Siyasa

Tirka-tirkar kujerar sanatan Kebbi ta Tsakiya ta kunno kai

Tirka-tirkar kujerar sanatan Kebbi ta Tsakiya ta kunno kai

Daga JAMIL GULMA a Kebbi Iskar guguwar siyasa dai ta soma kaɗawa a Jihar Kebbi, sai dai a wannan karon siyasar za ta zo da sabon salo saboda yanzu gabar cikin gida ce ke neman ruguza jamiyyar APC mai mulki sanadiyyar neman kujeru musamman a matakin tarayya da suka haɗa da Majalisar Dattawa da ta Wakilai. A duk lokacin da mutane fiye da ɗaya ke neman abu ɗaya kuma kowannen su yana iya ɗaukar kowane mataki don cimma burin sa ba shakka akwai gumurzu. Yanzu haka dai tirka-tirkar neman samun tikitin in zama ɗan takarar kujerar dan majalisar dattawa don…
Read More
Sai Abba ya yi da na sanin barin mu – Kwankwaso

Sai Abba ya yi da na sanin barin mu – Kwankwaso

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja  Tsohon ɗan takarar shugaban ƙasa kuma jagoran jam'iyyar NNPP a Nijeriya, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso ya ce yana da yaƙinin cewa sai gwamnan Kano Abba Kabir da muƙarrabansa sun yi da na sanin fita daga jam'iyyar NNPP da suka yi. Sanata Kwankwaso ya ce fitar gwamna Abba daga jam'iyyar NNPP ta zo da mamaki ga mutane da dama, kuma shi da kansa jin abin yake kamar a mafarki. ''Da yawa mutane ina da labarin, gani suke ma kamar wani tsari ne, da ni da shi, ko da ni da su. Nima sau da yawa…
Read More
NNPP ta sha alwashin sake ƙwace kujerar gwamnan Kano daga hannun Abba a 2027

NNPP ta sha alwashin sake ƙwace kujerar gwamnan Kano daga hannun Abba a 2027

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja  Kwankwaso ya buƙaci haɗin kai tsakanin Nijeriya da Amurka, ya yi kira ga Tinubu ya naɗa Jakadu da za su rika kare muradun Nijeriya a ƙasashen duniya Jam’iyyar NNPP reshen jihar Legas ta ce a shirye jam’iyyar take ta sake ƙwace mulki a Kano a 2027 duk kuwa da sauyin sheƙar gwamnanta tilo Abba Yusuf zuwa jam’iyyar APC. Sakataren yaɗa labaran NNPP a jihar, Richard Benson, ne ya bayyana hakan a cikin wata hira da ya yi da kamfanin dillancin labarai na ƙasa (NAN) a ranar Talata a jihar Legas. A yayin da yake…
Read More
Kotu ta soke zaɓen fidda gwani na gwamna na PDP a Ekiti

Kotu ta soke zaɓen fidda gwani na gwamna na PDP a Ekiti

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja  Wata babbar kotun tarayya da ke zamanta a Ado-Ekiti ta soke zaɓen fidda gwani na gwamna da jam’iyyar PDP ta gudanar a jihar Ekiti gabanin zaɓen shekarar 2026. Kotun ta kuma umarci jam’iyyar da ta sake gudanar da sabon zaɓen fidda gwani bisa bin doka da ƙa’idojin cikin gida na jam’iyyar. Alƙalin kotun, Babs Kuewumi, ne ya yanke hukuncin a ranar Talata a karar mai lamba FHC/AD/CS/29/2025, wadda Funso Ayeni, dan takarar gwamna, ya shigar kan PDP da Hukumar Zaɓe ta ƙasa (INEC). Ayeni ya kalubalanci sahihancin zaben fidda gwanin da ya fitar da…
Read More
An yaba wa Gwamna Zulum kan gudanar da zaɓen ƙananan hukumomi cikin lumana a Jihar Borno

An yaba wa Gwamna Zulum kan gudanar da zaɓen ƙananan hukumomi cikin lumana a Jihar Borno

Daga GAMBO ISA a Abuja Shugaban ƙaramar Hukumar Kaga a Jihar Borno, Hon. Mairu Goni Abdullahi, ya bayyana jin daɗinsa tare da yaba wa Gwamnan Jihar Borno, Farfesa Babagana Umara Zulum, bisa nasarar da aka samu wajen gudanar da zaɓen ƙananan hukumomin jihar cikin kwanciyar hankali, tsari da adalci. Ya ce wannan zaɓe ya nuna ƙwazon gwamnati da jajircewarta wajen ƙarfafa dimokiraɗiyya a matakin ƙasa. Hon. Mairu Goni Abdullahi ya bayyana hakan ne yayin wata ganawa da manema labarai a hedkwatar ƙaramar Hukumar Kaga, inda ya jaddada cewa zaɓen ya gudana lafiya ba tare da matsalolin tsaro ba. A cewarsa,…
Read More
Badaru ya ƙaryata raɗe-raɗin sauya sheƙarsa zuwa ADC

