Siyasa

‘Yan sanda sun cika hannu da korarren Kwamishinan Zaɓen Adamawa, Yunusa-Ari

‘Yan sanda sun cika hannu da korarren Kwamishinan Zaɓen Adamawa, Yunusa-Ari

'Yan sanda sun damƙe korarren Kwamishinan Zaɓe na Jihar Adamawa, Hudu Yunusa-Ari, kan abin da ya aikata yayain zaɓen gwamna a jihar. Kakakin 'yan sanda, Muyiwa Adejobi, ya bayyana a cikin sanarwar da ya fitar ranar Talata cewa, yanzu haka 'yan sanda na tsare da Yunusa-Ari. Sanarwar ta ce 'yan sanda sun cika hannu da Arin ne a Abuja, inda yake ci gaba da amsa tambaya kan dalilin da ya sa ya yi riga malam masallaci wajen bayyana sakamakon zaɓe alhali ana tsaka da tattara sakamakon zaɓen yayin zaɓen cike giɓi na gwamnan jihar da ya gudana kwanan baya. Ari…
Read More
Mun zo aikin ceto ne, cewar Zaɓaɓɓen Gwamnan Zamfara

Mun zo aikin ceto ne, cewar Zaɓaɓɓen Gwamnan Zamfara

Zaɓaɓɓen Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, a'ya ƙaddamar da kwamitin karɓar mulki a ranar Talata a Gusau, babban birnin jihar. Yayin ƙaddamar da kwamitin mai membobi 60, Dauda Lawal ya jaddada cewa ya zo aikin ceto ne tare da sake gina Jihar Zamfara. Sanarwar da ofishin zaɓaɓɓen gwamnan ya fitar mai ɗauke da sa hannun Sulaiman Bala Idris ta nunar cewa, an kafa kwamitin karɓar mulkin ne a ƙarƙashin jagorancin tsohon Sufeto Janar na ‘yan sanda, M.D Abubakar. Da yake jawabi a wajen ƙaddamar da kwamitin, mai girma Dauda Lawal, ya ce nauyin da ya rataya a kan kwamitin shi…
Read More
Ƙungiyoyi sun bayyana shiyyar da ya dace ta fitar da Shugaban Majalisar Dattawa

Ƙungiyoyi sun bayyana shiyyar da ya dace ta fitar da Shugaban Majalisar Dattawa

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Gamayyar ƙungiyoyin da ke sha'awar tsoma baqi a harkokin siyasa a arewa maso yamma, 'Rescue North West APC Group' ta ce, ta raba gardama kan kujerar Shugaban Majalisar Dattawa. An ruwaito gamayyar ƙungiyoyin na cewa shiyyar arewa maso yammacin Nijeriya ce ta cancanta ta samu kujerar shugaban majalisar dattawa ta 10 da za a kafa. A cewarsu, ya kamata a baiwa shiyyar wannan kujera saboda ta ba da gudummuwar tulin ƙuri'u, waɗanda suka taimaki Zaɓaɓɓen Shugaban Ƙasa, Bola Tinubu, ya kai ga nasara a zaɓen 2023. Bayan taron da ƙungiyoyin suka gudanar a jihohin Katsina, Kaduna,…
Read More
Tinubu, Shugaban APC na Ƙasa, Adamu da wasu sun yi ganawar sirri

Tinubu, Shugaban APC na Ƙasa, Adamu da wasu sun yi ganawar sirri

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Zaɓaɓɓen Shugaban Ƙasa, Sanata Bola Tinubu ya gana da Shugaban Jam’iyyar APC na Ƙasa, Sanata Abdullahi Adamu a gidan tsaro da ke Abuja. A wajen taron da aka gudanar a sirrance akwai Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Ahmad Lawan; Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Ovie Omo-Agege; Sakataren Yaɗa Labarai na Jam’iyyar APC na Ƙasa, Sanata Iyiola Omisore da tsohon Sakataren Kwamitin Yaƙin Neman Zaɓen Shugabancin Jam’iyyar APC, Hon James Faleke. A ƙarshen taron, Shugaban Jam’iyyar APC na Ƙasa ya ce taron wani aiki ne na yau da kullum. Ya ƙi bayyana batutuwan da aka tattauna…
Read More
Kansiloli sun tsige Mataimakin Shugaban Ƙaramar Hukuma a Katsina

Kansiloli sun tsige Mataimakin Shugaban Ƙaramar Hukuma a Katsina

Daga UMAR GARBA a Katsina Kansilolin Ƙaramar Hukumar Malumfashi guda 9 cikin 12 sun gudanar da wani zama na musamman tare da tsige Shugaban Majalisar, Hon. Abdullahi Rabi'u mai wakiltar mazaɓar Yaba da mataimakin shi, Hon Mustapha Ma'azu mai wakiltar mazaɓar Gorar-Dansaka. Haka zalika kamar yadda ɗaya daga cikin kansilolin ya shaida wa Blueprint Manhaja, kansiloli sun kuma tsige Mataimakin Shugaban Ƙaramar Hukumar ta Malumfashi, Hon Abdulrazak Tukur Maifada bisa zarge-zargen aikata ba daidai ba. Daga bisani kansilolin sun naɗa sababbin shuwagabannin kamar haka:- Hon. Salmanu Saminu a matsayin Shugaban Majalisar; Hon. Ibrahim Muhammed Rahimi (Yammama Ward) a matsayin Mataimakin…
Read More
Zaɓen Adamawa: IGP ya canja Kwamishinan ‘Yan Sanda mai lura da zaɓen jihar

