Siyasa

Jam’iyyar LP ta sanya 23 ga watan Mayu domin zaɓen fidda gwani na Shugaban ƙasa 

Jam’iyyar LP ta sanya 23 ga watan Mayu domin zaɓen fidda gwani na Shugaban ƙasa 

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja  Jam’iyyar Labour Party ta sanya ranar 23 ga Mayu, 2026 domin gudanar da zaɓen fidda gwani na Shugaban ƙasa gabanin zaɓen 2027. Mai ba shugaban riƙo na jam’iyyar shawara kan harkokin yaɗa labarai, Ken Asogwa ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar a Abuja, inda ya ce an amince da jadawalin ne a taron majalisar zartarwa ta ƙasa (NEC) tare da halartar hukumar zaɓe ta INEC. A cewarsa, jam’iyyar za ta gabatar da rijistar mambobinta ga INEC a ranar 15 ga Afrilu, yayin da za a gudanar da zabukan fidda gwani…
Read More
Wane zaɓi ya rage wa PDP gabanin zaɓen 2027?

Wane zaɓi ya rage wa PDP gabanin zaɓen 2027?

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja  A ranar Litinin 9 ga Maris, 2026, ne kotun ɗaukaka ƙara ta tabbatar soke hukuncin kotun farko, wanda ya hana hukumar Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta (INEC) amincewa da sakamakon babban taron Jam'iyyar PDP da aka yi a ranar 31 ga Oktoba, 2025. A bara ne dai mai shari'a James Omotosho na babban koton tarayya da ke Abuja ya soke babban taron PDP da aka yi a birnin Ibadan na jihar Oyo a ranar 15 da 16 ga watan Nuwamban bara. A hukuncin, wanda dukkan alƙalan kotun guda uku suka yanke, kotun ɗaukaka ƙarar…
Read More
Dalilin da ya sa na sauya sheƙa zuwa APC – Gwamna Dauda

Dalilin da ya sa na sauya sheƙa zuwa APC – Gwamna Dauda

Daga MAHDI MUSA MUHAMMAD Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayyana cewa rikicin cikin gida da kuma taƙaddamar shari’a da ke addabar Jam’iyyar PDP su ne manyan dalilan da suka sa ya yanke shawarar sauya sheƙa zuwa Jam’iyyar APC. Mataimakin Gwamnan Jihar Zamfara, Malam Mani Mummuni, ne ya sanar da sauyin sheƙar a hukumance a ranar Litinin, bayan wani taron masu ruwa da tsaki da aka gudanar a Gidan Gwamnatin Jihar da ke Gusau. A wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sulaiman Bala Idris, ya fitar, an bayyana cewa sauyin daga Jam’iyyar PDP zuwa APC ya zama dole…
Read More
2027: Yankin Kudu maso Yamma zai yi wa Tinubu ruwan ƙuri’u miliyan 10 – Bamidele

2027: Yankin Kudu maso Yamma zai yi wa Tinubu ruwan ƙuri’u miliyan 10 – Bamidele

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja  Shugaban Masu Rinjaye a Majalisar Dattawa, Opeyemi Bamidele, ya ce Jam’iyyar APC ta tsara shirin tattara ƙuri’u domin tabbatar da cewa yankin Kudu maso Yamma ya bai wa Shugaba Bola Tinubu aƙalla ƙuri’u miliyan 10 a zaɓen Shugaban ƙasa na 2027. Bamidele ya bayyana hakan ne a ranar Litinin yayin ƙaddamar da Kwamitin Yaƙin Neman Zaɓen Gwamnan Jihar Ekiti na 2026 mai mambobi 57 a birnin Ado Ekiti, babban birnin jihar. Shi ne shugaban wannan kwamitin. Yankin Kudu maso Yamma ya ƙunshi jihohin Ekiti, Ondo, Ogun, Osun, Lagos da Oyo, kuma Shugaba Tinubu ya…
Read More
ADC za ta bada mamaki a zaɓen 2027, inji jigo a jam’iyyar

ADC za ta bada mamaki a zaɓen 2027, inji jigo a jam’iyyar

Daga MAHDI MUSA MUHAMMAD Wani jigo a jam’iyyar ADC, Cif Ogochukwu Agabus Umunnakwe Onyema, ya bayyana cewa jam’iyyarsa na da ƙwarin gwiwar kawo babban sauyi a zaɓen shekarar 2027, inda ya ce ADC za ta ba da mamaki a siyasar Nijeriya. Onyema ya bayyana hakan ne yayin wata hira da aka yi da shi a birnin Enugu, inda ya ce shugabancin jam’iyyar ADC a halin yanzu yana da tsari mai kyau tare da ƙudurin kwace mulki daga hannun jam’iyya mai mulki ta APC a babban zaɓen da ke tafe. Ya ce, duk da ƙalubalen da ake fuskanta a siyasar ƙasar,…
Read More
Gwamna Bago ya umarci masu muƙaman siyasa da ke son tsaya takara su ajiye aiki

