02
Jan
Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello, ya bayyana aniyarsa ta tsayawa takarar Sanatan Kogi ta tsakiya a zaɓen 2027 mai zuwa. Bello ya bayyana hakan ne a wata ziyara da ya kai fadar Ohinoyi na Ebiraland, inda ya gana da sarakunan gargajiya, malaman addini da masu ruwa da tsaki na yankin majalisar dattawa. An yaɗa bidiyon ziyarar da kuma bayaninsa a shafin Facebook mai tabbatar da Bello a ranar Litinin. "Na yarda in tsaya takarar majalisar dattawa a 2027," inji tsohon gwamnan yayin da yake jawabi a wurin taron. Gwamnan jihar Kogi, Ahmed Usman…
