Siyasa

Ribar dimukraɗiyya sai hamdala a Zariya, amma a ƙara duba mata – Hajiya Salamatu

Ribar dimukraɗiyya sai hamdala a Zariya, amma a ƙara duba mata – Hajiya Salamatu

Daga ISAH GIDAN BAKKO a Zariya Wata fitacciyar 'yar siyasa a Jam'iyyar APC a ƙaramar hukumar birnin Zariya, Hajiya Salamatu ta bayyana yadda wasu zaɓaɓɓu ke rabon ribar dimukuraɗiyya a gundumomi goma sha uku a ko ƙaramar hukumar Zariya sai dai ta koka na yadda mata ba a yayyafa masu kamar yadda ake yayyafa wa maza ba a cewarta. Hajiya Salamatu ta ci gaba da cewa duk wani ɗan siyasa da kuma waɗanda ba ma siyasar suke yi ba, ya san jam'iyyar APC ta yi sa'ar samun wakilai guda biyu da suka san yadda al'umma suka yi amfani da damar…
Read More
Da Ɗumi-ɗumi: Kotun Ƙoli ta yi watsi da buƙatar Atiku ta neman gabatar da sabuwar hujja a kan Tinubu

Da Ɗumi-ɗumi: Kotun Ƙoli ta yi watsi da buƙatar Atiku ta neman gabatar da sabuwar hujja a kan Tinubu

Daga BASHIR ISAH Kotun Ƙoli ta yi watsi da buƙatar da tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa kuma ɗan takarar shugabancin ƙasa na Jam'iyyar PDP, Atiku Abubakar, ya gabatar wa kotun ta neman kotu ta ba shi damar gabatar mata da sabuwar hujja a kan Shugaban Ƙasa Bola Tinubu. Atiku ya buƙaci kotun da ta ba shi damar gabatar da bayanan da ya ce ya samo game da karatun da Tinubu ya ce ya yi a Jami'ar Jihar Chicago ta ƙasar Amurka. Tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasar na ra'ayin cewa bayanan bogi ne Tinubu ya miƙa wa Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC) a…
Read More
Kotun Ƙoli: Gobe su Atiku za su san matsayinsu

Kotun Ƙoli: Gobe su Atiku za su san matsayinsu

Daga BASHIR ISAH A ranar Alhamis ta wannan makon Kotun Ƙoli za ta yanke hukunci kan ƙarar da 'yan takarar shugabancin ƙasa ƙarƙashin jam'iyyun PDP da LP, Atiku Abubakar da Peter Obi suka shigar inda suke ƙalubalantar nasarar da Shugaba Bola Tinubu ya samu wadda Kotun Ɗaukaka Ƙara ta tabbatar masa da ita. Daraktan Yaɗa Labarai na Kotun Ƙoli, Dr Awemeri Festus Akande, shi ne ya bayyana hakan a ranar Laraba. Ya ce an ɗauki matakan tsaron da suka kamata domin tabbatar da lumana a ciki da wajen kotun. Baya ga rashin gamsuwa da nasarar Tinubu, Atiku yana kuma neman…
Read More
Tinubu ya naɗa sabbin kwamishinonin INEC na jihohi guda tara

Tinubu ya naɗa sabbin kwamishinonin INEC na jihohi guda tara

Daga BASHIR ISAH Shugaba Bola Tinubu ya amince da naɗin kwashinonin zaɓe na jihohi (RECs) guda tara ga Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC) na wa'adin shekara biyar. Tinubu ya naɗa kwamishinonin zaɓen ne kafin daga bisani Majalisar Dattawa ta tabbatar da naɗin nasu. Bayanin naɗin na ƙunshe ne cikin sanarwar da mai magana da yawun Shugaban Ƙasa, Ajuri Ngelale, ya fitar a ranar Laraba. Sanarwar ta ce Tinubu ya yi naɗin ne bisa damar da Sashe na 154 (1) na Kundin Tsarin Mulkin Nijeriya na 1999 wanda aka yi wa kwaskwarima, da Sashe na 6 na Dokar Zaɓe ta 2022…
Read More
Shugaban INEC ya gana da jam’iyyun siyasa gabanin zaɓen gwamnoni a jihohin Kogi, Bayelsa, Imo

Shugaban INEC ya gana da jam’iyyun siyasa gabanin zaɓen gwamnoni a jihohin Kogi, Bayelsa, Imo

Shugaban Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC), Mahmood Yakubu, ya gana da shugabannin jam'iyyun siyasa a hedikwatar hukumar da ke Abuja a ranar Talata. Taron ɓangare na shirye-shiryen da INEC ke yi don gudanar da zaɓen gwamnoni a jihohin Kogi da Bayelsa da kuma Imo nan gaba kaɗan. Ana sa sa ran shugaban INEC ya yi wa jam'iyyun bayanin shirye-shiryen INEC kan zaɓuɓɓukan da kuma rawar da Jam'iyyun za su taka. Kazalika, taron wata dama ce ga jam'yyun da lamarin ya shafa su bayyana wa shugban INEC damuwarsu da sauran lamurran da suka yi la'akari da su gabanin zaɓen.
Read More
Jaruma Tonto Dikeh ta sauya sheƙa zuwa APC

