Maganar Babban Kwamandan Hukumar Sibil Difens (NSCDC), Ahmed Audi, cewa sama da makarantu 60,000 daga cikin 81,000 a faɗin Nijeriya ba su da isasshen tsaro, lamari ne da ya girgiza zukata kuma ya kamata ya tayar da hankalin duk masu ruwa da tsaki.
Wannan ba ƙididdiga ce kawai ba; alama ce ta giɓin da ke barazana ga rayuka da makomar yara miliyoyi.
Audi ya bayyana hakan ne yayin karɓar baƙuncin Ministan Ilimi, Dakta Tunji Alausa, a ofishinsa da ke Abuja.
Ya yi nuni da cewa yawancin waɗannan makarantu ba su da katanga, ba su da jami’an tsaro, kuma suna buɗe ƙofa ga duk wani hari. Wannan ne ya sa NSCDC ta tsara dabarun tsaro bisa ga bayanan da ta tattara tare da miƙawa Ma’aikatar Ilimi ta Tarayya.
A cewarsa, tura rundunonin mata na musamman da kuma gina tsare-tsaren tsaro na al’umma sun taimaka wajen daƙile barazanar tsaro fiye da 110. Haka kuma, rundunar Kare Makarantu da shirye-shiryen haɗin gwiwa da al’umma sun ƙarfafa tattara bayanan sirri da ɗaukar matakin gaggawa.
A nasa ɓangaren, Ministan Ilimi ya jaddada ƙudurin gwamnati na ƙarfafa Shirin Kare Makarantu tare da NSCDC, tare da duba hanyoyin samar da kuɗaɗe masu ɗorewa domin tabbatar da tsaron makarantu ba ya fuskantar tsaiko.
Ya bayyana aniyar gwamnati na barin martanin gaggawa kawai zuwa samar da cikakken tsarin tsaro mai ɗorewa, musamman a makarantu masu rauni. Haka kuma, ya sanar da kafa sashen ‘Safe Schools’ a cikin ma’aikatar domin kula da aiwatar da shirin a ƙasa baki ɗaya, tare da ɓullo da fasahohin zamani kamar “matakan gaggawa” da ke haɗe da cibiyoyin kulawa.
An ƙaddamar da Shirin Kare Makarantu ne a 2014 bayan sace ‘yan mata a Chibok, jihar Borno, wani shiri da aka samar da haɗin gwiwar ofishin mai bai wa Majalisar ɗinkin Duniya shawara kan ilimi na duniya da kuma masu zaman kansu. Daga bisani, a Disambar 2022, gwamnatin tarayya ta fito da Tsarin ƙasa kan Tallafa wa Shirin Kare Makarantu na 2023–2026 da aka kiyasta zai ci naira biliyan 144.8, tare da kafa rundunar kariya da cibiyoyin sa ido a faɗin jihohi 36 da ƙananan hukumomi 774.
Sai dai duk da waɗannan tsare-tsare, hare-hare kan makarantu da sace ɗalibai sun ci gaba da faruwa, abin da ya sa Majalisar Dattawa ta fara bincike a kan yadda aka aiwatar da shirin duk da kuɗaɗe da alƙawurran da aka yi. Sabbin hare-hare a Kebbi da Neja sun sake jaddada cewa har yanzu makarantu na cikin haɗari.
Duk da cewa an samu ƙarin yawan makarantu da suka yi rajista a ƙarƙashin shirin, gaskiyar magana ita ce kashi 75 cikin 100 na makarantu ba su da cikakken tsaro. Wannan adadi ba zai zama abin karɓa ba a ƙasa da ke fuskantar barazanar ‘yan ta’adda da masu garkuwa da mutane.
Ra’ayinmu shi ne: ilimi ginshiƙi ne na ci gaban ƙasa. Ba za a iya barin makarantu a buɗe ga barazana ba. Jihohin da har yanzu ba su aiwatar da Shirin Kare Makarantu ba su daina jan ƙafa, su ɗauki mataki cikin gaggawa. Tsaron makaranta ba alheri ba ne; haƙƙi ne na kowane yaro ɗan Nijeriya.
Dimokuraɗiyya da ci gaban ƙasa ba su tabbata sai an kare wuraren da ake gina ilimi. Idan muka kasa kare makarantu, muna barazana ga makomar ƙasa baki ɗaya ne. Lokaci ya yi da dukkan hukumomi—na tarayya, na jihohi da na ƙananan hukumomi—za su haɗa kai domin tabbatar da cewa makaranta wuri ne na ilimi, ba na tsoro ba.