Badaru ya ƙaryata raɗe-raɗin sauya sheƙarsa zuwa ADC

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Tsohon Ministan Tsaro na Nijeriya , Mohammed Badaru Abubakar ya musanta rahotannin da ke cewa yana shirin sauya sheƙa daga jam'iyyarsa ta APC mai mulkin ƙasar zuwa jam'iyyar hamayya ta ADC. A wata sanarwa da tsohon ministan ya sanya wa hannu da kansa, ya ce wannan zancen, labarin ƙanzon kurege ne, kuma wani yunƙuri ne kawai na ɓata masa suna, da kuma kassara harkar siyasarsa. A tattaunawarsa da BBC wani hadimin tsohon ministan, Kwamared Abba Malami, ya ce su wannan labari ya zo musu ne ma da mamaki: ''Na farko dai babu ƙanshin gaskiya…
Read More
Kiraye-kirayen cewa na ajiye takara cin amanar ‘yan Nijeriya ne – Atiku

Kiraye-kirayen cewa na ajiye takara cin amanar ‘yan Nijeriya ne – Atiku

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja  Tsohon Mataimakin shugaban ƙasa, Atiku Abubakar, ya yi gargaɗi kan kiraye-kirayen da ake yi masa na ya ajiye takara a yaƙin neman shugabancin ƙasa ƙarƙashin jam’iyyar haɗaka ta ADC, yana mai cewa hakan cin amanar ‘yan Nijeriya ne. Sanarwar da mai bai wa Atiku shawara kan harkokin yaɗa labarai, Paul Ibe, ya fitar ta bayyana cewa duk wani yunƙuri na ganin Atiku ya ajiye takara zai goyi bayan manufofin kama-karya ne kawai tare kuma da tauye haƙƙin dimokuraɗiyya a Nijeriya. Sanarwar ta ce a cikin shekaru kusan uku da suka gabata, ‘yan Nijeriya sun…
Read More
Kotu ta soke rushewar shugabannin NNPP, ta tabbatar da jagorancin Abiya a Kano

Kotu ta soke rushewar shugabannin NNPP, ta tabbatar da jagorancin Abiya a Kano

Daga RABIU SANUSI a Kano Wata Babbar Kotu a Jihar Kano ta soke matakin rushe shugabannin jam’iyyar New Nigerian Peoples Party (NNPP) a matakan jiha, kananan hukumomi da mazabu, tare da bayyana hukuncin Kwamitin Gudanarwa na ƙasa (NWC) a matsayin babu inganci a doka. Mai shari’a Nasiru Saminu ne ya bayar da umarnin eɗ-parte a ranar Talata, inda ya kuma hana Kwamitin Gudanarwa na ƙasa na NNPP ɗaukar duk wani sabon mataki da ya shafi tsarin shugabancin jam’iyyar a Kano, har zuwa lokacin sauraron da yanke hukunci kan Motion on Notice da masu ƙara suka shigar. ƙarar mai lamba K/06/2026,…
Read More
Bai kamata a zargi Abba da cin amana ba — Shekarau

Bai kamata a zargi Abba da cin amana ba — Shekarau

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja  Tsohon Gwamnan Kano, Malam Ibrahim Shekarau, ya ce bai dace a zargi Gwamna Abba Kabir Yusuf da cin amana ba dangane da jita-jitar cewa zai fice daga jam’iyyar NNPP. Malam Shekarau ya bayyana cewa sauya sheƙa a siyasa ra’ayi ne wanda ya dogara da shawara da kuma halin da aka tsinci kai a ciki. Tsohon Gwamnan ya bayyana hakan ne a wata hira da kafar DCL Hausa, inda ya soki kalaman Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso, wanda ya ce ya kamata Gwamna Abba ya ajiye kujerarsa idan ya fice daga NNPP. A cewarsa, wannan magana…
Read More
Yadda shirin komawar Abba Gida-gida Jam’iyyar APC ya yamutsa hazon siyasar Kano 

Yadda shirin komawar Abba Gida-gida Jam’iyyar APC ya yamutsa hazon siyasar Kano 

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Shirin sauya sheƙar Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, daga NNPP zuwa APC ya jefa tafiyar Kwankwasiyya, wadda uban gidansa na siyasa, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso, yake jagoranta, cikin ruɗani. Majiyoyi da dama sun ce, babu gudu, babu ja da baya kan hukuncin da gwamnan ya yanke, ko da kuwa hakan zai kawo cikas tsakaninsa da Kwankwaso. Sanata Kwankwaso shi ne wanda ya kafa tafiyar Kwankwasiyya kuma ya taka muhimmiyar rawa wajen samun nasarar Abba a zaɓen gwamna a 2023. Sauya sheƙar Abba da ke tafe ta sake tayar da tsoffin taƙaddama a siyasar…
Read More