Siyasa

Yilwatda ga ‘yan Nijeriya: Gwamnoni da Ciyamomi suna karɓar kashi uku na kuɗaɗe a kowane wata

Yilwatda ga ‘yan Nijeriya: Gwamnoni da Ciyamomi suna karɓar kashi uku na kuɗaɗe a kowane wata

Daga SANI AHMAD GIWA pa Abuja Shugaban Jam'iyyar All Progressives Congress (APC) mai mulki a ƙasa, Farfesa Nentawe Yilwatda, a ranar Litinin ya buƙaci 'yan Nijeriya da su ɗora alhaki wa gwamnonin jihohinsu da shugabannin ƙananan hukumomi haƙƙoƙin saboda ƙaruwar kuɗaɗen da suke samu a kowane wata. Shugaban Jam'iyyar APC ya ce babu wani gwamna da shugaban ƙaramar hukuma da zai samu ƙasa da sau uku ko huɗu fiye da abin da suke samu a matsayin kuɗaɗen da ake ware musu a kowane wata kafin gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu ta fara aiki. Da yake jawabi a Abuja a wani…
Read More
Saura ƙiris APC ta mamaye Kaduna bakiɗaya – Uba Sani

Saura ƙiris APC ta mamaye Kaduna bakiɗaya – Uba Sani

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Jam’iyyar APC ta ƙara samun sabbin mambobi bayan wasu ‘yan majalisar dokokin jihar Kaduna guda huɗu da ‘yan majalisar wakilai ta tarayya guda biyar, tare da dubban magoya bayansu, sun sauya sheƙa zuwa jam’iyyar a babban gangamin da aka gudanar a ranar Asabar. Da wannan sabon sauya sheƙa, APC yanzu tana da ‘yan majalisar wakilai ta tarayya 13 daga jihar Kaduna, yayin da PDP ke da uku kacal. A majalisar dokokin jihar kuma, APC na da mambobi 26, PDP kuma takwas. An gudanar da gangamin a Filin Murtala Sƙuare da ke Kaduna. A jawabinsa,…
Read More
Nnamdi Kanu ya kori lauyoyinsa, ya ce zai kare kansa a kotu

Nnamdi Kanu ya kori lauyoyinsa, ya ce zai kare kansa a kotu

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Shugaban haramtacciyar ƙungiyar IPOB, Mista Nnamdi Kanu, ya kori dukkan lauyoyinsa tare da bayyana cewa zai kare kansa da kansa a gaban kotu. Kanu ya bayyana hakan ne a lokacin zaman kotu yayin da yake shirin fara kare kansa kan tuhumar da gwamnati take masa kan cin amanar ƙasa. A lokacin zaman kotun da aka gudanar a ranar Alhamis, babban lauyan Kanu, Sanata Kanu Agabi (SAN), ya sanar wa kotu cewa shi da sauran manyan lauyoyin Kanu sun janye daga kare shi a wannan shari’ar. Mai shari’a James Omotosho ya amince da buƙatar janyewar…
Read More
PDP ta ce ba za ta sanya wa ‘ya’yanta da ke alaƙa da APC takunkumi ba a yanzu 

PDP ta ce ba za ta sanya wa ‘ya’yanta da ke alaƙa da APC takunkumi ba a yanzu 

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Jam’iyyar PDP ta amince cewa wasu daga cikin ‘ya’yanta na alaƙa da Jam’iyyar APC mai mulki amma ta ce ta zaɓi kada ta sanya musu takunkumi a yanzu, inda ta fifita haɗin kai da kwanciyar hankali gabanin babban taronta na ƙasa da kuma babban zaɓen 2027. Blueprint Manhaja ta ruwaito cewa Debo Ologunagba, Sakataren Yaɗa Labarai na Jam’iyyar na ƙasa ne ya bayyana hakan a ranar Litinin da ta gabata a Abuja yayin da yake jawabi ga manema labarai kan shirye-shiryen jam’iyyar na zaɓen fidda gwani na babban taronta na ƙasa da aka shirya…
Read More
‘Yan Nijeriya ba za su sake zaɓenka ba, PDP ta buƙaci Tinubu ya shirya miƙa mulki a 2027

‘Yan Nijeriya ba za su sake zaɓenka ba, PDP ta buƙaci Tinubu ya shirya miƙa mulki a 2027

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Jam’iyyar PDP ta yi kira ga Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu da ya fara shirya takardar miƙa mulki, inda ta dage cewa ‘yan Nijeriya ba za su mayar da shi kan karagar mulki ba a 2027. Da yake jawabi a sakatariyar jam’iyyar PDP a jihar Yola a ranar Juma’a, sakataren ƙungiyar na jihar Adamawa, Hamza Madagali, ya ce jama’a sun daina hakuri da gwamnati mai ci. Ya zargi jam’iyyar All Progressiɓes Congress (APC) da rashin hangen nesa da alƙibla, yana mai bayyana manufofinta a matsayin “maƙiyar mutane da tattalin arziki.” "'Yan Nijeriya a shirye…
Read More
Za mu maye gurbin Abdulmumin Jibrin da ɗan takara mai ƙarfi a 2027, Kwankwaso ga magoya bayansa

