Siyasa

Ruwa ya kusa ƙare wa ɗan kada – Ganduje ga Kwankwaso

Ruwa ya kusa ƙare wa ɗan kada – Ganduje ga Kwankwaso

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Shugaban Jam’iyyar APC na ƙasa, Dakta Abdullahi Umar Ganduje, ya bayyana cewa, ƙiris ya rage madugun jam’iyyar NNPP, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso ya dawo jam’iyyarsu ta APC, saboda ruwa ya kusa ƙare wa ɗan kada. Ganduje ya bayyana hakan ne yana mai cewa jam’iyyar NNPP ta mutu murus, kuma jana’izarta kaɗai suke jira a gudanar a nan kusa. Dakta Ganduje ya bayyana haka ne a ranar Talata yayin ziyarar da wata ƙungiya mai goyon bayan Shugaba Bola Tinubu (TSG) ta kai sakatariyar APC ta ƙasa da ke Abuja. Ganduje ya ce, APC a kodayaushe…
Read More
Jam’iyyarmu ba za ta yi haɗaka da kowacce ba – Gwamnonin PDP

Jam’iyyarmu ba za ta yi haɗaka da kowacce ba – Gwamnonin PDP

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Gwamnonin da aka zaɓa a ƙarƙashin jam’iyyar PDP sun bayyana cewa ba za su yi haɗaka ko kawance da wata jam’iyya ta daban ba gabanin zaɓen 2027. Gwamnonin sun bayyana matsayinsu ne a cikin wata sanarwa da suka fitar a ranar Litinin bayan wata ganawa da suka gudanar a Ibadan, babban birnin jihar Oyo. Tattaunawa kan yiwuwar haɗa kai don kalubalantar jam’iyyar APC na ƙara ɗaukar hankali yayin da zaɓen 2027 ke ƙaratowa. Haka kuma, ’yan adawa sun fara gudanar da wasu “taruka masu mahimmanci” a wannan fanni. ɗaya daga cikin manyan masu goyon…
Read More
Kaduna za ta dawo mai jam’iyya ɗaya – Uba Sani

Kaduna za ta dawo mai jam’iyya ɗaya – Uba Sani

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Gwamnan Kaduna ya ce jam’iyyar APC za ta cigaba da mamaye jihar Kaduna har sai ta kawo jam’iyyar ɗaya ce a jihar. Ya ce a halin yanzu akwai ‘yan majalisun wakilai 4 da wasu ‘yan majalisun dokokin jihar daga ɓangarori daban-daban da suka dawo APC daga jam’iyyar adawa. Gwamna Uba Sani ya yi waɗannan kalamai ne a ranar Litinin a Zariya wanda ya ce sauyin sheƙar wasu ‘yan jam’iyyar adawa zuwa APC, “kyakkyawar alama ce ta irin ayyukan alkhairi da muke yi da tafiya da kowa da kowa a jihar Kaduna.” Shugaban majalisar dattawa,…
Read More
 Rikicin cikin gida ya canja shugabancin kansiloli sau uku a cikin watanni bakwai a Argungu

 Rikicin cikin gida ya canja shugabancin kansiloli sau uku a cikin watanni bakwai a Argungu

Daga JAMEEL GULMA a kebbi Rahotanni daga ƙaramar Hukumar mulki ta Argungu sun bayyana cewa bayan tayar da jijiyoyin wuya na wani lokaci kansilolin ƙaramar hukumar mulkin sun tsige kakakinsu, Honarabul Zayyan Alhassan, kansila mai wakiltar mazaɓar Lailaba kuma nan take  suka maye gurbinsa da Honarabul Mukhtar Umar Gero daga mazaɓar Gwazange a matsayin sabon jagoran kansilolin. Wannan ya biyo bayan wani zama da suka gudanar ranar Laraba 16 ga Afrilu, 2025 inda bayan zaman suka fitar da wata takarda mai ɗauke da sa hannun kansilolin da ta ke bayyana tsige Muhammed Zayyan tare da maye gurbinsa da Honarabul Muktar…
Read More
HOTUNA: Yadda aka rantsar da zaɓaɓɓun shugabannin ƙananan hukumin Katsina

HOTUNA: Yadda aka rantsar da zaɓaɓɓun shugabannin ƙananan hukumin Katsina

Daga UMAR GARBA a Katsina Gwamnan Jihar Katsina, Dikko Umar Raɗɗa, ya rantsar da sabbin shugabannin ƙananan hukumomin Jihar Katsina 34 tare da gargaɗin su akan su guji ɓarnatar da dukiyar al’umma, su kuma gudanar da mulki cikin gaskiya da adalci. An gudanar da bikin rantsuwar ne a filin wasa na Muhammad Dikko inda gwamnan ya nanata ƙudurinsa na bai wa ƙananan hukumonin goyon baya don gudanar da ayyukansu. Kazalika shugaban jam’iyyar APC na ƙasa, Dr. Abdullahi Umar Ganduje, ya yaba wa Raɗɗa a cewarsa gwamnan ya gudanar da sahihin zaɓen ƙananan hukumonin jihar 34. Dr. Ganduje, ya kuma nuna…
Read More
Atiku da Peter Obi na tattaunawa don sauya sheƙa zuwa SDP, inji Adebayo