Jaruma Tonto Dikeh ta sauya sheƙa zuwa APC

Jaruma a masana'antar Nollywood wadda ta tsunduma harkar siyasa, Tonto Dikeh, ta sauya sheƙa ta koma Jam'iyya mai mulki ta APC. Jarumar ta koma APC ne bayan da ta fice daga Jam'iyyar hamayya ta African Democratic Congress (ADC). Jarumar ta yi takarar mataimakin gwamna ƙarƙashin ADC yayin zaɓen 2023 a Jihar Ribas. A wannan Litinin ɗin ake sa ran Shugabar Matan APC ta Ƙasa, Dr Mary Alile, za ta karɓi Tonto Dikeh a Sakatariyar APC da ke Abuja da misalin ƙarfe 3 na rana. A shekarun baya-bayan nan, an ga yadda jaruman fina-finai na Arewaci da Kudancin Nijeriya suka ba…
Read More
Kotun Ƙoli ta yi watsi da ƙarar APM kan ƙalubalantar nasarar Tinubu

Kotun Ƙoli ta yi watsi da ƙarar APM kan ƙalubalantar nasarar Tinubu

Kotun Ƙoli ta yi watsi da ƙarar da Jam'iyyar Allied People’s Movement (APM) ta shigar inda take ƙalubalantar nasarar da Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya samu a zaɓen 2023. A ranar Litinin Kotun ta yi watsi da ƙarar bayan da mai ƙarar ta janye ƙarar da ta ɗaukaka. APM ta ɗaukaka ƙarar ne don ƙalubalantar sakamakon zaɓen shugaban ƙasa na 2023 wanda Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC) ta bayyana Tinubu a matsayin wanda ya lashe zaɓen. Tun da fari, Jam'iyyar ta AMP ta nuna rashin gamsuwarta da hukuncin Kotun Sauraron Ƙararrakin Zaɓen Shugaban Ƙasa ta yanke wanda hakan ya…
Read More
Mutum uku ne suka ɗora Tinubu

Mutum uku ne suka ɗora Tinubu

Daga BELLO MUHAMMAD SHARAƊA Ranar 25 ga watan Fabrairu 2023, jama'ar ƙasar nan suka fita filin zaɓe domin su zaɓi wanda zai mulke su tsawon shekara huɗu. Mutum huɗu ne suka fi samun tagomashi. Na ɗaya, ɗan takarar jam'iyyar APC wadda ke kan mulki, Jagaban Borgu, Bola Ahmed Tinubu. Na biyu Wazirin Adamawa Atiku Abubakar na PDP, na uku Peter Obi, na LP, sai na hudu Injiniya Rabiu Kwankwaso na NNPP. Hukumar zaɓe ta ƙasa ta bai wa mutane miliyan 93 katin zaɓe. Amma da aka zo hakikanin zaven, kashi 27 ne suka fito. Da quri'ar Tinubu da Atiku da…
Read More
Kotu ta tsige ɗan Majalisar Wakilai daga Adamawa

Kotu ta tsige ɗan Majalisar Wakilai daga Adamawa

Kotun Ɗaukaka Ƙara mai zamanta a Abuja ta tsige ɗan Majalisar Wakilai daga Jihar Adamawa, wato Hon. Jingi Rufai, na jam'iyyar PDP. Kafin wannan lokaci, Jingi Rufai shi ne mai wakiltar Mubi ta Arewa, Mubi ta Kadu da Maiha a Majalisar Wakilai ta Ƙasa. Kotun ta yanke hukuncin haka ne a zaman da ta yi a ranar Talata, inda ta bayyana ɗan takarar jam'iyyar APC, Hon. Jaafar Magaji, a matsayin wanda ya lashe zaɓe. Kotun ta kuma bai wa hukumar zaɓe IMEC umarni a kan ta miƙa wa Magaji shahadar lashe zaɓen ba tare da wani jinkiri ba. Wannan na…
Read More
Dalilin Sanata Ndume na ficewa daga zauren Majalisa a fusace

Dalilin Sanata Ndume na ficewa daga zauren Majalisa a fusace

Da alama dai abubuwa ba su tafiya yadda ya kamata wa Majalisar Dattawan Nijeriya musamman ganin yadda shugabanin majalisar suka shiga ganawar sirri mintoci ƙalilan da fara zaman majalisar a ranar Talata. Yayin zaman Majalisar a ranar Talata an ga Mai Tsawatarwa na Majalisar, Sanata Ali Ndume (APC Borno ta Kudu), ya yi ƙoƙarin nusar da Majalisar dangane da kurakuran da ake zargi Shugaban Majalisar, Godswill Akpabio ya tafka ba tare da an yi gyara ba. Kuskuren da Ndume ke nufi shi ne kan batun ƙudirin da Sanata Summaila Kawu (NNPP Kano ta Kudu) ya gabatar a majalisa kan buƙatar…
Read More