Siyasa

Zargin cushe a kasafin 2024: Yadda dakatar da Sanata Ningi ta tada ƙura a Nijeriya

Zargin cushe a kasafin 2024: Yadda dakatar da Sanata Ningi ta tada ƙura a Nijeriya

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja A Nijeriya, jam'iyyun hamayyar ƙasar sun yi Allah-wadarai da matakin da majalisar dattawa ta ɗauka na dakatar da Sanata Abdul Ningi na tsawon wata uku, bayan da ya yi wasu kalamai da ke nuna an cusa wasu kuɗi naira kusan tiriliyan huɗu, waɗanda ba a san inda aka nufa da su a kasafin kuɗin ƙasar na bana ba. Jam'iyyun hamayyar suna ganin kamata ya yi a fara da gudanar da bincike kan batun cushen kuɗin, don a tabbatar da gaskiya ko akasin zargin, kafin a ɗauki matakin dakatar da ɗan majalisar. Matakin dakatar da…
Read More
Atiku, Yari da Ningi suna yunƙurin kafa sabuwar jam’iyyar siyasa

Atiku, Yari da Ningi suna yunƙurin kafa sabuwar jam’iyyar siyasa

Daga MAHDI M. MUHAMMAD A cikin makon nan ne dai jaridar The Nation ta samu labarin cewa 'yan adawa na shirin kafa sabuwar jam’iyyar da za ta tunkari jam’iyyar APC mai mulki a babban zaɓe mai zuwa. Gabanin shekarar 2027, majiyoyi sun ce ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar PDP a zacen shekarar da ta gabata, Alhaji Atiku Abubakar, ya ƙaddamar da ƙudirin jam’iyyar da ake son a yi tare da haɗin gwiwar wasu 'yan majalisar dokokin ƙasar. An tattaro cewa, sansanin Atiku na taka-tsan-tsan da rashin haɗin kan da ke cikin babbar jam’iyyar adawa, yana tunanin cewa idan ta…
Read More
’Yar’Adua ya zama sabon shugaban Ƙungiyar Sanatocin Arewa

’Yar’Adua ya zama sabon shugaban Ƙungiyar Sanatocin Arewa

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Sanata mai wakiltar Katsina ta Tsakiya a Majalisar Dokokin Nijeriya, Abdulaziz Musa Yar’Adua, ya zama sabon Shugaban Ƙungiyar Sanatocin Arewa. An naɗa ’Yar’Adua, ɗan majalisa na jam’iyyar APC, a matsayin sabon shugaban ƙungiyar kwanaki biyu bayan dakatar da Sanata Abdul Ningi. Ningi, mai wakiltar Bauchi ta tsakiya, ya zargi babban zauren majalisar da karkatar da kasafin kuɗin shekarar 2024 har na naira tiriliyan 3.7. Duk da cewa batun ƙara kasafin kuɗi ba sabon abu ba ne a Nijeriya, amma wannan ne karon farko da wani ɗan majalisar dattawa da ya taka rawar gani wajen zartar da…
Read More
An rantsar da kantomomin riƙon ƙananan hukumomi a Kebbi

An rantsar da kantomomin riƙon ƙananan hukumomi a Kebbi

Daga JAMIL GULMA a Birnin Kebbi Ranar Talatar da ta gabata ne a Jihar Kebbi aka rantsar da ƙarin kwamishina ɗaya da shugabannin riƙo na ƙananan hukumomi 21 da ke akwai bayan rushe majalisun ƙananan hukumomin a cikin watan da ya gabata. Da yake jawabi jim kaɗan bayan kammala rantsar da shugabannin, Gwamna Nasir Idris ya yi kira ga al'ummar jihar Kebbi da su ci gaba da bai wa wannan gwamantin goyon baya don ganin ta aiwatar da ayyukan ci gaba da ta yi alƙawari a baya lokacin yaƙin neman zaɓe. "Wannan gwamnatin ta kowa da kowa ce da matasa…
Read More
Rikicin siyasar Ribas: A shirye nake na sauka daga kujerar gwamna – Fubara

Rikicin siyasar Ribas: A shirye nake na sauka daga kujerar gwamna – Fubara

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Gwamna Sim Fubara na Jihar Ribas ya bayyana aniyarsa ta barin kujerarsa domin samun dorewar zaman lafiya a jihar. Gwamnan ya bayyana hakan ne a wata tattaunawa da ya yi da AIT a ranar Alhamis, 7 ga Maris, 2024. A cewarsa, babu wata sadaukarwa da ta zarce shi da zai biya domin samun nasarar jihar. Fubara ya ci gaba da cewa akwai abubuwan da zai iya yi waɗanda za su haifar da "rikicin gaba ɗaya". Duk da haka, ikonsa na kamewa ko da yana da iko. A yayin tattaunawar, Fubara ya ce, “Babu wata…
Read More
Yadda Kakakin majalisar Bauchi ya koma muƙaminsa bayan yin murabus  

