Siyasa

2027: Masu ruwa da tsaki na ƙabilar Migili a Nasarawa sun roki Gwamna Sule ya ba su muƙamin mataimakin gwamna

2027: Masu ruwa da tsaki na ƙabilar Migili a Nasarawa sun roki Gwamna Sule ya ba su muƙamin mataimakin gwamna

Daga JOHN D WADA a Lafia Shugabannin ƙabilar Migili a Jihar Nasarawa sun roƙi gwamnan jihar Injiniya Abdullahi Sule da ya zaɓi ɗan asalin Migili a matsayin mataimakin wanda zai gaje shi a zaɓen 2027. Da yake jawabi a wani taron manema labarai a Lafia ranar Litinin, kwamared Sunday Aleku, mai magana da yawun matasan ƙungiyar masu ruwa da tsaki na Migili yace rokon yana da nufin tabbatar da cewa an ji muryar ƙungiyar a matakin mulki mafi girma na jihar. A cewar Aleku, mutanen Migili sun kasance masu goyon baya ga gwamnatoci daban-daban da daɗewa kuma suna taka rawar…
Read More
Zaɓen fidda gwani na APC: Hamza Sule Faskari zai yi takarar majalisar wakilai a Katsina

Zaɓen fidda gwani na APC: Hamza Sule Faskari zai yi takarar majalisar wakilai a Katsina

Daga ABDULLAHI MUHAMMAD a Katsina Masu ruwa da tsaki na jam'iyar APC ta tabbatar da takarar Hamza Sule zai wakilci al'ummar ƙananan hukumomin Faskari,Ƙankara da Sabuwa a zauren majalisar wakilai a zaɓen 2027. Bikin jaddada takarar da ya gudanar a Ƙankara da yawa daga cikin masu ruwa da tsaki na jam'iyar sun yaba da yadda kwamitin sasancin ya gudanar da aikin sa. Shugaban kwamitin sasancin Injiya Tanimu Sabuwa ya bayyana cewa masu ruwa da tsaki na jam'iyar da suka fito daga mazaɓu 31 na ƙananan hukumomin Faskari, Ƙanƙara da Sabuwa wanda suka wakilci ɗaukacin ya'yan jam'iyar suka tabbatar da takarar…
Read More
Gwamnatin Nasarawa ta kammala shirin zaɓen fitar da gwanin APC

Gwamnatin Nasarawa ta kammala shirin zaɓen fitar da gwanin APC

Daga JOHN D WADA a Lafia Gwamnan Jihar Nasarawa Injiniya Abdullahi Sule ya sanar da cewa an kammala dukkan shirye-shiryen gudanar da zaɓen fidda gwani na jam’iyya APC mai ci a jihar domin kujerun majalisar wakilai na tarayya wanda aka shirya za a gudanar a ranar Juma’a15 ga Mayu na shekarar 2026 da ake ciki a jihar. Gwamna Sule ya bayyana hakan ne yayin da yake wa manema labarai jawabi a sakatariyar ƙungiyar manema labarai ta ƙasa (NUJ) reshen jihar da ke Lafia babban birnin jihar. An wakilce gwamnan a taron ta hannun mataimakin sa na musamman kan harkokin hulɗa…
Read More
Dan takarar APC ya fashe da kuka bayan jam’iyya ta zaɓi ɗan takara ta hanyar maslaha

Dan takarar APC ya fashe da kuka bayan jam’iyya ta zaɓi ɗan takara ta hanyar maslaha

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja  Wani ɗan takarar Jam’iyyar All Progressiɓes Congress (APC), ya fashe da kuka bayan ya rasa damar samun tikitin takara, bayan da jam’iyyar ta zaɓi ɗan takara ta hanyar maslaha (consensus). A cikin wani bidiyo da ya bazu a kafafen sada zumunta, an ga ɗan takarar yana kuka tare da nuna takardar fom ɗin da ya saya, yana nuna takaicinsa kan yadda aka ba wani tikitin takarar duk da irin kuɗaɗen da ya kashe a wannan tafiya. Ya bayyana cewa ya zuba kuɗaɗe masu yawa wajen neman takarar, amma a ƙarshe aka cire shi daga…
Read More
Buba Galadima ya buƙaci Atiku ya shiga NDC don haɗin kan ‘yan adawa a zaɓen 2027

Buba Galadima ya buƙaci Atiku ya shiga NDC don haɗin kan ‘yan adawa a zaɓen 2027

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja  Jigo a jam’iyyar NDC, Buba Galadima, ya buƙaci tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Atiku Abubakar, da ya shiga jam’iyyar, yana mai gargadin cewa zai iya zama sanadiyar gazawar haɗin kan ‘yan adawa idan bai yi haka ba kafin zaɓen 2027. Galadima ya bayyana hakan ne a wata hira da gidan talabijin na Channels Tɓ, inda ya ce manyan ‘yan adawa na fara taruwa a ƙarƙashin NDC domin ƙarfafa haɗin gwiwa don kalubalantar jam’iyyar APC mai mulki. Ya ce wasu fitattun ‘yan siyasa sun riga sun koma NDC, yana mai jaddada cewa dole ne a haɗa…
Read More
Na shiga harkokin siyasa ne don taimakon al’umma, inji Adamu Danchina

