Siyasa

Sauya sheƙar Ubandoma zuwa APC ta janyo cece-kuce a Sakkwato

Sauya sheƙar Ubandoma zuwa APC ta janyo cece-kuce a Sakkwato

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja  Tsohon ɗan takarar gwamnan Jihar Sakkwato a zaɓen 2023, Malam Sa’idu Umar Ubandoma, ya fice daga jam’iyyar ADC tare da komawa APC. Wannan ma cikin wata sanarwa da mai taimaka wa Sanata Aliyu Magatakarda Wamakko kan yaɗa labarai, Bashar Abubakar, ya fitar. An ce Sanata Wamakko ne, ya tarɓi Ubandoma zuwa jam’iyyar APC a gidansa da ke Asokoro a Abuja. Ubandoma, wanda ya taɓa riƙe muƙamin Kwamishinan Kuɗi da kuma Sakataren Gwamnatin Jihar Sakkwato a gwamnatin Aminu Waziri Tambuwal, ya ce salon jagorancin Sanata Wamakko da ayyukan ci gaban da Gwamna Ahmed Aliyu ke…
Read More
2027: INEC ta bai wa APC, PDP, ADC, NDC da sauran jam’iyyu damar ɗora ‘yan takararsu a shafinta

2027: INEC ta bai wa APC, PDP, ADC, NDC da sauran jam’iyyu damar ɗora ‘yan takararsu a shafinta

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja  Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta ƙasa (INEC) ta bai wa jam'iyyun siyasa tara lambobin shiga (access codes) domin su fara loda sunayen 'yan takararsu a shafin hukumar gabanin babban zaɓen shekarar 2027. Binciken jaridar Leadership ya nuna cewa jam'iyyun da suka samu lambobin sun haɗa da All Progressiɓes Congress (APC), Peoples Democratic Party (PDP), African Democratic Congress (ADC), Nigeria Democratic Congress (NDC) da wasu jam'iyyu masu rijista. Ana sa ran jam'iyyun za su yi amfani da lambobin wajen loda sunayen 'yan takararsu na kujerun Shugaban ƙasa, Majalisar Dattawa, Majalisar Wakilai da kuma gwamna…
Read More
Kudirin dokokin da suka fi haifar da hargitsi a Majalisar Dattawa cikin shekara uku

Kudirin dokokin da suka fi haifar da hargitsi a Majalisar Dattawa cikin shekara uku

Daga MAHDI MUSA MUHAMMAD Yayin da Majalisar Dattawa ta 10 ke cika shekara uku da kafa ta a wannan watan Yuni, dokokin gyaran Dokar Zaɓe da kuma Dokokin Gyaran Haraji sun kasance cikin manyan dokokin da suka fi tayar da muhawara da cece-kuce a tsakanin ’yan siyasa, ƙungiyoyin farar hula da al’ummar Nijeriya baki ɗaya. Rahotanni sun nuna cewa zuwa ranar 29 ga Afrilu, 2026, Majalisar Dattawa ta 10 ta amince da sama da ƙudurori 100 tun bayan rantsar da ita a watan Yunin 2023. Bayanan da aka samo daga tsarin bibiyar ƙudurorin majalisar sun nuna cewa wasu ƙudurori 38…
Read More
An nemi haɗin kan ‘yan ADC da suka faɗi zaɓen fidda gwani a Kebbi 

An nemi haɗin kan ‘yan ADC da suka faɗi zaɓen fidda gwani a Kebbi 

Daga JAMIL GULMA a Kebbi  Mataimakin Shugaban Jam'iyyar ADC na jihar Kebbi Alhaji Musa Muhammad Dagwaya ya nemi haɗin kan 'ya'yan jam'iyyar ADC na jihar da  ba su sami nasarar a tsayar da su takarar kujerar muƙaman siyasa ba. Ya yi wannan kira ne a wani taron masu ruwa da tsaki na jam'iyyar ADC na gundumar Kebbi ta Arewa ranar Talatar da ta gabata a garin Argungu. Alhaji Musa Dagwaya ya bayyana cewa a matsayin mu na Musulmi duk mun san duk abinda ya faru to daman rubutacce ne saboda Allah ya riga ya gama tsara komai tun farkon duniya…
Read More
Kano: APC ta tabbatar da Tsamiyar Kara a matsayin ɗan takarar Gezawa

Kano: APC ta tabbatar da Tsamiyar Kara a matsayin ɗan takarar Gezawa

Daga IBRAHIM MUHAMMAD a Kano Jam’iyyar APC ta tabbatar da Hon. Abdullahi Yahaya Tsamiyar Kara a matsayin ɗan takararta na kujerar Majalisar Jihar Kano mai wakiltar ƙaramar hukumar Gezawa a zaɓen 2027. Wakilan jam’iyyar ƙarƙashin jagorancin Ahmad Haruna Bichi tare da jami’an uwar jam’iyyar APC ta jihar Kano, wakilan hukumar zaɓe ta ƙasa, jami’an tsaro da masu ruwa da tsaki ne suka shaida tabbatar da takarar tasa. An gudanar da taron ne ranar Laraba a harabar sakatariyar APC ta Gezawa. Da yake jawabi bayan tabbatar da shi, Hon. Tsamiyar Kara ya gode wa Allah bisa wannan nasara tare da bayyana…
Read More
Ƙungiyar APC Concern Group a Nasarawa ta nuna ɓacin rai kan yadda aka gudanar da zaɓen fidda gwani