Za mu maye gurbin Abdulmumin Jibrin da ɗan takara mai ƙarfi a 2027, Kwankwaso ga magoya bayansa

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar New Nigeria People’s Party, NNPP, a zaɓen 2023, Rabi’u Musa Kwankwaso, ya yi watsi da korar Abdulmumin Jibrin daga jam’iyyar, inda ya yaba wa reshen jihar Kano kan wannan mataki. Manhaja ta tuna cewa a wata hira da ya yi da wata kafar yaɗa labarai ta yanar gizo, DCL a kwanakin baya, Mista Jibrin ya fito fili ya bayyana aniyarsa ta ficewa daga jam’iyyar NNPP. Sakamakon haka, a ranar 6 ga watan Satumba, shugaban NNPP na jihar, Hashimu Dungurawa, ya sanar da korar Mista Jibrin a wani taron…
Read More
Muna yaba wa Gwani Makoɗa kan sakamakon NECO da ɗaliban Kano suka yi zarra – Hon. Doguwa

Muna yaba wa Gwani Makoɗa kan sakamakon NECO da ɗaliban Kano suka yi zarra – Hon. Doguwa

Daga MUHAMMADU MUJITABA a Kano Jagoran siyasar ƙaramar Hukumar Doguwa kuma mai ba wa Gwamnan Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf shawara kan dabarun tafiyar da siyasa, Hon. Ali Abdu Dogowa, ya bayyana cewa, nasarar da Kano ta samu a sakamakon jarrabawar kammala sakandire na hukumar shirya jarrabawa ta NECO babbar nasara ce ga al’ummar Kano da Arewa bakiɗaya. Hon. Dogowa ya jaddada cewa wannan nasara ta samo asali ne daga jajircewar Gwamnan Kano, Alhaji Abba Kabir Yusif, tare da kulawar Ma’aikatar Ilimi ƙarƙashin jagorancin Hon. Gwani Ali Haruna Makoɗa, wanda ya taka rawar gani wajen gyara tsarin ilimi a jihar.…
Read More
Dikko Raɗɗa ya rantsar da masu ba shi shawara guda biyu

Dikko Raɗɗa ya rantsar da masu ba shi shawara guda biyu

Daga ABDULLAHI MUHAMMAD a Katsina Gwamnan Jihar Katsina Malam Dikko Umar Raɗɗa ya rantsar da sabbin masu bashi shawara guda biyu. Sun haɗa da Hon. Tasi'u Dahiru Ɗanɗagoro a matsayin mai baiwa gwamna shawara akan Ilimin Alkur'ani da yaran da ba su zuwa makaranta. Sai Hon. Aminu Lawal Jibia wanda aka rantsar a matsayin mai bai wa gwamna shawara akan inganta rayuwar al'umma. Aminu Lawal ya taɓa riƙe muƙamin shugaban karamar hukumar Jibiya,ya kuma riƙe muƙamin mai ba gwamna shawara a gwamnatin Aminu Bello Masari kafin ya sami wannan muƙami. Haka shima Hon Tasi'u Dandagoro ya taɓa riƙe muƙamin shugaban…
Read More
Arewa ba za ta iya karɓar mulki ba a 2027 – Gwamna Bago

Arewa ba za ta iya karɓar mulki ba a 2027 – Gwamna Bago

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Gwamnan Jihar Neja, Umar Bago, ya bayyana cewa babu wata dama ta sake dawowa Arewa da mulki 2027, yana mai jaddada cewa dole ne a bar Shugaba Bola Tinubu ya kammala wa’adin mulkinsa na tsawon shekaru takwas. Da yake magana a shirin Sunday Politics na TɓC tare da Femi Akande, Bago ya ce waɗanda ke tada jijiyoyin wuya a Arewa bayan shekaru biyu kacal na mulkin Tinubu, suna yin rashin imani ne da kuma adawa da tsarin shiyya-shiyya da ya sa Nijeriya ta ɗore. "Saboda kuka da babbar murya, mutumin nan ya shafe shekaru…
Read More
Tinubu bai shirya gudanar da sahihin zaɓe ba a 2027 – Buba Galadima

Tinubu bai shirya gudanar da sahihin zaɓe ba a 2027 – Buba Galadima

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Jigo a Jam’iyyar NNPP, Buba Galadima, ya yi zargin cewa gwamnatin Shugaban ƙasa Bola Tinubu ba ta da niyyar gudanar da sahihi kuma ingantaccen zaɓe a 2027. Galadima ya bayyana hakan ne ranar Talata a wata hira da aka yi da shi a shirin Prime Time na gidan talabijin na Arise Tɓ, inda ya ce gwamnatin da jam’iyyar APC ke jagoranta ta kankane cibiyoyin gwamnati don amfaninta. “Wannan gwamnati ba ta shirya gudanar da zaɓen adalci ba. Daga yadda suke tafiyar da al’amura, za ka gane yadda suke tarwatsa jam’iyyun siyasa. Wannan yana nuna…
Read More