Siyasa

An shiga ruɗani game da hukuncin kotu kan shari’ar zaɓen Gwamnan Kaduna

An shiga ruɗani game da hukuncin kotu kan shari’ar zaɓen Gwamnan Kaduna

Jama'a sun shiga halin ruɗani game da shari'ar zaɓen gwamna a jihar Kaduna. Hakan ya faru ne bayan da wani rahoto ya nuna Kotun Sauraren Ƙararrakin Zaɓe na Gwamnan Jihar ta ayyana zaɓen a matsayin wanda bai kammala ba. Bayan kimanin awa guda da fitan rahoton, sai aka sake ganin wani rahoto na daban na cewa, kotun ta tabbatar da nasarar da Gwamna Uba Sani ya samu a zaɓen wanda hakan ke nuni da shi ne zaɓaɓɓen gwamnan jihar. Da yake yi wa Jaridar News Point Nigeria ƙarin haske game da hukuncin ta waya, lauyan Gwamna Sani, Ibrahim H O…
Read More
Da Ɗumi-ɗumi: Kotu ta ayyana zaɓen gwamnan Kaduna ‘Inconclusive’

Da Ɗumi-ɗumi: Kotu ta ayyana zaɓen gwamnan Kaduna ‘Inconclusive’

Kotun Sauraren Ƙararrakin Zaɓen Gwamnan Jihar Kaduna, ta ayyana zaɓen gwamnan jihar da ya gudana ran 18 ga Maris a matsayin wanda bai kammala ba, wato 'inconclusive.' Kotun ta ayyana hakan ne a zaman yanke hukunci kan shari'ar da ta yi a ranar Alhamis. Kotun, ƙarƙashin jagorancin Mai Shari'a Victor Oviawe ta bai wa Hukumar Zaɓe ta Ƙasa INEC, da ta gudanar da zaɓen cike giɓi a cikin kwana 90. Da wannan hukuncin, ana sa ran INEC ta sake shirya zaɓe a gundumomi bakwai a tsakanin ƙananan hukumomi huɗu kuma a rumfunan zaɓe 24 masu ɗauke da masu kaɗa ƙuri'a…
Read More
Shari’ar siyasar Kano: Inda jami’yyar NNPP mai mulki ta kuskure

Shari’ar siyasar Kano: Inda jami’yyar NNPP mai mulki ta kuskure

Daga ABDULAZIZ TIJJANI BAQO A matsayina na ɗan NNPC kuma ɗan kwankwasiyya cikakke, ga mahangata a game da hukuncin da kotu ta yanke a kan shari'ar da ake tafkawa a tsakanin jam'iyyarmu ta NNPP da kuma APC. Bayan karanta kes ɗinmu da APC daga farko zuwa ƙarshe, ba ni da wani haufi a kan cewa lauyoyinmu su suka yi mana illa a wannan kes din. Sun yi iya bakin ƙoƙarinsu. Amma kuskuren da suka yi wurin laƙantar doka ya jawo mana matsala. Kusan gabaɗaya kariyar da suka bayar ta dogara ne da roko kotu ta yi watsi da hujjojin da…
Read More
Da Ɗumi-ɗumi: Kotu ta tabbatar da Yahaya a matsayin zaɓaɓɓen Gwamnan Gombe

Da Ɗumi-ɗumi: Kotu ta tabbatar da Yahaya a matsayin zaɓaɓɓen Gwamnan Gombe

Kotun Sauraren Ƙararrakin Zaɓen Gwamnan Jihar Gombe ta tabbatar da Gwamna Muhammadu Inuwa Yahaya a matsayin wanda ya lashe zaɓen gwamnan jihar. Yayin zamanta a ranar Talata, kotun ta yi watsi da ƙarar da aka shigar inda ake ƙalubalantar nasarar lashe zaɓen da Yahaya ya yi. 'Yan takaran jam'iyyun hamayya a jihar, wato Jibrin Barde na PDP da Nafiu Bala na ADC, su ne suka shigar da ƙarar inda suka nuna rashin gamsuwarsu da sake zaɓen Inuwa Yahaya da Mataimakinsa, Manassah Daniel Jatau da aka yi a matsayin shugabannin jihar ƙarƙashin Jam'iyyar APC. Duka alƙalan kotun su uku, sun yi…
Read More
Shugabancin Legas: Gwamna Sanwo-Olu ya yi nasara a kotu

Shugabancin Legas: Gwamna Sanwo-Olu ya yi nasara a kotu

Kotun Sauraren Ƙorafe-ƙorafen Zaɓen Gwamna a Jihar Legas, ta tabbatar da Gwamna Babajide Sanwo-Olu a matsayin wanda ya lashe zaɓen gwamnan jihar. Da yake karanto hukuncin a madadin sauran alƙalan yayin zaman kotun a ranar Litinin, Mai Shari'a Mikail Abdullahi ya ce ƙarar da Jam'iyyar PDP da ɗan takararta, Olajide Adediran, suka shigar ba ta da daraja wanda hakan ne ya sa kotu ta kori ƙarar. Tuhumar da ake yi wa Gwamnan Sanwo-Olu ta haɗa da amfani da takardun bogi da kuma cewa jam'iyyarsu ta APC ba ta tsayar da shi da mataimakinsa takara bisa ƙa'ida ba. Bayan sauraren duka…
Read More
Kotu ta ayyana Alia a matsayin zaɓaɓɓen Gwamnan Binuwai

