Siyasa

Gwamna Bago ya umarci masu muƙaman siyasa da ke son tsaya takara su ajiye aiki

Gwamna Bago ya umarci masu muƙaman siyasa da ke son tsaya takara su ajiye aiki

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja  Gwamnatin jihar Neja ya bai wa masu riƙe da mukaman siyasa da masu riƙe da ofisoshin gwamnatin da ke tunanin tsayawa takara a zaben 2027 da su ajiye aikinsu kafin ko a ranar 23 ga watan Maris ɗin 2026. Ko’odinetan yaɗa labarai na ofishin sakataren gwamnatin jihar Neja, Lawal Tanko, ne ya bayyana hakan a cikin wani jawabi a ranar Lahadi, inda ya kafa hujja da fitar da jadawalin zaɓe da hukumar INEC ta yi. A cewar jawabin da sakataren gwamnatin jihar (SSG) ya fitar, Abubakar Usman, ya ce, umarnin ya zama dole domin…
Read More
Shugaban PDP na Zamfara ya koma APC

Shugaban PDP na Zamfara ya koma APC

Daga MAHDI MUSA MUHAMMAD Shugaban jam’iyyar PDP a Jihar Zamfara, Dokta Jamil Jibo Magayaki, ya fice daga jam’iyyar tare da komawa APC. Dokta Jamil ya koma jam’iyyar mai mulki ne bayan komawar Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, APC. A cikin wata sanarwa da ya wallafa a shafukansa na sada zumunta, tsohon shugaban PDP na jihar, ya ce ya ɗauki wannan mataki ne bisa halin da siyasa ta ke ciki a Jihar Zamfara. Sanarwar ta ce, “Ni, Dakta Jamil Jibo Magayaki, shugaban jam’iyyar PDP a Jihar Zamfara, ina sanar da ku a hukumance cewa na koma jam’iyyar APC.” Ya ƙara da…
Read More
Yadda APC da ADC ke sabunta rajistar mambobinsu

Yadda APC da ADC ke sabunta rajistar mambobinsu

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja  Jam'iyyun siyasa a Nijeriya sun ƙara ƙaimi wajen sabinta rijartar mambobinsu yayin da wa'adin da aka gindaya domin kowacce ta miƙawa hukumar zaɓen ƙasar cikakkiyar rijistar ke kawo jiki. Wannan na daga cikin shirye-shiryen tunkarar baban zaɓen ƙasar na 2027. A ƙarƙashin sabon jaddawalin zaɓen da hukumar zaɓen Nijeriya, INEC ta fitar, ana buƙatar jam'iyyun siyasar ƙasar su gabatar da cikakkiyar rijistar mambobinsu ya zuwa ranar 2 ga watan Afirelun 2026. Umarnin da INEC ta bai wa jam'iyyun siyasar na daga cikin tanadin dokar zaɓen Nijeriya ta 2026, wadda ke neman inganta yadda jam'iyyun…
Read More
Da na ci amanar Geidam gara na mutu — Mai Mala Buni

Da na ci amanar Geidam gara na mutu — Mai Mala Buni

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja  Gwamnan Jihar Yobe, Mai Mala Buni, ya ce ba zai taɓa cin amanar ubangidansa na siyasa kuma tsohon gwamnan jihar ba, Ibrahim Geidam, wanda yanzu shi ne Ministan Harkokin ’Yan Sanda. Buni ya bayyana hakan ne yayin taron zaɓen shugabannin jam’iyyar APC da aka gudanar a Fadar Gwamnatin Jihar Yobe da ke Damaturu. Gwamnan ya ce siyasarsa ta fara ne da goyon baya da amincewar Geidam. Kafin ya zama gwamna, Buni ya taɓa zama Mai Bai wa Gwamna Shawara kan Harkokin Siyasa a lokacin mulkin Geidam. Daga baya kuma ya zama Sakataren jam’iyyar APC…
Read More
Doguwa ya zama shugaban  jam’iyyar APC na Jihar Kano

Doguwa ya zama shugaban  jam’iyyar APC na Jihar Kano

Daga IBRAHIM HAMISU a Kano  Tsohon Kwamishinan Albarkatun Ruwa, Hon. Umar Haruna Doguwa, ya zama sabon Shugaban jam’iyyar All Progressiɓes Congress (APC) a Jihar Kano. An gudanar da zaɓensa ne a taron babban zaɓen jam’iyyar na jiha, wanda ya kammala a safiyar Laraba ƙarƙashin kulawar Kwamishinan Zaɓe na INEC a Kano, Ambasada Zango Abdu. Wakilai daga ƙananan hukumomi 44 na jihar sun amince da Doguwa da sauran ‘yan takarar maslaha ta hanyar kaɗa ƙuri’ar murya, a wani tsari da majiyoyin jam’iyyar suka bayyana a matsayin mai cike da zaman lafiya da gaskiya. An ware kujerar shugabancin ga Yankin Sanatan Kano…
Read More
Adamawa: Dan Atiku Abubakar ya ajiye muƙaminsa na kwamishina bayan sauyin sheƙar Fintiri zuwa APC

