20
Mar
Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Jam’iyyar Labour Party ta sanya ranar 23 ga Mayu, 2026 domin gudanar da zaɓen fidda gwani na Shugaban ƙasa gabanin zaɓen 2027. Mai ba shugaban riƙo na jam’iyyar shawara kan harkokin yaɗa labarai, Ken Asogwa ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar a Abuja, inda ya ce an amince da jadawalin ne a taron majalisar zartarwa ta ƙasa (NEC) tare da halartar hukumar zaɓe ta INEC. A cewarsa, jam’iyyar za ta gabatar da rijistar mambobinta ga INEC a ranar 15 ga Afrilu, yayin da za a gudanar da zabukan fidda gwani…
