Siyasa

Buba Galadima ya buƙaci Atiku ya shiga NDC don haɗin kan ‘yan adawa a zaɓen 2027

Buba Galadima ya buƙaci Atiku ya shiga NDC don haɗin kan ‘yan adawa a zaɓen 2027

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja  Jigo a jam’iyyar NDC, Buba Galadima, ya buƙaci tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Atiku Abubakar, da ya shiga jam’iyyar, yana mai gargadin cewa zai iya zama sanadiyar gazawar haɗin kan ‘yan adawa idan bai yi haka ba kafin zaɓen 2027. Galadima ya bayyana hakan ne a wata hira da gidan talabijin na Channels Tɓ, inda ya ce manyan ‘yan adawa na fara taruwa a ƙarƙashin NDC domin ƙarfafa haɗin gwiwa don kalubalantar jam’iyyar APC mai mulki. Ya ce wasu fitattun ‘yan siyasa sun riga sun koma NDC, yana mai jaddada cewa dole ne a haɗa…
Read More
Na shiga harkokin siyasa ne don taimakon al’umma, inji Adamu Danchina

Na shiga harkokin siyasa ne don taimakon al’umma, inji Adamu Danchina

Daga MUAZU HARDAWA a Bauchi Shahararren ɗan siyasa kuma ɗan kasuwa a fannin ma’adinai a jihar Bauchi da ma ƙasa baki ɗaya, Alhaji Abdullahi Adamu Danchina, ya bayyana kudirinsa na ci gaba da shiga harkokin siyasar Nijeriya domin taimaka wa al’umma su samu abin yi, ingantacciyar rayuwa da kuma tsaro. Danchina ya bayyana hakan ne a garin Narabi yayin da yake ganawa da manema labarai, inda ya ce halin da Nijeriya, musamman yankin Arewa, ke ciki a halin yanzu abin tausayi ne. Ya ce a kullum yana shiga daji domin aikin haƙo ma’adinai, inda ake yawan kiransa ba ƙaƙƙautawa don…
Read More
PDP ta rasa ‘yan majalisa biyar, APC biyu a wani sabon sauya sheƙa

PDP ta rasa ‘yan majalisa biyar, APC biyu a wani sabon sauya sheƙa

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja  Wani sabon yanayi na sauya sheƙa ya sake bayyana a Majalisar Wakilai ta Tarayya, inda wasu ‘yan majalisa suka sauya jam’iyyunsu a wani mataki da ake dangantawa da shirye-shiryen zaben 2027 mai zuwa. A zaman majalisar da aka koma bayan hutun Easter, Mataimakin Kakakin Majalisar, Benjamin Kalu, ya karanta wasiƙun sauya sheƙa daga ‘yan majalisa daban-daban, lamarin da ke nuna yadda harkokin siyasa ke kara sauyawa a Nijeriya. Kalu ya yi watsi da ra’ayin cewa sauya sheƙar na nufin karkata kasar zuwa jam’iyya daya, yana mai cewa hakan alama ce ta ‘yancin dimokuradiyya. Ya…
Read More
Tsare-tsaren Tinubu sun jefa kaso 63 na ‘yan Nijeriya cikin matsanancin talauci – Atiku

Tsare-tsaren Tinubu sun jefa kaso 63 na ‘yan Nijeriya cikin matsanancin talauci – Atiku

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja  Tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Atiku Abubakar, ya soki tsare-tsaren tattalin arziƙin shugaba Tinubu tare da kafa hujja da rahoton bankin duniya wanda ya ce talauci na ci gaba da tsananta a Nijeriya. A cikin jawabin da ya fitar a ranar Juma’a a Abuja, mai taimaka wa Atiku kan yaɗa labarai, Phrank Shaibu, ya ce, bankin duniyar ya nuna irin “mahuyacin halin” da miliyoyin ‘yan Nijeriya ke fama da ita. Ya abato bankin na cewa sama da kaso 60% na ‘yan Nijeriya na rayuwa ƙasa da ma’aunin talauci idan aka kwatanta da kaso 40% da…
Read More
Shirin ‘Renewed Hope’ na Tinubu ga ‘yan Nijeriya yaudara ce – Aregbesola

Shirin ‘Renewed Hope’ na Tinubu ga ‘yan Nijeriya yaudara ce – Aregbesola

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja  Sakataren Jam’iyyar ADC na ƙasa, Rauf Aregbesola, ya ce, shirin shugaba Tinubu na sabunta fata ba zai kawo wa ‘yan Nijeriya wani ci gaba ba. Aregbesola, tsohon gwamnan Osun ya yi wannan kalamai ne a yayin da yake magana a lokacin gangamin taron jam’iyyar na ƙasa wanda tsagin shugabancin da David Mark yake jagoranta a Abuja. Ya kuma buƙaci ‘yan Nijeriya da su yi tsakatsantsan, yana mai cewa gwamnatin ta gaza wajen cika alƙawuran yaƙin neman zaɓen da ya yi ba. “Shirin sabunta fata yaudara ce. Yaushe za a cimma shirin sabunta fatan?” ya…
Read More
Jam’iyyar LP ta sanya 23 ga watan Mayu domin zaɓen fidda gwani na Shugaban ƙasa 

