04
Jul
Daga BASHIR ISAH Jam'iyya mai mulki ta APC ta gargaɗi sanatocinta masu shirin sauya sheƙa zuwa Jam'iyyar PDP cewa, suna iya rasa kujerunsu muddin suka aikata hakan. APC ta yi wannan barazana ne bisa la'akari da shirin da wasu sanatocinta su 15 ke da shi na ficewa daga jama'iyyar. Jam'iyyar ta faɗa wa sanatocin cewa, ficewa daga cikinta kasada ce babba domin kuwa hakan ka iya zama sanadiyyar rasa kujerunsu a Majalisar Tarayya. A hannu guda, su ma sanatocin kansu cike suke da tsoron kada bayan sun sauya sheƙar PDP ta ƙi cika alƙawarin kyautata musu da ta yi, musamman…