Yahaya Bello ya bayyana aniyarsa ta tsayawa takarar Sanata a Kogi ta tsakiya

Spread the love

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja

Tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello, ya bayyana aniyarsa ta tsayawa takarar Sanatan Kogi ta tsakiya a zaɓen 2027 mai zuwa.

Bello ya bayyana hakan ne a wata ziyara da ya kai fadar Ohinoyi na Ebiraland, inda ya gana da sarakunan gargajiya, malaman addini da masu ruwa da tsaki na yankin majalisar dattawa.

An yaɗa bidiyon ziyarar da kuma bayaninsa a shafin Facebook mai tabbatar da Bello a ranar Litinin.

“Na yarda in tsaya takarar majalisar dattawa a 2027,” inji tsohon gwamnan yayin da yake jawabi a wurin taron.

Gwamnan jihar Kogi, Ahmed Usman Ododo, ya halarci taron, tare da wasu jiga-jigan ‘yan siyasa da shugabannin al’umma.

Kamar yadda shafin jaridar Peoples Daily ya ruwaito, Ododo ya roki magabacinsa da ya amsa kiraye-kirayen da shugabannin jam’iyyar da ‘yan mazaɓar suka yi masa na neman ya wakilci gundumar a majalisar dokokin ƙasar.

Rahoton ya ce an yi wannan roko ne a gaban Ohinoyi na Ebiraland da wasu masu fada a ji daga yankin.

Bello, wanda ya mulki jihar Kogi daga 2016 zuwa 2024, ya kasance jigo a jam’iyyar All Progressiɓes Congress a jihar.

A halin da ake ciki, Kogi Watch ta ruwaito cewa shugaban ƙaramar hukumar Okehi, Amoka Eneji, ya taya Bello murnar bayyana aniyarsa ta tsayawa takarar.

An ruwaito Eneji yana mai cewa tsohon gwamnan ya yi aiki da yawa don haɗin kai da ci gaban mutanen Ebira, ya ƙara da cewa shugabancin Bello zai yi fice a tarihin Ebira.

A halin yanzu dai kujerar Sanatan Kogi ta tsakiya tana hannun Sanata Natasha Akpoti-Uduaghan, wacce aka zaɓa a shekarar 2023.

Akpoti-Uduaghan, lauya kuma tsohon ɗan takarar gwamna, ta kafa tarihi a matsayin mace ta farko da ta wakilci gundumar a majalisar dattawa.

.

By ukarofi