta ce ta samu koke-koke daga masu wannan sana’a da shugabanninsu kan rahotannin da ke yawo cewa an hana gudanar da sana’ar downloading a Kano. A cikin wata sanarwa, hukumar ta ce babu wata hukuma da ta tuntube ta ko ta yi shawara da ita kafin a yaɗa irin waɗannan bayanai. Ta ce masu sana’ar downloading na daga cikin waɗanda take da alhakin sa ido…
Read More

NAHCON za ta mayar wa alhazan 2026 kuɗaɗen da ba a yi musu hidimarsu ba

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Hukumar Jigilar Alhazan Nijeriya NAHCON, ta tabbatar wa mahajjatan 2026 cewa za ta mayar musu da kuɗaɗensu da suka biya na hidimar da ba a musu ba. Da yake jawabi a taron ajandar gyara da nazari na masu ruwa da tsaki bayan kammala ayyukan hajjin, Shugaban NAHCON, Ambasada Isma'il Abba Yusuf ya ce hukumar ta fara ta fara aiki akan rahotannin kuɗaɗen da aka kashe tare da haɗin-gwiwar hukumomin Saudiyya domin tabbatar da adalci akan aikin hajjin da aka kammala a kwanan nan. Ya yi gargaɗi ga kamfanonin hidimar hajji na Nijeriya akan cewa…
Read More

Hauhawar farashin kayayyakin abinci a Nijeriya ya ragu da kaso 15.91 – NBS

Sabbin alƙaluman da Hukumar Ƙididdiga ta Ƙasa (NBS) ta fitar sun nuna cewa hauhawar farashin kayayyaki ta ragu kaɗan da kaso 15.91 a watan Yuni na shekarar 2026, idan aka kwatanta da kaso 15.93 da aka samu a watan Mayu. Sai dai duk da wannan raguwar da aka samu, rahoton ya nuna cewa farashin kayan abinci ya ci gaba da ƙaruwa, lamarin da ke ci gaba da jefa iyalai da dama cikin matsin rayuwa. Kayayyakin da aka fi samun ƙarin farashi sun haɗa da tumatir, barkono, nama, wake, garin rogo, ayaba da sauran kayan masarufi da al'umma ke amfani da…
Read More

Karon farko cikin shekaru biyu Tinubu zai halarci babban taron Majalisar Ɗinkin Duniya

Shugaba Bola Tinubu ya tabbatar da cewa zai halarci taro Babban Taron Majalisar Ɗinkin Duniya (UN General Assembly) karo na 81 da za a gudanar a watan Satumba. Ana sa ran Shugaba Tinubu zai gabatar da jawabi a gaban shugabannin ƙasashe da wakilan duniya, inda zai yi bayani kan sauye-sauyen da gwamnatinsa ta aiwatar da kuma irin nasarorin da Nijeriya ta samu a fannonin tattalin arziki, gudanar da mulki da sauran muhimman gyare-gyare. Taron na ɗaya daga cikin manyan tarukan duniya da ke haɗa shugabannin ƙasashe domin tattauna batutuwan da suka shafi zaman lafiya, tsaro, ci-gaban tattalin arziƙi da haɗin-gwiwa…
Read More

Malami na shirin ɗaukaka ƙara bayan hukuncin kotu na ƙwace kadarorinsa

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Ofishin tsohon Antoni Janar na Ƙasa kuma Ministan Shari’a, Abubakar Malami (SAN), ya ƙudiri aniyar ɗaukaka ƙara akan hukuncin Babbar Kotun Tarayya na ƙwace kadarorin Malami. Ya ce, Malami bai amince da wasu ɓangarori na gudanar da hukuncin ba don haka zai ɗaukaka ƙara a kai, yana mai umartar tawagar lauyoyinsa da su gaggauta kai lamarin Kotun Ɗaukaka Ƙara. A cewar Malami yana sa ran Kotun Ɗaukaka Ƙarar za ta yi dogon nazari akan hukuncin da kuma tabbatar da adalci a kai. A sanarwar da Mohammed Bello Doka, mai taimaka masa akan harkokin yaɗa…
Read More

Kofin Duniya: Argentina za ta kara da Sifaniya a wasan ƙarshe bayan doke Ingila

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Ƙasar Argentina ta yi nasarar hayewa zuwa zagayen wasan ƙarshe a gasar Kofin Duniya ta 2026 bayan doke Ingila da ci 2 da 1 a wasan dab da na ƙarshe a ranar Laraba. Hakan na nufin mai riƙe da kofin za ta kara da ƙasar Sifaniya a wasan ƙarshen a gasar da ke cigaba da gudana a Nahiyar Amurka. Da fari, Ingila ce ta fara zura ƙwallo a wasan a minti na 55 ta hannun ɗan wasa Anthony Gordon, lamarin da ya ba ƙasar damar jan ragamar wasan. Bayan gurmurzu na tsawon minti 30…
Read More