Atiku da Peter Obi na tattaunawa don sauya sheƙa zuwa SDP, inji Adebayo

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja  Tsohon ɗan takarar Shugaban ƙasa na Jam'iyyar PDP a zaɓen 2023, Atiku Abubakar da takwaransa na LP Mista Peter Obi, na tattaunawa da Jam'iyyar Social Democratic Party (SDP) don komawa cikinta. Tsohon ɗan takarar shugaban ƙasa na SDP a zaɓen 2023, Adewole Adebayo, ne ya bayyana haka a shirin Sunday Politics na Channels Teleɓision. Wannan bayani na Adebayo ya biyo bayan sauya sheƙar da tsohon Gwamnan Jihar Kaduna, Nasir El-Rufai, ya yi daga jam’iyyar APC mai mulki zuwa SDP. Adebayo ya ce, “Mutane suna shiga jam’iyyarmu, kuma muna maraba da su. Kuna gani yadda…
Read More
Dangantaka ta fara tsami tsakanin Wike da gwamnan Bayelsa tun bayan dokar ta-ɓaci a Ribas

Dangantaka ta fara tsami tsakanin Wike da gwamnan Bayelsa tun bayan dokar ta-ɓaci a Ribas

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja  Rikicin siyasa a yankin Kudu maso Kudancin Nijeriya na yaɗuwa zuwa jihar Bayelsa tun bayan saka dokar ta-ɓaci da Shugaba Bola Tinubu ya yi a jihar Ribas mai maƙwabtaka. A wannan karon ma, Ministan Abuja kuma tsohon gwamnan Ribas, Nyesom Wike, shi ne kan gaba a rikicin, wanda wani magoyin bayansa George Turnah ya nemi shirya gangamin nuna goyon baya ga ministan da kuma Shugaba Tinubu na jam'iyyar APC a jihar ta Bayelsa. Sai dai tuni wata babbar kotun Bayelsa ta haramta yin taron bayan antoni janar na gwamnatin jihar ya kai ƙarar Mista…
Read More
An samu rarrabuwar kai a Jam’iyyar Labour bayan hukuncin Kotun ƙoli

An samu rarrabuwar kai a Jam’iyyar Labour bayan hukuncin Kotun ƙoli

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Daya daga cikin manyan jam'iyyun adawa a Nijeriya wato Labour Party, ta faɗa halin ƙaƙa-ni-ka-yi duk da hukuncin Kotun ƙoli na baya-bayan nan, wanda aka shigar domin warware rikicin shugabanci da ke addabar jam'iyyar. Rikicin dai ya kaure ne tsakanin shugabancin jam'iyyar ƙarƙashin jagorancin Julius Abure da kuma ɗaya ɓangaren wanda ya ayyana Nenadi Usman a matsayin shugabar riƙo. Jam'iyyar Labour ta shiga rikicin ne, bayan rasuwar shugabanta na kasa, Alhaji Abdulkadir Abdulsalam a shekara ta 2020. Inda ake ta saɓata juyata tsakanin masu goyon bayan shugabancin Julius Abure da masu ganin ya zama…
Read More
Ƙungiyar matasan APC ta yi raddi kan zarge-zargen da Hon. Jaji ya yiwa Matawalle

Ƙungiyar matasan APC ta yi raddi kan zarge-zargen da Hon. Jaji ya yiwa Matawalle

Daga SANUSI MUHAMMAD a Gusau Ƙungiyar jajirtattun matasan jam'iyyar APC ta ƙasa, National Youths ɓanguard of APC ta sa ƙafa ta shure ɗaukacin zarge-zargen da Hon. Aminu Sani Jaji ya yi wa Ministan ƙasa a ma'aikatar tsaron Nijeriya, Dr Bello Muhammed Matawalle, cewa yana kitsa zarge-zargen ayyukan cin amanar jam’iyya a kansa. A cikin wata sanarwa da ta fitar, Sakataren yaɗa labaran ƙungiyar na ƙasa Dr Adeniyi Wale, ya bayyana zarge-zargen Hon. Jaji a matsayin “maras tushe,” yana mai cewa hakan wata hanya ce ta karkatar da hankalin jama’a daga abubuwan da yake kullawa a siyasa. “Jaji ya jima yana…
Read More
Kotun zaɓen Edo ta kori ƙarar da aka shigar kan Okpebolo da APC

Kotun zaɓen Edo ta kori ƙarar da aka shigar kan Okpebolo da APC

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Kotun sauraron ƙararrakin zaben gwamnan jihar Edo da ke zamanta a Abuja, ta yi watsi da ƙarar da Jam'iyyar Action Alliance (AA) da wani Adekunle Omoaje suka shigar a kan Gwamna Monday Okpebholo da jam’iyyar All Progressiɓes Congress (APC), saboda rashin cancanta da kuma rashin cancanta. Kotun ta ce Adekunle Omoaje, wanda ya shigar da ƙara na haɗin guiwa, ba shi da hurumin yin shari’ar. Daga cikin sauran, kotun ta ce Omoaje bai shiga zaɓen gwamna ba, don haka ba shi da hurumin kokwanto kan sahihancin zaɓen. Kotun ta kuma ce abin da Omoaje…
Read More