Jam’iyyar LP ta sanya 23 ga watan Mayu domin zaɓen fidda gwani na Shugaban ƙasa 

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja  Jam’iyyar Labour Party ta sanya ranar 23 ga Mayu, 2026 domin gudanar da zaɓen fidda gwani na Shugaban ƙasa gabanin zaɓen 2027. Mai ba shugaban riƙo na jam’iyyar shawara kan harkokin yaɗa labarai, Ken Asogwa ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar a Abuja, inda ya ce an amince da jadawalin ne a taron majalisar zartarwa ta ƙasa (NEC) tare da halartar hukumar zaɓe ta INEC. A cewarsa, jam’iyyar za ta gabatar da rijistar mambobinta ga INEC a ranar 15 ga Afrilu, yayin da za a gudanar da zabukan fidda gwani…
Read More
Wane zaɓi ya rage wa PDP gabanin zaɓen 2027?

Wane zaɓi ya rage wa PDP gabanin zaɓen 2027?

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja  A ranar Litinin 9 ga Maris, 2026, ne kotun ɗaukaka ƙara ta tabbatar soke hukuncin kotun farko, wanda ya hana hukumar Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta (INEC) amincewa da sakamakon babban taron Jam'iyyar PDP da aka yi a ranar 31 ga Oktoba, 2025. A bara ne dai mai shari'a James Omotosho na babban koton tarayya da ke Abuja ya soke babban taron PDP da aka yi a birnin Ibadan na jihar Oyo a ranar 15 da 16 ga watan Nuwamban bara. A hukuncin, wanda dukkan alƙalan kotun guda uku suka yanke, kotun ɗaukaka ƙarar…
Read More
Dalilin da ya sa na sauya sheƙa zuwa APC – Gwamna Dauda

Dalilin da ya sa na sauya sheƙa zuwa APC – Gwamna Dauda

Daga MAHDI MUSA MUHAMMAD Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayyana cewa rikicin cikin gida da kuma taƙaddamar shari’a da ke addabar Jam’iyyar PDP su ne manyan dalilan da suka sa ya yanke shawarar sauya sheƙa zuwa Jam’iyyar APC. Mataimakin Gwamnan Jihar Zamfara, Malam Mani Mummuni, ne ya sanar da sauyin sheƙar a hukumance a ranar Litinin, bayan wani taron masu ruwa da tsaki da aka gudanar a Gidan Gwamnatin Jihar da ke Gusau. A wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sulaiman Bala Idris, ya fitar, an bayyana cewa sauyin daga Jam’iyyar PDP zuwa APC ya zama dole…
Read More
2027: Yankin Kudu maso Yamma zai yi wa Tinubu ruwan ƙuri’u miliyan 10 – Bamidele

2027: Yankin Kudu maso Yamma zai yi wa Tinubu ruwan ƙuri’u miliyan 10 – Bamidele

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja  Shugaban Masu Rinjaye a Majalisar Dattawa, Opeyemi Bamidele, ya ce Jam’iyyar APC ta tsara shirin tattara ƙuri’u domin tabbatar da cewa yankin Kudu maso Yamma ya bai wa Shugaba Bola Tinubu aƙalla ƙuri’u miliyan 10 a zaɓen Shugaban ƙasa na 2027. Bamidele ya bayyana hakan ne a ranar Litinin yayin ƙaddamar da Kwamitin Yaƙin Neman Zaɓen Gwamnan Jihar Ekiti na 2026 mai mambobi 57 a birnin Ado Ekiti, babban birnin jihar. Shi ne shugaban wannan kwamitin. Yankin Kudu maso Yamma ya ƙunshi jihohin Ekiti, Ondo, Ogun, Osun, Lagos da Oyo, kuma Shugaba Tinubu ya…
Read More
ADC za ta bada mamaki a zaɓen 2027, inji jigo a jam’iyyar

ADC za ta bada mamaki a zaɓen 2027, inji jigo a jam’iyyar

Daga MAHDI MUSA MUHAMMAD Wani jigo a jam’iyyar ADC, Cif Ogochukwu Agabus Umunnakwe Onyema, ya bayyana cewa jam’iyyarsa na da ƙwarin gwiwar kawo babban sauyi a zaɓen shekarar 2027, inda ya ce ADC za ta ba da mamaki a siyasar Nijeriya. Onyema ya bayyana hakan ne yayin wata hira da aka yi da shi a birnin Enugu, inda ya ce shugabancin jam’iyyar ADC a halin yanzu yana da tsari mai kyau tare da ƙudurin kwace mulki daga hannun jam’iyya mai mulki ta APC a babban zaɓen da ke tafe. Ya ce, duk da ƙalubalen da ake fuskanta a siyasar ƙasar,…
Read More