15
Feb
Daga UMAR GARBA a Katsina Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Jihar Katsina (KATSIEC) ta saka ranar 15 ga watan Fabrairu, 2025 a matsayin ranar gudanar da zaɓukan shugabannin ƙananan hukumomi da kansilolo a jihar. Shugaban hukumar, Lawal Alhassan Faskari ne ya bayyana haka a wurin taron masu ruwa da tsaki kan zaɓen wanda ya gudana a hedikwatar hukumar dake G.R.A. A cewar shi, jam'iyyu masu rajista ne kawai za a bari su tsayar da 'yan takara a kujeru daban-daban. Alhaji Lawal Alhassan ya ce sashe na 28 na dokar zaɓen Nijeriya da aka yi wa gyaran fuska 2022 ne…