06
Feb
Daga JAMIL GULMA a Kebbi Iskar guguwar siyasa dai ta soma kaɗawa a Jihar Kebbi, sai dai a wannan karon siyasar za ta zo da sabon salo saboda yanzu gabar cikin gida ce ke neman ruguza jamiyyar APC mai mulki sanadiyyar neman kujeru musamman a matakin tarayya da suka haɗa da Majalisar Dattawa da ta Wakilai. A duk lokacin da mutane fiye da ɗaya ke neman abu ɗaya kuma kowannen su yana iya ɗaukar kowane mataki don cimma burin sa ba shakka akwai gumurzu. Yanzu haka dai tirka-tirkar neman samun tikitin in zama ɗan takarar kujerar dan majalisar dattawa don…
