Siyasa

Yadda Kakakin majalisar Bauchi ya koma muƙaminsa bayan yin murabus  

Yadda Kakakin majalisar Bauchi ya koma muƙaminsa bayan yin murabus  

Daga BAKURA MUHAMMAD a Bauchi Tsohon Kakakin Majalisar Dokoki Jihar Bauchi wanda a zaɓen gama-gari na ranar 18 ga watan Maris ta shekarar da ta gabata 2023 ya tsaya takarar zaɓen wa'adin wakilci zango na biyu, amma ya faɗi zaɓen, a ranar Laraba ya sake ɗare wa kujerar da ta shugabancin majalisar, sakamakon zaɓen cike gurbi da hukumar zaɓe mai zaman kanta (INEC) ta yi a ranar 3 ga watan Fabrairu da ya gabata.  Ɗan takarar shiga majalisar dokoki na jam'iyyar APC daga mazaɓar Ningi ta Tsakiya, Malam Khalid Ningi, shine ya ƙalubalancin zaɓen na tsohon kakakin majalisa Abubakar Yakubu…
Read More
Kakakin Majalisar Jihar Zamfara na fuskantar barazanar tsigewa

Kakakin Majalisar Jihar Zamfara na fuskantar barazanar tsigewa

Daga BASHIR ISAH Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Zamfara, Hon. Bilyaminu Moriki, na fuskantar barazanar tsigewa daga mafiya rinjayen mambobin majalisar. Ya zuwa haɗa wannan rahoto, MANHAJA ta tattaro cewar galibin 'yan majalisar na gudanar da taro a harabar majalisar da yammacin ranar Alhamis kan yadda za su tsige kakakin majalisar. Kazalika, ziyarar da wakilinmu ya kai harabar majalisar ya gano yadda aka rufe harabar majalisar da kuma girke jami'an tsaro da suka haɗa da 'yan danda da sibul difens a cikinta. Bincike ya nuna hatta sandan majalisar bai tsira ba, don kuwa an samu wasu da suka yi awon gaba…
Read More
Tsohon Gwamnan Kaduna, Ramalan Yero ya koma APC

Tsohon Gwamnan Kaduna, Ramalan Yero ya koma APC

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Tsohon Gwamnan Jihar Kaduna Mukhtar Ramalan Yero ya koma Jam'iyyar APC, watanni kaɗan bayan ficewarsa daga Jam'iyyar PDP. Ramalan Yero ya sanar da ficewar tasa ne a wani bayani da ya yi wa manema labaru, ranar Litini ta makon jiya a garin Kaduna. A bayanin nasa, tsohon gwamnan na jihar Kaduna ya ce ya koma APC ne bisa dalilai na ƙashin kansa bayan ya tattauna da wadanda ke kusa da shi a harkar siyasa. A cikin watan Oktoban shekarar 2023 ne Yero ya bayyana ficewarsa daga jam'iyyar PDP. Ramalan Yero ya riƙe gwamnan jihar…
Read More
‘Yan daba sun wargaza zaɓen fidda gwani a Edo

‘Yan daba sun wargaza zaɓen fidda gwani a Edo

Daga BASHIR ISAH Wasu 'yan daba ɗauke da makamai sun tarwatsa harabar Lushville Hotel and Suites da ke yankin GRA, Benin, inda nan ne wurin da aka shirya gudanar da zaɓen fidda gwani na Jam'iyyar APC don takarar gwamnan Jihar Edo. An ce sun wargaza shirin tattara sakamakon zaɓen ne inda suka kai wa wasu masu faɗa a ji farmaki tare kuma da ji wa 'yan jarida da dama rauni da farfasa musu kayan aiki. ’Yan Majalisa Wakilai 60 sun buƙaci a sauya fasalin Nijeriya An sake buɗe Sahad Stores a Abuja bayan shafe sa’o’i 24 a rufe Jami'in tattara…
Read More
Hukumar Zaɓe ta Katsina ta sanar da ranar gudanar da zaɓen ƙananan hukumomi

