20
Jul
Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Darakta Janar na ƙungiyar masu biyayya ga Obi, Yunusa Tanko, ya bayyana cewa tsohon gwamnan jihar Anambra, Peter Obi, zai tsaya takarar shugaban ƙasa a 2027 ba tare da la’akari da samun tikitin jam’iyyar adawa ko a’a ba. Manhaja ta ruwaito cewa, gamayyar jam'iyyar adawa ta ƙasa ta amince da jam'iyyar Action Democratic Congress, ADC, a matsayin jam'iyyar da za ta fafata a zaɓen 2027. Sai dai tun bayan ɓullar ƙawancen 'yan adawa, aka fara nuna damuwa kan yadda aka ware tikitin takarar shugaban ƙasa na jam'iyyar. Da yawa daga cikin shugabannin ƙungiyar da…
