Siyasa

Shugaban ƙaramar hukumar Baɓura ya gargaɗi al’umma kan sare itatuwa barkatai

Shugaban ƙaramar hukumar Baɓura ya gargaɗi al’umma kan sare itatuwa barkatai

Daga ABDULLAHI SANI DOGUWA a Kano A ƙoƙarinta na tallafa wa gwamnatin jihar Jigawa wajen yaƙi da sare itatuwa ba bisa ƙa'ida ba, ƙaramar Hukumar ɓaɓura ta gargaɗi manoma da makiyaya da su guji wannan dabi'a da ke haddasa lalacewar muhalli da barazana ga rayuka da dukiyoyin al'umma. Shugaban ƙaramar Hukumar Babura, Alhaji Muhammad Hamisu Garu, ya bayyana hakan yayin da ya kai ziyarar jaje ga al'ummomin da guguwar iska da ruwan sama suka shafa a sassa daban-daban na karamar hukumar. Ya ce gwamnatinjihar karkashin jagorancin Gwamna Malam Umar Namadi na daukar matakai domin dakile matsalar lalacewar muhalli, wadda ke…
Read More
Yadda Shettima, Kwankwaso da Amaechi za su sauya alƙiblar zaɓen 2027

Yadda Shettima, Kwankwaso da Amaechi za su sauya alƙiblar zaɓen 2027

Daga MAHDI MUSA MUHAMMAD Bayan manyan jam’iyyun siyasa sun bayyana sunayen waɗanda za su yi musu takarar mataimakin shugaban ƙasa a zaɓen 2027, hankalin masu bibiyar siyasa ya karkata kan irin tasirin da waɗannan zaɓaɓɓun abokan takara za su iya yi wajen ƙara wa jam’iyyunsu ƙarfi a akwatin zaɓe. Da Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta ƙasa (INEC) ta rufe karɓar sunayen ’yan takara, shugaban ƙasa mai ci, Bola Ahmed Tinubu na Jam’iyyar APC zai sake neman wa’adin mulki tare da mataimakinsa, Sanata Kashim Shettima. A ɓangaren Jam’iyyar ADC kuwa, tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Atiku Abubakar, ya zaɓi tsohon gwamnan…
Read More
Jam’iyyu uku sun gaza gabatar da ’yan takarar shugaban ƙasa kafin INEC ta rufe shafinta

Jam’iyyu uku sun gaza gabatar da ’yan takarar shugaban ƙasa kafin INEC ta rufe shafinta

Daga MAHDI MUSA MUHAMMAD Jam’iyyun siyasa uku ne har zuwa ƙarshen wa’adin da Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta ƙasa (INEC) ta bayar ba su kai sunayen ‘yan takararsu na shugaban ƙasa da mataimakansa cikin tsarin lantarkin hukumar ba, gabanin rufe shafin karɓar sunayen da ƙarfe 11:59 na daren ranar Talata. Wani babban jami’in INEC, wanda ya nemi a sakaya sunansa saboda ba shi da izinin yin magana a hukumance, ya shaida wa manema labarai cewa jam’iyyun da abin ya shafa sun haɗa da Jam’iyyar APGA, ɓangaren Jam’iyyar PDP da Nyesom Wike ke jagoranta, da kuma ɓangaren Jam’iyyar LP ƙarƙashin…
Read More
Shugaban APC ya fara zawarcin tilon sanatan NDC, Rufai Hanga

Shugaban APC ya fara zawarcin tilon sanatan NDC, Rufai Hanga

Daga MAHDI MUSA MUHAMMAD Shugaban Jam’iyyar APC na ƙasa, Farfesa Nentawe Yilwatda, ya kai ziyarar ban girma ga Sanata Rufa’i Sani Hanga, wanda shi ne kaɗai Sanatan NDC daga Jihar Kano, a gidansa da ke Abuja a daren ranar Laraba. Rahotanni sun ce, a cewar mai taimaka wa Sanatan kan harkokin yaɗa labarai, Umar Saminu Mai-Adashi, ganawar ta gudana cikin yanayi na fahimtar juna, inda ɓangarorin biyu suka tattauna muhimman batutuwan da suka shafi siyasar Nijeriya da ci gaban ƙasa. Mai-Adashi ya bayyana a shafinsa na Facebook cewa tattaunawar ta fi karkata ne kan yadda za a ƙarfafa dimokuraɗiyya, da…
Read More
Sauya sheƙar Ubandoma zuwa APC ta janyo cece-kuce a Sakkwato

Sauya sheƙar Ubandoma zuwa APC ta janyo cece-kuce a Sakkwato

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja  Tsohon ɗan takarar gwamnan Jihar Sakkwato a zaɓen 2023, Malam Sa’idu Umar Ubandoma, ya fice daga jam’iyyar ADC tare da komawa APC. Wannan ma cikin wata sanarwa da mai taimaka wa Sanata Aliyu Magatakarda Wamakko kan yaɗa labarai, Bashar Abubakar, ya fitar. An ce Sanata Wamakko ne, ya tarɓi Ubandoma zuwa jam’iyyar APC a gidansa da ke Asokoro a Abuja. Ubandoma, wanda ya taɓa riƙe muƙamin Kwamishinan Kuɗi da kuma Sakataren Gwamnatin Jihar Sakkwato a gwamnatin Aminu Waziri Tambuwal, ya ce salon jagorancin Sanata Wamakko da ayyukan ci gaban da Gwamna Ahmed Aliyu ke…
Read More
2027: INEC ta bai wa APC, PDP, ADC, NDC da sauran jam’iyyu damar ɗora ‘yan takararsu a shafinta