Zaɓen Adamawa: IGP ya canja Kwamishinan ‘Yan Sanda mai lura da zaɓen jihar

Babban Sufeton 'Yan Sanda (IGP), Usman Baba, ya ba da umarnin janye Kwamishinan 'Yan Sanda mai lura da sha'anin zaɓe a Jihar Adamawa, Mohammed Barde. Manhaja ta gano cewar IGP ya sake ba da umarnin gaggawa a kan Kwamishinan 'Yan Sanda mai kula da Jihar Gombe, CP Etim Equa, ya koma Adamawa da aiki don ci gaba da lura da sha'anin zaɓen gwamnan jihar wanda bai kammala ba. Da yake zantawa da manema labarai ranar Talata a Abuja, Kakakin Rundunar 'Yan Sanda, Muyiwa Adejobi, ya ce IGP na bakin ƙoƙarinsa wajen tabbatar da komai ya gudana cikin nasara. A cewarsa,…
Read More
Shugabancin Adamawa: Fintiri ya zarce

Shugabancin Adamawa: Fintiri ya zarce

Hukumar Zaɓe ta bayyana Gwamna Ahmadu Fintiri na Jam'iyyar PDP a matsayin wanda ya lashe zaɓen gwamna a Jihar Adamawa. Sakamakon zaɓe ya nuna Fintiri ya lashe zaɓen cike giɓin da ya gudana a jihar Asabar da ta gabata da ƙuri'u 9,337 wanda hakan ya ba shi damar doke abokiyar hamayyarsa ta Jam'iyyar APC, Sanata Aishatu ‘Binani’ Dahiru wadda ta tsira da ƙuri'u 6,513. Bayan kammala zaɓen baki ɗaya, alƙaluma sun nuna Fintiri ya tashi da ƙuri'u 430,861, yayin da Binani ta samu ƙuri'u 398,788. Da yammacin ranar Talata INEC ta kawo ƙarshen tirka-tirkar zaɓen na gwamnan Adamamwa inda ta…
Read More
INEC ta tsayar da ranar bayyana sakamakon zaɓen Gwamnan Adamawa

INEC ta tsayar da ranar bayyana sakamakon zaɓen Gwamnan Adamawa

Hukumar Zaɓe ta Ƙasa, INEC, ta tsayar da ranar da za ta bayyana sakamakon zaɓen Gwamnan Jihar Adamawa. Ya zuwa ranar Alhamis ake sa ran INEC ta bayya sakamakon zaɓen na Adamawa. A cewar Kwamishina a hukumar, Dr Festus Okoye, INEC za ta yi zama a ranakun Talata da Laraba don tattauna batun. A ranar Litinin INEC ta dakatar da Kwamishinan Zaɓe na Jihar Adamawa (REC), Hudu Yunusa Ari, saboda riga-malam-masallacin da ya yi wajen karɓe ikon Baturen Zaɓe tare da bayyana 'yar takarar Jam'iyyar APC, Sanata Aisha Dahiru Binani, a matsayin wadda ta lashe zaɓe tun kafin kammala tattara…
Read More
Sanata Marafa ya amince da shan kaye, ya ce babu batun zuwa kotu

Sanata Marafa ya amince da shan kaye, ya ce babu batun zuwa kotu

Ɗan takarar Sanatan Zamfara ta Tsakiya ƙarƙashin Jam'iyyar APC, Sanata Kabiru Garba Marafa, ya ce ya amince ya sha kaye a hannun takwaransa na PDP, Hon. Ikira Aliyu Bilbis. A jawabinsa da aka yaɗa ranar Litinin, Marafa ya yi alƙawarin ba zai tafi kotu don ƙalubalantar sakamakon zaɓen ba. Saboda a cewarsa, zuwa kotu zai karkatar da hankalin zaɓaɓɓen sanatan daga barin yin aikin da ya kamata, wanda hakan kuwa zai shafi shiyyarsu. Ɗan siyasar ya yi amfani da wannan dama wajen yaba wa al'ummar Zamfara ta Tsakiya dangane da damar da suka ba shi ta zame musu wakili a…
Read More
Sanata Binani ta garzaya kotu neman adalci

Sanata Binani ta garzaya kotu neman adalci

'Yar takarar gwamna ta Jam'iyyar APC a Jihar Adamawa, Sanata Aisha Binani Dahiru, ta garzaya kotu don neman a yi mata adalci a matsayin wadda ta lashe zaɓen Gwamna a jihar. Aisha ta tafi Babbar Kotu a Abuja ne inda ta shigar da ƙarar neman kotu ta dakatar da matakin da Hukumar Zaɓe, INEC, ta ɗauka na soke bayyana ta a matsayin wadda ta lashe zaɓen Gwamnan Adamawa bayan zaɓen da ya gudana ranar 18 ga Maris wanda aka kammala ran 15 ga Afrilu. Kazalika, Sanata Binani na neman kotu ta hana INEC ɗaukar wani mataki na gaba dangane da…
Read More