Ƙungiyar APC Concern Group a Nasarawa ta nuna ɓacin rai kan yadda aka gudanar da zaɓen fidda gwani

Daga JOHN WADA a Lafia Ƙungiyar All Progressives Congress (APC) concern group a jihar Nasarawa ta nuna ɓacin rai kan yadda aka gudanar da zaɓukan fidda gwanin jam’iyyar da aka gudanar a faɗin jihar a yanzu inda suka bayyana tsarin a matsayin zamba. A cewar ƙungiyar dukkan tsarin zaɓen da aka gudanar a jihar kawo yanzu ya cika da maguɗi kuma bai bi ƙa’idar dimokuraɗiyya da adalci ba. Da yake zantawa da manema labarai a sakatariyar ƙungiyar 'yan jaridu na jihar Nasarawa dake Lafia babban birnin jihar shugaban tawagar honorabul Abdullahi Yammani ya bayyana cewa an tsara zaɓukan da gangan…
Read More
2027: Masu ruwa da tsaki na ƙabilar Migili a Nasarawa sun roki Gwamna Sule ya ba su muƙamin mataimakin gwamna

2027: Masu ruwa da tsaki na ƙabilar Migili a Nasarawa sun roki Gwamna Sule ya ba su muƙamin mataimakin gwamna

Daga JOHN D WADA a Lafia Shugabannin ƙabilar Migili a Jihar Nasarawa sun roƙi gwamnan jihar Injiniya Abdullahi Sule da ya zaɓi ɗan asalin Migili a matsayin mataimakin wanda zai gaje shi a zaɓen 2027. Da yake jawabi a wani taron manema labarai a Lafia ranar Litinin, kwamared Sunday Aleku, mai magana da yawun matasan ƙungiyar masu ruwa da tsaki na Migili yace rokon yana da nufin tabbatar da cewa an ji muryar ƙungiyar a matakin mulki mafi girma na jihar. A cewar Aleku, mutanen Migili sun kasance masu goyon baya ga gwamnatoci daban-daban da daɗewa kuma suna taka rawar…
Read More
Zaɓen fidda gwani na APC: Hamza Sule Faskari zai yi takarar majalisar wakilai a Katsina

Zaɓen fidda gwani na APC: Hamza Sule Faskari zai yi takarar majalisar wakilai a Katsina

Daga ABDULLAHI MUHAMMAD a Katsina Masu ruwa da tsaki na jam'iyar APC ta tabbatar da takarar Hamza Sule zai wakilci al'ummar ƙananan hukumomin Faskari,Ƙankara da Sabuwa a zauren majalisar wakilai a zaɓen 2027. Bikin jaddada takarar da ya gudanar a Ƙankara da yawa daga cikin masu ruwa da tsaki na jam'iyar sun yaba da yadda kwamitin sasancin ya gudanar da aikin sa. Shugaban kwamitin sasancin Injiya Tanimu Sabuwa ya bayyana cewa masu ruwa da tsaki na jam'iyar da suka fito daga mazaɓu 31 na ƙananan hukumomin Faskari, Ƙanƙara da Sabuwa wanda suka wakilci ɗaukacin ya'yan jam'iyar suka tabbatar da takarar…
Read More
Gwamnatin Nasarawa ta kammala shirin zaɓen fitar da gwanin APC

Gwamnatin Nasarawa ta kammala shirin zaɓen fitar da gwanin APC

Daga JOHN D WADA a Lafia Gwamnan Jihar Nasarawa Injiniya Abdullahi Sule ya sanar da cewa an kammala dukkan shirye-shiryen gudanar da zaɓen fidda gwani na jam’iyya APC mai ci a jihar domin kujerun majalisar wakilai na tarayya wanda aka shirya za a gudanar a ranar Juma’a15 ga Mayu na shekarar 2026 da ake ciki a jihar. Gwamna Sule ya bayyana hakan ne yayin da yake wa manema labarai jawabi a sakatariyar ƙungiyar manema labarai ta ƙasa (NUJ) reshen jihar da ke Lafia babban birnin jihar. An wakilce gwamnan a taron ta hannun mataimakin sa na musamman kan harkokin hulɗa…
Read More
Dan takarar APC ya fashe da kuka bayan jam’iyya ta zaɓi ɗan takara ta hanyar maslaha

Dan takarar APC ya fashe da kuka bayan jam’iyya ta zaɓi ɗan takara ta hanyar maslaha

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja  Wani ɗan takarar Jam’iyyar All Progressiɓes Congress (APC), ya fashe da kuka bayan ya rasa damar samun tikitin takara, bayan da jam’iyyar ta zaɓi ɗan takara ta hanyar maslaha (consensus). A cikin wani bidiyo da ya bazu a kafafen sada zumunta, an ga ɗan takarar yana kuka tare da nuna takardar fom ɗin da ya saya, yana nuna takaicinsa kan yadda aka ba wani tikitin takarar duk da irin kuɗaɗen da ya kashe a wannan tafiya. Ya bayyana cewa ya zuba kuɗaɗe masu yawa wajen neman takarar, amma a ƙarshe aka cire shi daga…
Read More