2027: INEC ta bai wa APC, PDP, ADC, NDC da sauran jam’iyyu damar ɗora ‘yan takararsu a shafinta

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja  Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta ƙasa (INEC) ta bai wa jam'iyyun siyasa tara lambobin shiga (access codes) domin su fara loda sunayen 'yan takararsu a shafin hukumar gabanin babban zaɓen shekarar 2027. Binciken jaridar Leadership ya nuna cewa jam'iyyun da suka samu lambobin sun haɗa da All Progressiɓes Congress (APC), Peoples Democratic Party (PDP), African Democratic Congress (ADC), Nigeria Democratic Congress (NDC) da wasu jam'iyyu masu rijista. Ana sa ran jam'iyyun za su yi amfani da lambobin wajen loda sunayen 'yan takararsu na kujerun Shugaban ƙasa, Majalisar Dattawa, Majalisar Wakilai da kuma gwamna…
Read More
Kudirin dokokin da suka fi haifar da hargitsi a Majalisar Dattawa cikin shekara uku

Kudirin dokokin da suka fi haifar da hargitsi a Majalisar Dattawa cikin shekara uku

Daga MAHDI MUSA MUHAMMAD Yayin da Majalisar Dattawa ta 10 ke cika shekara uku da kafa ta a wannan watan Yuni, dokokin gyaran Dokar Zaɓe da kuma Dokokin Gyaran Haraji sun kasance cikin manyan dokokin da suka fi tayar da muhawara da cece-kuce a tsakanin ’yan siyasa, ƙungiyoyin farar hula da al’ummar Nijeriya baki ɗaya. Rahotanni sun nuna cewa zuwa ranar 29 ga Afrilu, 2026, Majalisar Dattawa ta 10 ta amince da sama da ƙudurori 100 tun bayan rantsar da ita a watan Yunin 2023. Bayanan da aka samo daga tsarin bibiyar ƙudurorin majalisar sun nuna cewa wasu ƙudurori 38…
Read More
An nemi haɗin kan ‘yan ADC da suka faɗi zaɓen fidda gwani a Kebbi 

An nemi haɗin kan ‘yan ADC da suka faɗi zaɓen fidda gwani a Kebbi 

Daga JAMIL GULMA a Kebbi  Mataimakin Shugaban Jam'iyyar ADC na jihar Kebbi Alhaji Musa Muhammad Dagwaya ya nemi haɗin kan 'ya'yan jam'iyyar ADC na jihar da  ba su sami nasarar a tsayar da su takarar kujerar muƙaman siyasa ba. Ya yi wannan kira ne a wani taron masu ruwa da tsaki na jam'iyyar ADC na gundumar Kebbi ta Arewa ranar Talatar da ta gabata a garin Argungu. Alhaji Musa Dagwaya ya bayyana cewa a matsayin mu na Musulmi duk mun san duk abinda ya faru to daman rubutacce ne saboda Allah ya riga ya gama tsara komai tun farkon duniya…
Read More
Kano: APC ta tabbatar da Tsamiyar Kara a matsayin ɗan takarar Gezawa

Kano: APC ta tabbatar da Tsamiyar Kara a matsayin ɗan takarar Gezawa

Daga IBRAHIM MUHAMMAD a Kano Jam’iyyar APC ta tabbatar da Hon. Abdullahi Yahaya Tsamiyar Kara a matsayin ɗan takararta na kujerar Majalisar Jihar Kano mai wakiltar ƙaramar hukumar Gezawa a zaɓen 2027. Wakilan jam’iyyar ƙarƙashin jagorancin Ahmad Haruna Bichi tare da jami’an uwar jam’iyyar APC ta jihar Kano, wakilan hukumar zaɓe ta ƙasa, jami’an tsaro da masu ruwa da tsaki ne suka shaida tabbatar da takarar tasa. An gudanar da taron ne ranar Laraba a harabar sakatariyar APC ta Gezawa. Da yake jawabi bayan tabbatar da shi, Hon. Tsamiyar Kara ya gode wa Allah bisa wannan nasara tare da bayyana…
Read More
Ƙungiyar APC Concern Group a Nasarawa ta nuna ɓacin rai kan yadda aka gudanar da zaɓen fidda gwani

Ƙungiyar APC Concern Group a Nasarawa ta nuna ɓacin rai kan yadda aka gudanar da zaɓen fidda gwani

Daga JOHN WADA a Lafia Ƙungiyar All Progressives Congress (APC) concern group a jihar Nasarawa ta nuna ɓacin rai kan yadda aka gudanar da zaɓukan fidda gwanin jam’iyyar da aka gudanar a faɗin jihar a yanzu inda suka bayyana tsarin a matsayin zamba. A cewar ƙungiyar dukkan tsarin zaɓen da aka gudanar a jihar kawo yanzu ya cika da maguɗi kuma bai bi ƙa’idar dimokuraɗiyya da adalci ba. Da yake zantawa da manema labarai a sakatariyar ƙungiyar 'yan jaridu na jihar Nasarawa dake Lafia babban birnin jihar shugaban tawagar honorabul Abdullahi Yammani ya bayyana cewa an tsara zaɓukan da gangan…
Read More