Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja
Gwamnan Jihar Osun Ademola Adeleke ya bayyana komawarsa Jam’iyyar Accord, inda ya ce a cikinta ne zai yi takarar neman wa’adin mulkinsa na biyu a zaɓen da za a yi a shekarar 2026.
Gwamnan ya bayyana haka ne a wani taro da ya gudana a fadar gidan gwamnatin jihar, inda ya yi maraba da jagororin jam’iyyar na jiha da na ƙasa.
“Tun a ranar 6 ga watan Nuwamba na yanke shawarar komawa Jam’iyyar Accord domin in yi takarar tazarce bayan tattaunawa da na yi da masu ruwa da tsaki da mazauna jiharmu ta Osun.”
Ya ce ya zaɓi jam’iyyar ne saboda tsarinta na taimakon al’umma, “tsarin da ya yi daidai da tsarinmu na ba jin daɗin ma’aikatanmu da ma al’ummarmu muhimmanci.
“Mutanen Osun sun zaɓa mulki mai kyau ne a zaɓen shekarar 2022, kuma ina da yaƙinin za su sake zaɓenmu domin ci gaba da mulki a zaɓen shekarar 2026. Mutane suna ƙaunar mu ci gaba, kuma Jam’iyyar Accord ce jam’iyyarmu a zaɓen baɗi,” inji gwamnan a sanarwar da mai magana da yawunsa, Mallam Olawale Rasheed ya fitar.
Shi kuwa takwaransa, Gwamna Siminalayi Fubara na Jihar Ribas ya sanar da komawarsa zuwa jam’iyyar APC.
Fubara ya bayyana haka ne yayin wani zama na masu ruwa tsaki a gidan Gwamnatin jihar.
Hakan na zuwa ne jim-kaɗan bayan ya fice daga babbar jam’iyyar adawa ta PDP.
Idan ba a manta ba a ranar Litinin ne gwamnan ya yi wata ganawar sirri da Shugaba Bola Tinubu a Fadar Shugaban ƙasa da ke Abuja.