Hukumar Zaɓe ta Katsina ta sanar da ranar gudanar da zaɓen ƙananan hukumomi

Daga UMAR GARBA a Katsina Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Jihar Katsina (KATSIEC) ta saka ranar 15 ga watan Fabrairu, 2025 a matsayin ranar gudanar da zaɓukan shugabannin ƙananan hukumomi da kansilolo a jihar. Shugaban hukumar, Lawal Alhassan Faskari ne ya bayyana haka a wurin taron masu ruwa da tsaki kan zaɓen wanda ya gudana a hedikwatar hukumar dake G.R.A. A cewar shi, jam'iyyu masu rajista ne kawai za a bari su tsayar da 'yan takara a kujeru daban-daban. Alhaji Lawal Alhassan ya ce sashe na 28 na dokar zaɓen Nijeriya da aka yi wa gyaran fuska 2022 ne…
Read More
Zaɓen cike gurbi: Kakakin Majalisar Dokokin Nasarawa ya rantsar da mambobi biyu

Zaɓen cike gurbi: Kakakin Majalisar Dokokin Nasarawa ya rantsar da mambobi biyu

DAGA JOHN D. WADA a Lafiya Shugaban Majalisar Dokokin Jihar Nasarawa, Honorabul Danladi Jatau, ya rantsar da mambobin majalisar biyu wadanda suka lashe zaben cike gurbi wanda aka gudanar a karshen mako da ya gabata a mazabunsu. Mambobin biyu da aka rantsar su ne; Hon. Mohammed Adamu Omadefu (APC Keana) da Hon. Musa Ibrahim Abubakar (NNPP Doma ta Kudu). A jawabinsa a lokacin da yake rantsar da sabbin ‘yan majlisar a zauren majalisar da Lafiya Fadar Gwamnatin jihar, Kakakin Majalisar, Danladi Jatau, bayan ya taya 'yan majalisar murna dangane da sake mallakar kujerunsu a majalisar, ya kuma kalubalence su da…
Read More
PDP ta ƙara ba Shugaban Matasan jam’iyyar na ƙasa dama a karo na biyu – Mannir Abdullahi

PDP ta ƙara ba Shugaban Matasan jam’iyyar na ƙasa dama a karo na biyu – Mannir Abdullahi

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja An yi kira ga uwar Jam'iyyar PDP ta ƙasa, da ta ƙara bai wa Shugaban Matasan Jam'iyyar na Ƙasa dama a karo na biyu domin ƙara ƙarfafa wa matasa a sha'anin shugabanci. Kakakin gamayyar ƙungiyoyin matasa na Arewacin Nijeriya, Kwamared Mannir Abdullahi Giwa shi ne ya bayyana haka a lokacin da yake zantawa da manema labarai jiya Alhamis. Kwamared Mannir ya ce tunda aka ba Nijeriya 'yancin kai a 1960 aka kuma fara mulkin dimukraɗiyya ba a tava shugaban matasa na kasa mai ƙoƙari da sanin makamar aiki kamar Prince Muhd Kadaɗe Suleiman ba,…
Read More
Ayyukan ‘yan daba sun tilasta wa INEC dakatar da zaɓen cike giɓi a Kano da sauransu

Ayyukan ‘yan daba sun tilasta wa INEC dakatar da zaɓen cike giɓi a Kano da sauransu

Daga BASHIR ISAH Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC) ta dakatar da ci gaba da zabe a wasu mazabun da ake sake zabe a jihohin Kano da Enugu da Akwa Ibom saboda matsalolin da suka hada da sace jami'an zabe da sauransu. Yankunan da dakatarwar ta shafa sun hada da Enugu ta Kudu 1, Mazabar Tarsyya ta Ikono/Ini a Akwa Ibom da kuma Mazabar Kunchi/Tsanyawa a jihar Kano. Bayanin haka na kunshe ne cikin sanarwar da INEC dinnta fitar a ranar Asabar mai dauke da sa hannun Kwamishinanta na kasa kan shaa'nin yada labarai, Sam Olumekun. Hukumar ta…
Read More
Filato: An fara raba kayan aikin zaɓe babu tambarin PDP

Filato: An fara raba kayan aikin zaɓe babu tambarin PDP

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC) ta fara rabon muhimman kayan zabe a kananan hukumomi shida na jihar Filato gabanin zaben da za a sake gudanarwa ranar Asabar. An yi rabon kayayyakin zaben ne a harabar Babban Bankin Nijeriya da ke Jos, babban birnin jihar. An gudanar da rabon kayayyakin ne a gaban wakilan jam’iyyun siyasa, masu sa ido, ‘yan jarida da jami’an tsaro. Sai dai da aka fara rabon kayayyakin, an gano cewa babu tambarin Jam’iyyar PDP a takardar jefa kuri'a yayin da wasu da suka hada da APC, PRP, da…
Read More