Siyasa

Dalilan da ya sa muka kusa barin Jam’iyyar NNPP Kwankwasiyya a Ribas – Hon. Libda

Dalilan da ya sa muka kusa barin Jam’iyyar NNPP Kwankwasiyya a Ribas – Hon. Libda

Daga MAHAMMADU MUJITABA a Kano  Shugaban matasan Kwankwasiyya, kuma mataimakin shugaban matasan jam'iyyar NNPP na Jihar Ribas, Hon. Kabiru Libda ya bayyana cewa ganin yadda suka yi wa jam'iyyar NNPP Kwankwasiyya hidima ta hanyoyi daban-daban har kuma ɗan takarar shugaban ƙasa Sanata Rabiu Musa Kwankwaso ya samu ƙuri'u masu yawa a Jihar Ribas a zaɓen gamagari na 2023, wanda kuma a cewarsa suka wayar da kan 'yan uwansu na Jihar Kano da gagarumar gudunmawa, wanda hakan tasa abokan da masoyan da duk wanda zasu gaya masa ya ji Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf ya zaɓa a zaɓen gwamna, haka duk…
Read More
A lissafin da na yi, Tinubu na uku zai zo a zaɓen Shugaban ƙasa na 2027 – El-Eufai

A lissafin da na yi, Tinubu na uku zai zo a zaɓen Shugaban ƙasa na 2027 – El-Eufai

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Tsohon Gwamnan Kaduna Nasir El-Rufai ya yi hasashen cewa Shugaba Bola Tinubu zai zo na uku ne a zaɓen shugaban ƙasa na 2027. El-Rufai jigo a jam’iyyar ADC, ya bayyana cewa Tinubu zai sha kashi a zaɓen 2027 idan ya tsaya takara, inda ya ce mafi yawan abin da zai samu shi ne zuwa na uku a zagaye na farko wanda hakan zai kai ga sake zaɓe ba tare da shi ba. El-Rufai ya bayyana haka a tattaunawa da tashar Channels a ranar Lahadi, inda ya shawarci Tinubu da ya ɗauki darasi daga tsohon…
Read More
Mambobin APC sama da 200 sun sauya sheƙa zuwa PDP a Jigawa 

Mambobin APC sama da 200 sun sauya sheƙa zuwa PDP a Jigawa 

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja  Aƙalla mambobi 289 na Jam’iyyar APC mai mulki sun sauya sheƙa zuwa jam’iyyar PDP a  mazaɓar Sakwaya, ƙaramar Hukumar Dutse, jihar Jigawa. Jaridar Manhaja ta rawaito cewa taron sauya sheƙar ya gudana ne a ranar Juma’a a ofishin PDP na mazaɓar, inda mataimakin shugaban jam’iyyar na jiha, Umar Danjani, ya wakilci shugaban jihar wajen tarbar sabbin mambobin. ɗanjani ya yaba wa fitattun ‘yan adawa da suka fito daga sassan jihar don halartar taron, yana mai bayyana sauya sheƙar a matsayin babban ƙarfafawa ga jam’iyyar wajen samun haɗin kai da ƙarfi gabanin zaɓe. Ya jaddada…
Read More
Wararrun ‘yan majalisar dokokin Zamfara sun yi Allah wadai da gwamnatin jihar kan matsalar tsaro

Wararrun ‘yan majalisar dokokin Zamfara sun yi Allah wadai da gwamnatin jihar kan matsalar tsaro

Daga SANUSI MUHAMMAD a Gusau Wararrun ƴan majalisar dokokin Jihar Zamfara ƙarƙashin jagorancin Rt Hon Bashar Aliyu Gummi ta sake yin Allah wadai da halin ko in kula da Gwamna Dauda Lawal Dare ke yi kan matsalar tsaro a jihar. 'Yan Majalisar sunyi kira ga gwamnatin tarayya da ta haɗa kai da jami’an tsaro a Zamfara domin ceto rayukan al’ummar jihar da dukiyoyinsu kamar yadda yake ƙunshe a kundin tsarin mulki Kashi na biyu. A zaman su na yau, ‘yan majalisar sun yi nasu bitar yadda ‘yan bindiga suka lalata jihar ta hanyar kai hare-hare a wasu al’ummomi da dama…
Read More
Sake zaɓen Tinubu zai lalata makomar Nijeriya — El-Rufai 

Sake zaɓen Tinubu zai lalata makomar Nijeriya — El-Rufai 

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja  Tsohon Gwamnan Jihar Kaduna, Nasir El-Rufai, ya ce idan Shugaba Bola Ahmed Tinubu da jam’iyyar APC suka sake lashe zaɓe a 2027, hakan zai lalata makomar ’yan Nijeriya. El-Rufai, ya faɗi haka ne a Jihar Sakkwato yayin wani gangamin wayar da kan jama’a da jam’iyyar adawa ta ADC, ta shirya. Ya ce yana goyon bayan wannan haɗaka, kuma zai taimaka wajen ganin ’yan Nijeriya sun sauke APC daga kan mulki. “Idan muka bar wannan gwamnati ta ci gaba da mulki zuwa karo na biyu, ragowar abin da ya rage na haɗin kai da amincewa…
Read More
Idan aka zaɓe ni zan yi wa’adi ɗaya na shekaru huɗu na sauka daga mulki – Obi 

