Siyasa

Jam’iyyar ADC a Kano ta yi taron gangami da jam’iyyu don ƙwace mulki a hannun APC

Jam’iyyar ADC a Kano ta yi taron gangami da jam’iyyu don ƙwace mulki a hannun APC

Daga IBRAHIM MUHAMMAD a Kano Jam'iyyar ADC mai alamar musabaha reshen jihar Kano, ta gudanar da taron gangamin na ƙoƙarin haɗa kan jam'iyyu domin yanda za a haɗu domin a tunkari kawar da jam'iyya mai mulki a zaɓe mai zuwa. Taron ya sami halartar dukkanin musu ruwa da tsakin jam'iyyar ADC na jihar da wakilan wasu jam'iyu da suka haɗa da PDP da PRP da sauran wasu jam'iyyun da kuma wasu  malaman jamia da suka gabatar da jawabai akan abinda ya shafi haɗin kai. A yayin taron daya gudana a ɗakin taro na Mumbayya  tsohon ɗan takarar Gwamnan jihar Kano…
Read More
Buni ya bai wa manoma 1,000 tallafin aikin gona

Buni ya bai wa manoma 1,000 tallafin aikin gona

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Gwamnan jihar Yobe, Mai Mala Buni, ya raba kayayyakin noma ga magidanta 1,000 da suka haɗa da ‘yan gudun hijira daga Mandunari da ke ƙaramar Hukumar Gujba da sauran al’ummomin da suke zaune a yankin. Da yake jawabi a gidan gwamnati da ke Damaturu, Buni ya bayyana cewa, duk da cewa al’ummomin Mandunari ya kasance su ne yankin al’umma guda ɗaya tilo a jihar Yobe da har yanzu ba a sake tsugunar da su ba, al’ummarta sun nuna jajircewarsu na komawa gidajen kakanninsu. Ya kuma jaddada ƙudirin gwamnatin jihar na tabbatar da dawowar duk…
Read More
Rashin adalci da son kai a PDP ya sa muka bar ta – Mustapha Inuwa

Rashin adalci da son kai a PDP ya sa muka bar ta – Mustapha Inuwa

Daga ABDULLAHI MUHAMMAD a Katsina Babban jam'iyyar adawa ta PDP a Katsina na gab da rugujewa, hakan ya biyo bayan ficewa da jiga jigan ya'yan jam'iyar keyi. Na baya bayan nan sune ƙungiyar tsaffin yan takara na jam'iyar adawa ta PDP a jihar da suka sauya sheka zuwa sabuwar tafiyar a Jihar Katsina. Tsaffin yan takarar da suka sauya sheka su 287 sun haɗa da yan takarar kujerar ɗan majalisa 24 da na kujerar shugabancin ƙaramar hukuma su 13 da su kayi takara a shekarar 2022 da 2025. Sai 'yan takarar kujerar kansila 240 da suka fito daga ƙananan hukumomi…
Read More
2027: Masu sauya sheƙa zuwa APC masu zunubi ne da ke neman gafara – Dalung

2027: Masu sauya sheƙa zuwa APC masu zunubi ne da ke neman gafara – Dalung

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Tsohon Ministan Matasa da Ci gaban Wasanni, Solomon Dalung, ya bayyana 'yan siyasa da ke sauya sheƙa daga jam’iyyun hamayya zuwa jam’iyyar APC mai mulki a matsayin masu zunubi da ke neman gafara. Dalung, yayin da ya ke jawabi a Abuja, ya musanta ra’ayin da ke cewa ‘yan siyasa na komawa APC ne saboda jam’iyyar ta tabuka abin a zo a gani. A cewarsa, “a’a, masu zunubi ne da ke neman gafara daga zunubansu da dama.” Dalung ya ce masu sauya sheƙar suna kawai cika abin da tsohon Gwamnan Jihar Edo, Adams Oshiomhole, ya…
Read More
Zan iya mutuwa a kan APC, inji Uzor Kalu

Zan iya mutuwa a kan APC, inji Uzor Kalu

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja  Tsohon Gwamnan Jihar Abia, Orji Uzor Kalu, ya sake jaddada cewa a shirye ya ke ya ba da ransa akan jam’iyyar APC, musamman a jihar Abia. Ya bayyana haka ne a hirarsa da manema labarai a garinsu na Igbere, Jihar Abia. Da aka tambaye shi ko APC na da wata dama ta kayar da jam’iyyar Labour Party (LP) a zaɓen 2027 a jihar Abia, Kalu wanda ke wakiltar Abia ta Arewa a Majalisar Dattawa, ya ce shi da sauran magoya bayan APC za su yi aiki tuƙuru domin nasarar shugaban ƙasa a jihar. Ya…
Read More
Na shirya yin haɗaka don ƙalubalantar Tinubu a 2027 – Amaechi

