18
May
Daga JOHN D WADA a Lafia Shugabannin ƙabilar Migili a Jihar Nasarawa sun roƙi gwamnan jihar Injiniya Abdullahi Sule da ya zaɓi ɗan asalin Migili a matsayin mataimakin wanda zai gaje shi a zaɓen 2027. Da yake jawabi a wani taron manema labarai a Lafia ranar Litinin, kwamared Sunday Aleku, mai magana da yawun matasan ƙungiyar masu ruwa da tsaki na Migili yace rokon yana da nufin tabbatar da cewa an ji muryar ƙungiyar a matakin mulki mafi girma na jihar. A cewar Aleku, mutanen Migili sun kasance masu goyon baya ga gwamnatoci daban-daban da daɗewa kuma suna taka rawar…