Idan aka zaɓe ni zan yi wa’adi ɗaya na shekaru huɗu na sauka daga mulki – Obi 

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Tsohon ɗan takarar shugabancin Nijeriya a jam'iyyar Labour, Peter Obi ya ce idan ya samu nasarar zama shugaban ƙasar, wa'adi ɗaya na shekara huɗu kawai zai yi kamar yadda ya yi alƙawari. Obi ya bayyana haka ne a shafinsa na X, inda ya ce ko tsohon shugaban Amurka, Abraham Lincoln wa'adi ɗaya ya yi na shekara huɗu, "sannan John F. Kennedy bai ma ƙarasa wa'adi ɗaya ba, amma ana cigaba da tunawa da su a matsayin shugabanni masu adalci." Ya ce ko a Afirka, Nelson Mandela ya zama abin koyi a duniya wajen shugabanci…
Read More
2027: APC a Kano ta bayyana goyon baya ga Tinubu 

2027: APC a Kano ta bayyana goyon baya ga Tinubu 

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja  Masu ruwa da tsaki na Jam'iyyar APC a Jihar Kano sun bayyana goyon baya ga shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu domin ya sake tsayawa takara a zaɓe na biyu a 2027, tare da tabbatar da biyayyarsu ga jagoran jam’iyyar a Kano, Dr. Abdullahi Umar Ganduje. Sun bayyana goyon bayan ne a taron masu ruwa da tsaki na musamman da ya gudana a ranar Talata a gidan Ganduje da ke Kano. Taron ya mayar da hankali ne kan haɗin kan jam’iyya, shirin zabe mai zuwa, da kuma ci gaban da gwamnatin Tinubu ke samu a…
Read More
Dole a bar mana kujerar mataimakin shugaban ƙasa – Tsagin ANPP

Dole a bar mana kujerar mataimakin shugaban ƙasa – Tsagin ANPP

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja  Tsagin tsohuwar jam'iyyar All Nigeria Peoples Party wato ANPP da ke cikin babbar jam'iyyar APC da ke mulki a Nijeriya sun ce lallai ne a bar musu kujerar mataimakin shugaban ƙasa a zaɓen shekarar 2027, inda suka buƙaci shugaban ƙasar, Bola Tinubu ya yi watsi da buƙatar nemo wani daban. Tsagin ANPP ɗin sun ce su ne na biyu wajen ƙarfi a haɗakar da aka yi a shekarar 2013 da ta haifar da jam'iyyar APC, inda suka yi barazanar cewa yin watsi da su a tikitin takarar zaɓen 2027 zai iya tilasta musu su…
Read More
Bukar Guba ya yaba wa Blueprint kan karrama Gwamnan Yobe 

Bukar Guba ya yaba wa Blueprint kan karrama Gwamnan Yobe 

Daga GAMBO ISA a Abuja Shugaban ƙaramar Hukumar Bursari ta Jihar Yobe, Honorabul Lawan Bukar Guba, ya miƙa saƙon taya murna ga Hukumar Kamfanin Jaridar Blueprint bisa amincewa tare da karrama Mai Girma Gwamna Mai Mala Buni a matsayin Gwarzon Gwamna na shekarar 2024. A wata sanarwa da aka raba wa Blueprint, Hon. Lawan Bukar Guba ya bayyana karramawar a matsayin wadda ta dace kuma ta dace da shi, inda ya ba da misali da yadda gwamnan ya tabbatar da nasarorin da ya samu a muhimman fannoni kamar bunƙasa jarin ɗan Adam, ababen more rayuwa (musamman hanyoyi), ilimi, ICT, kiwon…
Read More
APC ta lashe zaɓen ƙananan hukumomin Legas

APC ta lashe zaɓen ƙananan hukumomin Legas

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Jam’iyyar APC mai mulki ta lashe dukkan kujerun shugabancin ƙananan hukumomi guda 30 a zaɓen ƙananan hukumomin da aka gudanar a Jihar Legas. Shugabar Hukumar ta (LASIEC), Mai Shari’a Bola Okikiolu-Ighile (mai ritaya) ce ta bayyana hakan yayin sanar da sakamakon zaɓen a wajen taron ’yan jarida a Sakatariyar Hukumar da ke Yaba a ranar Lahadi. Ta bayyana cewa jamiyyar APC ta kuma samu nasara a kujeru 375 daga cikin 376 na kansiloli a faɗin jihar, inda jam’iyyar PDP ta samu kujera guda daya a mazabar Ward D a Yaba. Shugabar hukumar zaben ta…
Read More