Babaji

4771 Posts

Majalisar Dattawa za ta fara bin diddigin hazaƙar wakilai yayin kowane zama

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Majalisar Dattawa na shirin samar da wani tsari domin kula da lamuran halarta da hazaƙar sanatoci a yayin zaman majalisa, a matsayin wani ɓangare na ƙarfafa ƙoƙarinsu a harkokinta. Sanata Abdul Ningi (Jihar Bauchi) ne ya gabatar da buƙatar a ranar Laraba, inda nemi shugabancin majalisar da ta riƙa tattara rahoton halarta da gudunmawa yayin muhawara akan muhimman batutuwan majalisa. A cewarsa, yana da kyau a riƙa tantance wa da wa ne suke ƙoƙarin bayar da gudunmawa a majalisar domin ƙara wa mambobin ƙwarin-gwiwar tofa albarkacin baki da yin abin da ya dace akan…
Read More

Kotu ta umarci a ƙwace kadarorin biliyan N212.8 da aka alaƙanta da Malami na dindindin

Babbar Kotun Tarayya ta Abuja, ta bayar da umarnin ƙwace sama da kadarori guda 40 da ake danganta su da tsohon Antoni Janar na Kasa kuma Ministan Shari’a, Abubakar Malami, tare da mayar da su mallakin Gamnatin Tarayya. Mai shari’a Joyce Abdulmalik ce ta yanke hukuncin a ranar Laraba, bayan ta amince da buƙatar Hukumar EFCC, wadda ta ce Malami da sauran masu iƙirarin mallakar kadarorin sun kasa tabbatar wa kotu cewa sun mallake su ne ta hanyoyin da doka ta aminta da su. Gabanin hukuncin, kotun ta yi watsi da duk ƙorafe-ƙorafe da buƙatun da Malami, iyalansa da wasu…
Read More

Kogi: ‘Yan bindiga sun sace shugaban makaranta da ɗalibai yayin da ake tsaka da rubuta NECO

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Wasu da ake zargin 'yan bindiga ne, sun ƙaddamar da farmaki a makarantar sakandare ta Opada-Olowa da ke Ƙaramar Hukumar Dekina ta Jihar Kogi, inda suka yi awon-gaba da shugaban makaranta, jami'in sanya ido na jarrabawar NECO da ɗalibai guda huɗu. Rahotanni sun bayyana cewa, al'amarin ya fara ne da misalin ƙarfe 2 na ranar Talata yayin da ɗalibai ke tsaka da rubuta jarrabawa. Mazauna yankin sun ce, wasu 'yan bindiga cikin adadi mai yawa ne suka kutsa cikin garin, inda suka riƙa harbe-harbe domin tsorata su gabanin su kai farmaki a makarantar. A…
Read More

Zargin rashawa: Kotu ta bada belin tsohon shugaban Kotun Ɗa’ar Ma’aikata, Ɗanladi Umar kan miliyan N100

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Mai Shari'a Peter Kekemeke na Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja, ya bayar da belin tsohon shugaban Kotun Ɗa'ar Ma'aikata (CCT), Ɗanladi Umar, wanda ke fuskantar gurfanarwa akan tuhume-tuhume guda huɗu na zargin saɓa wa dokokin aiki da rashawa. Rahotanni sun bayyana cewa, Mai Shari'a Kekemeke ya ce an bada belin Ɗanladi Umar ne akan Naira miliyan 100 da kuma sharaɗin samo mutum ɗaya da zai tsaya masa da ke da shaidar mallakar wata kadara a Abuja. Hakan na nufin tsohon shugaban na CCT zai cigaba da zama a kurkukun Kuje har sai an…
Read More

Majalisar Dattawa ta tara wa iyalan malamai da ɗaliban Oyo da aka ceto miliyan N50

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Shugaban Majalisar Dattawa, Godswill Akpabio, ya sanar da tara Naira miliyan 50 a matsayin tallafi ga iyalan waɗanda garkuwar makarantun Ƙaramar Hukumar Oriire da ke Jihar Oyo ta rutsa da su a kwanan nan. Akpabio ya bayyana haka ne a yayin zaman majalisar na yau Laraba, inda ya ce tallafin na da nufin rage wa iyalan da al'amarin ya shafa raɗaɗi. A cewarsa, za a bayar da Naira miliyan 10 ga kowane ɗaya daga cikin iyalai uku na sojojin da suka rasa rayukansu yayin ceto mutanen, kamar yadda za a ba wa na malamai…
Read More