Na shirya yin haɗaka don ƙalubalantar Tinubu a 2027 – Amaechi

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Tsohon Ministan Sufuri kuma jigo a Jam’iyyar APC mai mulki, Rotimi Amaechi, ya bayyana cewa ya shirya yin haɗaka da wasu ’yan siyasa domin ƙalubalantar Shugaba Bola Ahmed Tinubu a zaɓen 2027. A wata hira da ya yi da BBC, Amaechi ya ce matsin tattalin arziƙi da tsadar rayuwa da ake fuskanta a ƙasar ne babban dalilin da ya sa ake buƙatar sabuwar haɗaka a siyasa. Ko da yake bai tabbatar da cewa zai tsaya takarar shugaban ƙasa ba, sai dai ya ce komai zai bayyana nan da wani lokaci. “Lokaci ne kawai zai…
Read More
Zai fi kyau Tinubu ya mayar da hankali kan ’yan Nijeriya ba zaɓen 2027 ba — ACF

Zai fi kyau Tinubu ya mayar da hankali kan ’yan Nijeriya ba zaɓen 2027 ba — ACF

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Kungiyar Tuntuɓa ta Arewacin Nijeriya ACF ta bukaci Shugaba Bola Tinubu da manyan muƙarraban gwamnatinsa da su daina gaggawar shige-da-fice wajen neman tazarce a Zaɓen 2027. ACF ta ce zai fi dacewa gwamnatin Tinubun ta mayar da hankali wajen ganin ta kyautata rayuwar ’yan Nijeriya maimakon gangamin yaƙin neman a sake zaɓensa a 2027, lamarin da ƙungiyar ke cewa hakan ya yi wuri. Wannan kira dai na kunshe cikin wata sanarwar yi wa musulmi barka da Sallah Babba da kakakin ƙungiyar na ƙasa, Farfesa Tukur Muhammad-Baba ya fitar. ƙungiyar ta bayyana rashin jin daɗinta…
Read More
Ba zan iya zama da El-Rufai a jam’iyya ɗaya ba, Sanata Wadada na shirin ficewa daga SDP

Ba zan iya zama da El-Rufai a jam’iyya ɗaya ba, Sanata Wadada na shirin ficewa daga SDP

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Sanata mai wakiltar mazaɓar Nasarawa ta yamma, Ahmed Wadada, ya bayyana shirinsa na ficewa daga jam’iyyar Social Democratic Party, SDP, zuwa jam’iyyar APC. Wadada ya bayyana hakan ne yayin wata tattaunawa da manema labarai a garin Keffi na jihar Nasarawa a ranar Asabar. A cewarsa, sauya sheka da tsohon gwamnan jihar Kaduna Nasir El-Rufai ya yi zuwa SDP na daga cikin manyan dalilan da suka sa ya yanke wannan shawarar. Ya ce ba zai iya zama jam’iyya da El-Rufai ba saboda bambancin akida ta siyasa. "Duk da cewa Malam El-Rufai yayana ne, amma ba…
Read More
PDP za ta gurfanar da Matawalle a gaban kotu bisa zargin ɓata sunan Gwamna Lawal

PDP za ta gurfanar da Matawalle a gaban kotu bisa zargin ɓata sunan Gwamna Lawal

Daga SANUSI MUHAMMAD a Gusau Jam'iyyar PDP a Jihar Zamfara ta yanke shawarar maka ƙaramin ministan tsaro, Honorabul Bello Matawalle a kotu bisa zargin ɓata sunan gwamnan jihar Dauda Lawal. Bayanin hakan na ƙunshe ne a cikin wata sanarwa mai ɗauke da sa hannun sakataren yaɗa labaran jam’iyyar na jihar, Halliru Andi wanda ya rabawa manema labarai a Gusau. Haliru Andi ya ce jam’iyyar PDP ta kammala shirye-shiryen ɗaukar matakin shari’a a kan Matawalle kan kisan gillar da ya yi da kuma ikirarin ɓata suna ga Gwamna Dauda Lawal. Ya ce, "Kwamitin gudanarawa na jam'iyyar PDP reshen jihar Zamfara (SWC)…
Read More
Wike ya sha alwashin jan zugar yaƙin neman zaɓen Tinubu a 2027, ya yi iƙirarin ba yadda PDP ta iya da shi

Wike ya sha alwashin jan zugar yaƙin neman zaɓen Tinubu a 2027, ya yi iƙirarin ba yadda PDP ta iya da shi

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Ministan babban birnin tarayya Abuja, Nyesom Wike, ya ce, shi ne zai jagoranci yaƙin neman zaɓen Shugaban Tinubu na 2027 a jihar Ribas. Wike ya bayyana hakan ne a Abuja a ranar Litinin a yayin wata hira da gidan talabijin na Channels. Duk da kasancewarsa ɗan jam’iyayar PDP ne, amma yanzu Ministan Abujan a ƙarƙashin gwamnatin Tinubu ɗan jam’iyyar APC. Ana dai zargin Wike da cin dunduniyar PDP saboda gwamnatin Tinubu sai dai a kodayaushe yakan ce shi ɗan PDP ne na gani kashe ni wanda kuma ya ci ribarta. Sannan an yi wa…
Read More