23
Aug
Daga JAMIL GULMA a Kebbi Tun bayan shari’ar da ta biyo bayan zargin takardun shaidar kammala karatun sakandare na Mataimakin Gwamnan Jihar Kebbi, Sanata Umar Abubakar Argungu, Tafidan Kabi, bayan babban zaɓen shekarar 2023, wasu jiga-jigan jam’iyyar APC da ke adawa da shi suka yi ta ƙoƙarin ganin an sauya shi daga mukaminsa. Shari’ar ta haifar da zazzafar taƙaddama, inda ’yan jam’iyyar PDP suka kalubalanci nasarar Gwamna Malam Nasir Idris da mataimakinsa Sanata Umar Abubakar Argungu. Yanzu dai rahotanni sun tabbatar da cewa an sauya Mataimakin Gwamnan Jihar Kebbi, Sanata Umar Abubakar Argungu, inda aka maye gurbinsa da Ibrahim Augie.…
