14
Aug
Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Ma'aikatar Kuɗi ta Tarayya ta ɗora wa Babban Kamfanin Man Fetur na Ƙasa (NNPCL) laifi bisa rashin gabatar da rahotannin bayanan da ake buƙata don warware tambayoyin kuɗaɗe da aka yi a rahoton shirin tabbatar da gaskiya da adalci kan kuɗaɗen masana'antun fitarwa (NEITI) na mai da gas na 2021 zuwa 2023. Babban Sakataren ma'aikatar, Raymond Omachi ne ya bayyana haka a ranar Alhamis yayin bayyana a gaban kwamitin binciken kuɗaɗen al'umma na Majalisar Dattawa, inda yake amsa tambayoyi kan rashin fahimtar haƙiƙanin yadda aka sarrafa wasu kuɗaɗe daga rahoton NEITI. Daga cikin ababen…