Kotu ta ayyana Alia a matsayin zaɓaɓɓen Gwamnan Binuwai

Kotun Sauraren Ƙorafe-ƙorafen Zaɓen Gwamnan Jihar Binuwai mai zamanta a Makurdi, ta tabbatar da Gwamna Hyacinth Alia na Jam'iyyar APC a matsayin zaɓaɓɓen gwamnan jihar. Kotun ta kuma yi watsi da ƙarar da Jam'iyyar PDP da ɗan takararta, Titus Uba, suka shigar inda suke ƙalubalabtar sakamakon zaɓen gwamnan jihar da ya gudana a ranar 18 ga Maris. Shugaban alƙalan kotun, Mai Shari'a Ibrahim Karaye, ya ce kotun ba ta da hurumin sauraren ƙarar kasancewar ƙorafe-ƙorafen da aka gabatar mata abu ne da ya shafi gabanin zaɓe kamar yadda yake ƙunshe a Sashe na 285 ns Dokar Zaɓe. Kotun ta ce…
Read More
Hukuncin Kotu: Za mu ƙwato ‘yancinmu a Kotun Ɗaukaka Ƙara – Gwamna Yusuf

Hukuncin Kotu: Za mu ƙwato ‘yancinmu a Kotun Ɗaukaka Ƙara – Gwamna Yusuf

Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, ya ce za su ɗukaka ƙara domin ƙwato 'yancensu. Kszalika, yi kira ga al'ummar jihar da a zauna lafiya, tare da shan alwashin zai yi amfani da hanyar shari'a wajen maido da nasarar da aka ƙwace masa. Manhaja ta rawaito a Larabar da ta gabata Kotun Sauraren Ƙararrakin Zaɓen Gwamnan Kano ta yanke hukunci kan shari'ar da ke gabanta inda ta ce Yusuf Gawuna ne zaɓaɓɓen Gwamnan Kano amma ba Yusuf Kabir ba. Kotun ta bada umarnin a janye shaidar lashe zaɓen da aka bai wa Abba Kabir na Jam'iyyar NNPP sannan a miƙa…
Read More
Da Ɗumi-ɗumi: Kotu ta ce Yusuf Gawuna ne zaɓaɓɓen Gwamnan Kano

Da Ɗumi-ɗumi: Kotu ta ce Yusuf Gawuna ne zaɓaɓɓen Gwamnan Kano

Kotun Sauraren Ƙararrakin Zaɓen Gwamna a Kano, ta tsige Gwamna Abba Kabir Yusuf na Jam'iyyar NNPP sannan ta ayyana Yusuf Gawuna na Jam'iyyar APC a matsayin wanda ya lashe zaɓen gwamnan jihar da aka guda a ranar 18 ga Maris. Bayan kammala zaɓe Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC) ta ayyana Yusuf Kabir a matsayin wanda ya lashe zaɓen. Yayin da ɗan takarar APC, Nasir Gawuna, ya taya Kabir ɗin murnar lashe zaɓen ita kuwa jam'iyyarsa ta APC garzayawa kotu ta yi don ƙalubalantar sakamakon zaɓen. Yayin zaman yanke hukuncin da kotun ta yi a ranar Laraba, alƙalan kotun sun ba…
Read More
Atiku ya ɗaukaka ƙara kan hukuncin Kotun Sauraren Ƙararrakin Zaɓe

Atiku ya ɗaukaka ƙara kan hukuncin Kotun Sauraren Ƙararrakin Zaɓe

Ɗan takarar shugabancin ƙasa na jam'iyyar PDP a babban zaɓen 2023, Abubakar Atiku, ya garzaya Kotun Ƙoli don kotun ta yi watsi da hukuncin da Kotun Sauraren Ƙararrakin Zaɓen Shugaban Ƙasa ta yanke a ranar 6 ga Satumba. A hukuncin da ta yanke, Kotun Sauraren Ƙararrakin Zaɓen ta ce Bola Ahmed Tinubu shi ne wanda ya lashe zaɓen shugaban ƙasa a babban zaɓen da ya gabata. Sai dai, Atiku ya ce kotun ta tafka kuskure a hukuncin da ta yanke ranar Talata ƙarƙashin jagorancin Mai Shari'a Haruna Simon Tsammani. Ƙarar da Atiku ya ɗaukaka ta hannun babban lauyansa, Chief Chris…
Read More
Shari’ar Gwamnan Kano: Kotu ta ayyana ranar da za ta yanke hukunci

Shari’ar Gwamnan Kano: Kotu ta ayyana ranar da za ta yanke hukunci

Kotun Sauraren Ƙararrakin Zaɓen Gwamnan Kano ta ayyana ranar Laraba ta wannan mako a matsayin ranar da za ta yanke hukunci kan shari'ar da ke gabanta inda Jam'iyyar APC ke ƙalubalantar nasarar da Gwamna Abba Kabir Yusuf na Jam'iyyar NNPP ya samu a zaɓen gwamnan jihar da ya gabata. A ranar Litinin da ta gabata Kotun ta sanar da ranar da za ta yanke hukuncin cikin sanarwar da ta aike wa ɓangarorin da shari'ar ta shafa. Sakataren lauyoyin NNPP, Barrister Bashir T/Wurzici, ya tabbatar wa Jaidar Daily Trust da hakan, yana mai cewa lallai an miƙa wa tawagar lauyoyi takardar…
Read More