Sahun ƙarshe na ‘yan Nijeriya da aka kwaso daga Afirka ta Kudu ya iso Legas

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Jirigin ƙarshe da Gwamnatin Tarayya ta tura domin ɗebo 'yan Nijeriya guda 308 daga ƙasar Afirka ta Kudu akan matsalolin hare-haren baƙi ya iso Legas, lamarin da ya kawo ƙarshen jigilar 'yan ƙasa da suka maƙale a ƙasar. Hakan na zuwa ne sakamakon yawan kai hare-hare akan 'yan ƙasashen waje saboda ƙyamar baƙi da 'yan ƙasar kudancin Afirkan ke nunawa a wasu sassa. Rahotanni sun bayyana cewa, jirgin, wanda ya ɗebo wasu manyan jami'an gwamnati uku, ya isa filin jiragen sama na Murtala Muhammed ne da misalin ƙarfe 11:30 na safiyar Laraba. Wannan shi…
Read More

Kofin Duniya: Sifaniya ta kai wasan ƙarshe bayan doke Faransa

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Ƙasar Sifaniya ta Nahiyar Turai ta yi nasarar tsallakewa zuwa zagayen wasan ƙarshe a gasar Kofin Duniya na 2026 bayan doke Faransa da ci 2 da 0. 'Yan wasa Mikel Oyarzabal da Pedro Porro ne suka zura ƙwallayen da suka kori 'yan koci Didier Deschamps a wasan na dab da na ƙarshe da aka gudanar a daren jiya Talata. Wannan al'amari ya kawo ƙarshen fatan Les Bleus na lashe kofin da kuma rashin nasara a karon farko a gasar duk da cewa tana cikin ƙasashen da ke kan gaba da ake wa fatan lashe…
Read More

Kano: Da lafiya ilimi ke wanzuwa – Masanin lafiya a Bichi

Bisa la'akari da abubuwan da suke haddasa Cutar Tetanos da ake rasa rayuwar 'ya'ya mata, musamman masu juna-biyu da ake yin biyu babu wajen mutuwar uwa da ɗa a yayin naƙuda, sakamakon shigar cutar ta hanyar jin ciwo ko rauni. Jami'ar Yaɗa Labarai ta Ƙaramar Hukumar Bichi, Jamila Abdullahi Rijiyar Lemo ta rawaito, Jami'in Kula da Harkar Sadarwa da Wawala na Sashen Lafiya dake Bichi, Malam Nura Ibrahim Abubakar, ya gudanar da zama na musamman tare da Sashen Hukumar Iimi na yankin haɗi da Ƙungiyar Malamai waɗanda suka shafi ɓangaren makarantun mata a ƙaramar hukumar. Bayan ɗimbun godiya da ya…
Read More

Rigakafin Tetanos kariya ce ta tsawon rayuwa, inji masanin lafiya

An gudanar da allurar Rigakafin Ƙwayar Cutar Tetanos ga adadin yara sama da 90,000 na ɗaukacin Ƙaramar Hukumar Bichi, inda kuma ƙaramar hukumar ta kasance a cikin ƙananan hukumomi 10 da suka ciri tutar gudanar da wannan muhimmin aikin yadda ya kamata a faɗin jihar Kano. Hakan na ƙunshe ne a wata sanarwa da Jami'ar Yaɗa Labarai ta yankin, Jamila Abdullahi Rijiyar Lemo, ta raba wa manema labarai. Ta bayyana cewa, Shugaban Sashen Lafiya a Matakin Farko, Alhaji Kabir Abubakar Gwarzo, wanda ya samu wakilcin Jami'in Gudanar da Allurar Rigakafi na ƙaramar hukumar, Malam Mahmud Garba ya ce, Bichi na…
Read More

An tsinci gawa mai guntulallen kai a harabar Jami’ar Jos

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Al'umma sun girgiza a ranar Talata bayan gano wata gawar wani mutum da aka tsige wa kai a tsohuwar harabar Jami'ar Jos da ke Jihar Filato. Rahotanni sun bayyana cewa, an yi zargin waɗanda suka halaka shi sun tafi da kan nasa, inda suka bar gangan jikin kaɗai a wajen da aka ƙaddamar da farmakin. Ɗalibai da dama da ma'aikatan jami'ar ciki har da Shugaban Tsaro, Mista Agama Tangni sun tabbatar da faruwar al'amarin ga manema labarai a Jos, ranar Talata. A cewar Tangni, sun gano cewa mamacin ba ɗalibi ko ma'aikacin jami'ar ba…
Read More