Adamawa: Dan Atiku Abubakar ya ajiye muƙaminsa na kwamishina bayan sauyin sheƙar Fintiri zuwa APC

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja  Adamu Atiku-Abubakar ya ajiye muƙaminsa a matsayin kwamishinan ayyuka da bunƙasa makamashi na jihar Adamawa. Mai taimaka masa kan yaɗa labarai, Abdulaziz Jauro, ne ya sanar da hakan. Ana dai sa ran ɗan tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Atiku Abubakar, zai koma jam’iyyar ADC. Tsohon kwamishinan ya gode wa gwamna Ahmadu Fintiri “kan ba shi dama da ganin cancantarsa na rike muƙamin.” Ya kuma bayyana cewa wannan dama karramawa ce a gare shi inda ya yi alƙawarin ci gaba da mara wa shirin gwamnatin baya na kawo ci gaba a jihar. “Tsohon kwamishinan ya miƙa…
Read More
Dan majalisar Kano ya tsere bayan an yi masa ihun “ba ma yi” a taron APC

Dan majalisar Kano ya tsere bayan an yi masa ihun “ba ma yi” a taron APC

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja  An yi wa ɗan Majalisar Tarayya mai wakiltar Dawakin Tofa/Tofa/Rimin Gado, Tijjani Abdulkadir Jobe, ihun “ba ma yi” a yayin wani taron zaɓen shugabannin jam’iyyar APC da aka gudanar a ƙaramar Hukumar Tofa da ke Jihar Kano. Bidiyoyin da suka karaɗe kafafen sada zumunta sun nuna yadda wasu matasa da magoya bayan jam’iyyar suka yi ta ihu da kalaman nuna ƙin amincewa yayin da ɗan majalisar ke jawabi a taron da aka gudanar a mahaifarsa. Wannan lamari dai ya sanya ɗan majalisar ya cika bujensa da iska yayin da jami’ansa da magoya bayansa suka…
Read More
NNPP ta bayyana dalilin ƙaurace wa zaɓen cika gurbi a Kano bayan ƙarancin fitowar masu kaɗa ƙuri’a

NNPP ta bayyana dalilin ƙaurace wa zaɓen cika gurbi a Kano bayan ƙarancin fitowar masu kaɗa ƙuri’a

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja  Jam’iyyar APC ta lashe zaɓuka a ƙananan hukumomin Ungogo da Kano Municipal a Kano bayan da jam’iyyar adawa ta NNPP ta ƙi shiga zaɓen. Zaɓen cike gurbin dai an yi ne a ranar Asabar biyo bayan rasuwar ‘yan majalisa biyu a Kano a watan Disamba, Aminu Sa’adu (Ungogo) da Sarki Aliyu (Kano Municipal). Dukkan mutane biyun ‘yan jam’iyyar NNPP wadda a lokacin ita ce ke mulki kafin sauyin sheƙar gwamna Abba Yusuf zuwa zuwa APC a watan da ya gabata. ‘Ya’yan ‘yan majalisar da suka rasu – Aminu Sa’adu Jr. da Nabil Daneji –…
Read More
Tirka-tirkar kujerar sanatan Kebbi ta Tsakiya ta kunno kai

Tirka-tirkar kujerar sanatan Kebbi ta Tsakiya ta kunno kai

Daga JAMIL GULMA a Kebbi Iskar guguwar siyasa dai ta soma kaɗawa a Jihar Kebbi, sai dai a wannan karon siyasar za ta zo da sabon salo saboda yanzu gabar cikin gida ce ke neman ruguza jamiyyar APC mai mulki sanadiyyar neman kujeru musamman a matakin tarayya da suka haɗa da Majalisar Dattawa da ta Wakilai. A duk lokacin da mutane fiye da ɗaya ke neman abu ɗaya kuma kowannen su yana iya ɗaukar kowane mataki don cimma burin sa ba shakka akwai gumurzu. Yanzu haka dai tirka-tirkar neman samun tikitin in zama ɗan takarar kujerar dan majalisar dattawa don…
Read More
Sai Abba ya yi da na sanin barin mu – Kwankwaso

Sai Abba ya yi da na sanin barin mu – Kwankwaso

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja  Tsohon ɗan takarar shugaban ƙasa kuma jagoran jam'iyyar NNPP a Nijeriya, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso ya ce yana da yaƙinin cewa sai gwamnan Kano Abba Kabir da muƙarrabansa sun yi da na sanin fita daga jam'iyyar NNPP da suka yi. Sanata Kwankwaso ya ce fitar gwamna Abba daga jam'iyyar NNPP ta zo da mamaki ga mutane da dama, kuma shi da kansa jin abin yake kamar a mafarki. ''Da yawa mutane ina da labarin, gani suke ma kamar wani tsari ne, da ni da shi, ko da ni da su. Nima sau da yawa…
Read More