Na shiga harkokin siyasa ne don taimakon al’umma, inji Adamu Danchina

Daga MUAZU HARDAWA a Bauchi Shahararren ɗan siyasa kuma ɗan kasuwa a fannin ma’adinai a jihar Bauchi da ma ƙasa baki ɗaya, Alhaji Abdullahi Adamu Danchina, ya bayyana kudirinsa na ci gaba da shiga harkokin siyasar Nijeriya domin taimaka wa al’umma su samu abin yi, ingantacciyar rayuwa da kuma tsaro. Danchina ya bayyana hakan ne a garin Narabi yayin da yake ganawa da manema labarai, inda ya ce halin da Nijeriya, musamman yankin Arewa, ke ciki a halin yanzu abin tausayi ne. Ya ce a kullum yana shiga daji domin aikin haƙo ma’adinai, inda ake yawan kiransa ba ƙaƙƙautawa don…
Read More
PDP ta rasa ‘yan majalisa biyar, APC biyu a wani sabon sauya sheƙa

PDP ta rasa ‘yan majalisa biyar, APC biyu a wani sabon sauya sheƙa

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja  Wani sabon yanayi na sauya sheƙa ya sake bayyana a Majalisar Wakilai ta Tarayya, inda wasu ‘yan majalisa suka sauya jam’iyyunsu a wani mataki da ake dangantawa da shirye-shiryen zaben 2027 mai zuwa. A zaman majalisar da aka koma bayan hutun Easter, Mataimakin Kakakin Majalisar, Benjamin Kalu, ya karanta wasiƙun sauya sheƙa daga ‘yan majalisa daban-daban, lamarin da ke nuna yadda harkokin siyasa ke kara sauyawa a Nijeriya. Kalu ya yi watsi da ra’ayin cewa sauya sheƙar na nufin karkata kasar zuwa jam’iyya daya, yana mai cewa hakan alama ce ta ‘yancin dimokuradiyya. Ya…
Read More
Tsare-tsaren Tinubu sun jefa kaso 63 na ‘yan Nijeriya cikin matsanancin talauci – Atiku

Tsare-tsaren Tinubu sun jefa kaso 63 na ‘yan Nijeriya cikin matsanancin talauci – Atiku

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja  Tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Atiku Abubakar, ya soki tsare-tsaren tattalin arziƙin shugaba Tinubu tare da kafa hujja da rahoton bankin duniya wanda ya ce talauci na ci gaba da tsananta a Nijeriya. A cikin jawabin da ya fitar a ranar Juma’a a Abuja, mai taimaka wa Atiku kan yaɗa labarai, Phrank Shaibu, ya ce, bankin duniyar ya nuna irin “mahuyacin halin” da miliyoyin ‘yan Nijeriya ke fama da ita. Ya abato bankin na cewa sama da kaso 60% na ‘yan Nijeriya na rayuwa ƙasa da ma’aunin talauci idan aka kwatanta da kaso 40% da…
Read More
Shirin ‘Renewed Hope’ na Tinubu ga ‘yan Nijeriya yaudara ce – Aregbesola

Shirin ‘Renewed Hope’ na Tinubu ga ‘yan Nijeriya yaudara ce – Aregbesola

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja  Sakataren Jam’iyyar ADC na ƙasa, Rauf Aregbesola, ya ce, shirin shugaba Tinubu na sabunta fata ba zai kawo wa ‘yan Nijeriya wani ci gaba ba. Aregbesola, tsohon gwamnan Osun ya yi wannan kalamai ne a yayin da yake magana a lokacin gangamin taron jam’iyyar na ƙasa wanda tsagin shugabancin da David Mark yake jagoranta a Abuja. Ya kuma buƙaci ‘yan Nijeriya da su yi tsakatsantsan, yana mai cewa gwamnatin ta gaza wajen cika alƙawuran yaƙin neman zaɓen da ya yi ba. “Shirin sabunta fata yaudara ce. Yaushe za a cimma shirin sabunta fatan?” ya…
Read More
Jam’iyyar LP ta sanya 23 ga watan Mayu domin zaɓen fidda gwani na Shugaban ƙasa 

Jam’iyyar LP ta sanya 23 ga watan Mayu domin zaɓen fidda gwani na Shugaban ƙasa 

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja  Jam’iyyar Labour Party ta sanya ranar 23 ga Mayu, 2026 domin gudanar da zaɓen fidda gwani na Shugaban ƙasa gabanin zaɓen 2027. Mai ba shugaban riƙo na jam’iyyar shawara kan harkokin yaɗa labarai, Ken Asogwa ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar a Abuja, inda ya ce an amince da jadawalin ne a taron majalisar zartarwa ta ƙasa (NEC) tare da halartar hukumar zaɓe ta INEC. A cewarsa, jam’iyyar za ta gabatar da rijistar mambobinta ga INEC a ranar 15 ga Afrilu, yayin da za a gudanar da zabukan fidda gwani…
Read More