Siyasa

2027: Obi zai fice daga jam’iyyar haɗaka idan bai samu tikitin takara ba – Yunusa Tanko

2027: Obi zai fice daga jam’iyyar haɗaka idan bai samu tikitin takara ba – Yunusa Tanko

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Darakta Janar na ƙungiyar masu biyayya ga Obi, Yunusa Tanko, ya bayyana cewa tsohon gwamnan jihar Anambra, Peter Obi, zai tsaya takarar shugaban ƙasa a 2027 ba tare da la’akari da samun tikitin jam’iyyar adawa ko a’a ba. Manhaja ta ruwaito cewa, gamayyar jam'iyyar adawa ta ƙasa ta amince da jam'iyyar Action Democratic Congress, ADC, a matsayin jam'iyyar da za ta fafata a zaɓen 2027. Sai dai tun bayan ɓullar ƙawancen 'yan adawa, aka fara nuna damuwa kan yadda aka ware tikitin takarar shugaban ƙasa na jam'iyyar. Da yawa daga cikin shugabannin ƙungiyar da…
Read More
Tinubu na kitsa yadda zai gurgunta haɗakar ‘yan hamayya – ADC

Tinubu na kitsa yadda zai gurgunta haɗakar ‘yan hamayya – ADC

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Jam'iyyar African Democratic Congress wato ADC, wadda wasu manyan 'yan hamayya a Nijeriya suka haɗu a ƙarƙashinta domin ƙalubalantar Shugaba Tinubu a zaɓen 2027 ta yi zargin cewa akwai wasu daga cikin gwamnatin Tinubun da ke neman tarwatsa shirin 'yan phamayyar. A wata sanarwa da sakataren yaɗa labaranta na riko kuma kakakinta Malam Bolaji Abdullahi ya fitar a ranar Litinin, jam'iyyar ta ADC ta bayyana cewa an gayyaci tsofaffin shugabannin jam'iyyar na jihohi da manyan ƙusoshin kwamitin zartarwarta na jihohin arewa maso gabas da arewa maso yamma wata ganawa ta sirri da manyan jami'an…
Read More
Tsohon sakataren gwamnatin Nijeriya Babachir Lawal ya fice daga APC

Tsohon sakataren gwamnatin Nijeriya Babachir Lawal ya fice daga APC

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Tsohon Sakataren Gwamnatin Tarayya, Babachir David Lawal, ya bayyana ficewarsa daga jam’iyyar APC a hukumance, ta cikin wata wasiƙa da ya aikawa shugaban jam’iyyar na mazaɓarsa ta Banshika a ƙaramar hukumar Hong, jihar Adamawa. A wasiƙar da aka sanya ranar 29 ga Yuni, 2025, Babachir ya ce ficewarsa ta fara aiki nan take, tare da bayyana cewa zai bayyana sabuwar jam’iyyar da zai shiga a nan gaba kaɗan. Ya ce matakin na ɗaya daga cikin shirinsa na haɗa kai da sauran ‘yan Nijeriya domin gyara ƙasar daga kuskure da gazawar tsohuwar jam’iyyarsa ta APC…
Read More
Zan tsaya takarar Shugaban ƙasa a 2027 – Peter Obi

Zan tsaya takarar Shugaban ƙasa a 2027 – Peter Obi

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar Labour Party a zaɓen 2023, Peter Obi, ya tabbatar wa magoya bayansa cewa zai tsaya takarar shugaban ƙasa a zaɓen shekarar 2027, kuma ba zai yi fiye da wa’adi guda ba idan ya ci zaɓe. Mista Obi ya bayyana hakan ne a cikin wata sanarwa da mai magana da yawun Peter Obi Media Reports, Ibrahim Umar, ya fitar a ranar Litinin a Abuja. Tsohon ɗan takarar shugaban ƙasar ya tabbatar da cewa yana cikin tattaunawar kafa kawancen jam’iyyu, yana mai cewa burinsa shi ne ceton Nijeriya daga halin…
Read More
Har yanzu PDP na nan da ƙarfinta – Isa Ashiru

Har yanzu PDP na nan da ƙarfinta – Isa Ashiru

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Yayin da fagen siyasar Nijeriya ke ci gaba da ɗaukar ɗumi, wasu manyan 'yan siyasa a babbar jam'iyyar adawa ta PDP sun nanata cewa har yanzu jam'iyyar tana nan da ƙarfinta kuma a dunƙule. Shugabannin jam'iyyar sun kuma ce ana ci gaba da shirye-shiryen babban taron jam'iyyar don zaɓen shugabannin da za su ja ragamar ta. Honarabul Isa Ashiru Kudan, wanda ya yi wa jam'iyyar PDP takarar gwamnan jihar Kaduna har sau biyu - a shekarar 2019 da kuma 2023, ya shaida wa BBC cewa suna ɗaukar matakai waɗanda yanzu har sun kai ga…
Read More
2027: Lokacin ceto ya yi na haɗakar jam’iyyun adawa, inji Gafakan Akko