Gwamna Bago ya umarci masu muƙaman siyasa da ke son tsaya takara su ajiye aiki

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja  Gwamnatin jihar Neja ya bai wa masu riƙe da mukaman siyasa da masu riƙe da ofisoshin gwamnatin da ke tunanin tsayawa takara a zaben 2027 da su ajiye aikinsu kafin ko a ranar 23 ga watan Maris ɗin 2026. Ko’odinetan yaɗa labarai na ofishin sakataren gwamnatin jihar Neja, Lawal Tanko, ne ya bayyana hakan a cikin wani jawabi a ranar Lahadi, inda ya kafa hujja da fitar da jadawalin zaɓe da hukumar INEC ta yi. A cewar jawabin da sakataren gwamnatin jihar (SSG) ya fitar, Abubakar Usman, ya ce, umarnin ya zama dole domin…
Read More
Shugaban PDP na Zamfara ya koma APC

Shugaban PDP na Zamfara ya koma APC

Daga MAHDI MUSA MUHAMMAD Shugaban jam’iyyar PDP a Jihar Zamfara, Dokta Jamil Jibo Magayaki, ya fice daga jam’iyyar tare da komawa APC. Dokta Jamil ya koma jam’iyyar mai mulki ne bayan komawar Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, APC. A cikin wata sanarwa da ya wallafa a shafukansa na sada zumunta, tsohon shugaban PDP na jihar, ya ce ya ɗauki wannan mataki ne bisa halin da siyasa ta ke ciki a Jihar Zamfara. Sanarwar ta ce, “Ni, Dakta Jamil Jibo Magayaki, shugaban jam’iyyar PDP a Jihar Zamfara, ina sanar da ku a hukumance cewa na koma jam’iyyar APC.” Ya ƙara da…
Read More
Yadda APC da ADC ke sabunta rajistar mambobinsu

Yadda APC da ADC ke sabunta rajistar mambobinsu

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja  Jam'iyyun siyasa a Nijeriya sun ƙara ƙaimi wajen sabinta rijartar mambobinsu yayin da wa'adin da aka gindaya domin kowacce ta miƙawa hukumar zaɓen ƙasar cikakkiyar rijistar ke kawo jiki. Wannan na daga cikin shirye-shiryen tunkarar baban zaɓen ƙasar na 2027. A ƙarƙashin sabon jaddawalin zaɓen da hukumar zaɓen Nijeriya, INEC ta fitar, ana buƙatar jam'iyyun siyasar ƙasar su gabatar da cikakkiyar rijistar mambobinsu ya zuwa ranar 2 ga watan Afirelun 2026. Umarnin da INEC ta bai wa jam'iyyun siyasar na daga cikin tanadin dokar zaɓen Nijeriya ta 2026, wadda ke neman inganta yadda jam'iyyun…
Read More
Da na ci amanar Geidam gara na mutu — Mai Mala Buni

Da na ci amanar Geidam gara na mutu — Mai Mala Buni

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja  Gwamnan Jihar Yobe, Mai Mala Buni, ya ce ba zai taɓa cin amanar ubangidansa na siyasa kuma tsohon gwamnan jihar ba, Ibrahim Geidam, wanda yanzu shi ne Ministan Harkokin ’Yan Sanda. Buni ya bayyana hakan ne yayin taron zaɓen shugabannin jam’iyyar APC da aka gudanar a Fadar Gwamnatin Jihar Yobe da ke Damaturu. Gwamnan ya ce siyasarsa ta fara ne da goyon baya da amincewar Geidam. Kafin ya zama gwamna, Buni ya taɓa zama Mai Bai wa Gwamna Shawara kan Harkokin Siyasa a lokacin mulkin Geidam. Daga baya kuma ya zama Sakataren jam’iyyar APC…
Read More
Doguwa ya zama shugaban  jam’iyyar APC na Jihar Kano

Doguwa ya zama shugaban  jam’iyyar APC na Jihar Kano

Daga IBRAHIM HAMISU a Kano  Tsohon Kwamishinan Albarkatun Ruwa, Hon. Umar Haruna Doguwa, ya zama sabon Shugaban jam’iyyar All Progressiɓes Congress (APC) a Jihar Kano. An gudanar da zaɓensa ne a taron babban zaɓen jam’iyyar na jiha, wanda ya kammala a safiyar Laraba ƙarƙashin kulawar Kwamishinan Zaɓe na INEC a Kano, Ambasada Zango Abdu. Wakilai daga ƙananan hukumomi 44 na jihar sun amince da Doguwa da sauran ‘yan takarar maslaha ta hanyar kaɗa ƙuri’ar murya, a wani tsari da majiyoyin jam’iyyar suka bayyana a matsayin mai cike da zaman lafiya da gaskiya. An ware kujerar shugabancin ga Yankin Sanatan Kano…
Read More