Yadda Kakakin majalisar Bauchi ya koma muƙaminsa bayan yin murabus  

Daga BAKURA MUHAMMAD a Bauchi Tsohon Kakakin Majalisar Dokoki Jihar Bauchi wanda a zaɓen gama-gari na ranar 18 ga watan Maris ta shekarar da ta gabata 2023 ya tsaya takarar zaɓen wa'adin wakilci zango na biyu, amma ya faɗi zaɓen, a ranar Laraba ya sake ɗare wa kujerar da ta shugabancin majalisar, sakamakon zaɓen cike gurbi da hukumar zaɓe mai zaman kanta (INEC) ta yi a ranar 3 ga watan Fabrairu da ya gabata.  Ɗan takarar shiga majalisar dokoki na jam'iyyar APC daga mazaɓar Ningi ta Tsakiya, Malam Khalid Ningi, shine ya ƙalubalancin zaɓen na tsohon kakakin majalisa Abubakar Yakubu…
Read More
Kakakin Majalisar Jihar Zamfara na fuskantar barazanar tsigewa

Kakakin Majalisar Jihar Zamfara na fuskantar barazanar tsigewa

Daga BASHIR ISAH Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Zamfara, Hon. Bilyaminu Moriki, na fuskantar barazanar tsigewa daga mafiya rinjayen mambobin majalisar. Ya zuwa haɗa wannan rahoto, MANHAJA ta tattaro cewar galibin 'yan majalisar na gudanar da taro a harabar majalisar da yammacin ranar Alhamis kan yadda za su tsige kakakin majalisar. Kazalika, ziyarar da wakilinmu ya kai harabar majalisar ya gano yadda aka rufe harabar majalisar da kuma girke jami'an tsaro da suka haɗa da 'yan danda da sibul difens a cikinta. Bincike ya nuna hatta sandan majalisar bai tsira ba, don kuwa an samu wasu da suka yi awon gaba…
Read More
Tsohon Gwamnan Kaduna, Ramalan Yero ya koma APC

Tsohon Gwamnan Kaduna, Ramalan Yero ya koma APC

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Tsohon Gwamnan Jihar Kaduna Mukhtar Ramalan Yero ya koma Jam'iyyar APC, watanni kaɗan bayan ficewarsa daga Jam'iyyar PDP. Ramalan Yero ya sanar da ficewar tasa ne a wani bayani da ya yi wa manema labaru, ranar Litini ta makon jiya a garin Kaduna. A bayanin nasa, tsohon gwamnan na jihar Kaduna ya ce ya koma APC ne bisa dalilai na ƙashin kansa bayan ya tattauna da wadanda ke kusa da shi a harkar siyasa. A cikin watan Oktoban shekarar 2023 ne Yero ya bayyana ficewarsa daga jam'iyyar PDP. Ramalan Yero ya riƙe gwamnan jihar…
Read More
‘Yan daba sun wargaza zaɓen fidda gwani a Edo

‘Yan daba sun wargaza zaɓen fidda gwani a Edo

Daga BASHIR ISAH Wasu 'yan daba ɗauke da makamai sun tarwatsa harabar Lushville Hotel and Suites da ke yankin GRA, Benin, inda nan ne wurin da aka shirya gudanar da zaɓen fidda gwani na Jam'iyyar APC don takarar gwamnan Jihar Edo. An ce sun wargaza shirin tattara sakamakon zaɓen ne inda suka kai wa wasu masu faɗa a ji farmaki tare kuma da ji wa 'yan jarida da dama rauni da farfasa musu kayan aiki. ’Yan Majalisa Wakilai 60 sun buƙaci a sauya fasalin Nijeriya An sake buɗe Sahad Stores a Abuja bayan shafe sa’o’i 24 a rufe Jami'in tattara…
Read More
Hukumar Zaɓe ta Katsina ta sanar da ranar gudanar da zaɓen ƙananan hukumomi

Hukumar Zaɓe ta Katsina ta sanar da ranar gudanar da zaɓen ƙananan hukumomi

Daga UMAR GARBA a Katsina Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Jihar Katsina (KATSIEC) ta saka ranar 15 ga watan Fabrairu, 2025 a matsayin ranar gudanar da zaɓukan shugabannin ƙananan hukumomi da kansilolo a jihar. Shugaban hukumar, Lawal Alhassan Faskari ne ya bayyana haka a wurin taron masu ruwa da tsaki kan zaɓen wanda ya gudana a hedikwatar hukumar dake G.R.A. A cewar shi, jam'iyyu masu rajista ne kawai za a bari su tsayar da 'yan takara a kujeru daban-daban. Alhaji Lawal Alhassan ya ce sashe na 28 na dokar zaɓen Nijeriya da aka yi wa gyaran fuska 2022 ne…
Read More