11
Jul
Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Tsohon ɗan takarar gwamnan Jihar Sakkwato a zaɓen 2023, Malam Sa’idu Umar Ubandoma, ya fice daga jam’iyyar ADC tare da komawa APC. Wannan ma cikin wata sanarwa da mai taimaka wa Sanata Aliyu Magatakarda Wamakko kan yaɗa labarai, Bashar Abubakar, ya fitar. An ce Sanata Wamakko ne, ya tarɓi Ubandoma zuwa jam’iyyar APC a gidansa da ke Asokoro a Abuja. Ubandoma, wanda ya taɓa riƙe muƙamin Kwamishinan Kuɗi da kuma Sakataren Gwamnatin Jihar Sakkwato a gwamnatin Aminu Waziri Tambuwal, ya ce salon jagorancin Sanata Wamakko da ayyukan ci gaban da Gwamna Ahmed Aliyu ke…