2027: Lokacin ceto ya yi na haɗakar jam’iyyun adawa, inji Gafakan Akko

Daga ABUBAKAR A. BOLARI a Gombe Wani malamin addinin Musulunci kuma shugaban makarantar AƙSAT ta Gombe, Dakta Auwal Abdullahi, wanda aka fi sani da Gafakan Akko, ya bayyana cikakken goyon bayansa ga ƙoƙarin da jam’iyyun adawa ke yi na haɗa ƙarfi da ƙarfinsu domin kawar da jam’iyyar APC a babban zaɓen 2027. A cikin wata hira da ya yi da manema labarai a Gombe, Dakta Auwal ya bayyana damuwarsa matuƙa kan yadda halin tsaro da tattalin arzikin ƙasa ke kara tabarbarewa a ƙarƙashin gwamnatin APC.  Ya ce wahalar da ‘yan Nijeriya ke ciki a yau ta kai matakin da bai…
Read More
Zan tsaya takarar Shugaban ƙasa a 2027 – Peter Obi

Zan tsaya takarar Shugaban ƙasa a 2027 – Peter Obi

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Dan takarar Shugaban ƙasa na jam’iyyar Labour Party a zaɓen 2023, Peter Obi, ya tabbatar wa magoya bayansa cewa zai tsaya takarar shugaban ƙasa a zaɓen shekarar 2027, kuma ba zai yi fiye da wa’adi guda ba idan ya ci zaɓe. Mista Obi ya bayyana hakan ne a cikin wata sanarwa da mai magana da yawun Peter Obi Media Reports, Ibrahim Umar, ya fitar a ranar Litinin a Abuja. Tsohon ɗan takarar shugaban ƙasar ya tabbatar da cewa yana cikin tattaunawar kafa ƙawancen jam’iyyu, yana mai cewa burinsa shi ne ceton Nijeriya daga halin…
Read More
Ba zan fice daga Jam’iyyar PDP ba – Muftwang

Ba zan fice daga Jam’iyyar PDP ba – Muftwang

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja  Gwamnan Jihar Filato da ke tsakiyar Nijeriya, Caleb Muftwang ya musanta rahotannin cewa yana daga cikin gwamnonin jam'iyyar adawa ta PDP da ke shirin komawa jam'iyya mai mulki ta APC. A kwanan nan ne dai wasu jaridun ƙasar suka ambato shi a cikin gwamnonin da ke shirin sauya sheƙa daga babbar jam'iyyar adawar daidai lokacin da rikicin cikin gida ya dabaibaye ta. To sai dai , Gwamna Muftawang ya shaidawa BBC cewa ba kamshin gaskiya a wannan zancen: ''Akwai abokina da ya turo man da wannan labari sai na ce ai ba a hana…
Read More
APC: Ra’ayin Tinubu kan murabus ɗin Ganduje da batun sauya sheƙar Kwankwaso

APC: Ra’ayin Tinubu kan murabus ɗin Ganduje da batun sauya sheƙar Kwankwaso

Daga MAHDI MUSA MUHAMMAD Jam’iyyar APC ta tabbatar da cewa tana gudanar da shawarwari game da batun maye gurbin tsohon shugabanta, Abdullahi Ganduje, wanda ya yi murabus a makon da ya gabata. Sakataren yaɗa labaran jam’iyyar, Feliɗ Morka a wata hira da gidan telebijin na ‘Channels’, ya ce APC tana aiki da lissafi wajen ganin ta cike gurbin da ganduje ya bari. Ya kuma ce, za a sanar da sabon shugaban jam’iyyar ne a yayin gudanar da babban zamanta na ƙasa, wanda kawo yanzu ba a bayyana ranar da za a yi haka ba. Game da batun yiwuwar tsohon gwamnan…
Read More
2027: Ba ni da sha’awar tikitin mataimakin shugaban ƙasa, inji Wamakko

2027: Ba ni da sha’awar tikitin mataimakin shugaban ƙasa, inji Wamakko

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Sanata mai wakiltar Sakkwato ta Arewa Sanata Aliyu Wamakko, ya nisanta kansa daga rahotannin da ke alaƙanta shi da wani raɗe-raɗin da ake yaɗawa na cewa yana son zama mataimakin shugaban ƙasa a 2027. A wata sanarwar manema labarai da ya rabawa manema labarai a safiyar Litinin, tsohon gwamnan jihar Sakkwato kuma Sarkin Yamman Sakkwato, ya bayyana iƙirarin a matsayin ƙarya, da kuma ɓata masa siyasa. Hakan na zuwa ne a matsayin martani ga wata sanarwa da aka danganta ga shugaban ƙaramar hukumar Kebbe, Abdullahi Yerima, wanda wata jarida ta buga. A cikin wata…
Read More