Siyasa

El-Rufa’i da Amaechi manyan maƙiyan ci gaban ƙasa ne, inji Yerima Shettima 

El-Rufa’i da Amaechi manyan maƙiyan ci gaban ƙasa ne, inji Yerima Shettima 

Daga ABBA MUHAMMAD a Kaduna Shugaban ƙungiyar Tuntuɓa ta Matasan Arewa (AYCF), Alhaji Yerima Shettima, ya yi martani dangane da kalaman da tsohon Gwamnan jihar Kaduna El-Rufa’i da tsohon Minista Rotimi Amaechi suka yi a taron da suka yi a Abuja, inda ya bayyana kalaman nasu a matsayin soki burutsu. Yerima Shettima ya ƙara da cewar a daidai lokacin da Nijeriya ke ƙoƙarin farfaɗowa daga matsalolin da suka addabe ta ɓangaren tsaro da tattalin arziki, abin takaici ne a samu irin waɗannan kalamai marasa kan gado na fita daga bakin waɗanda ake yi musu kallon manya. Ya ƙara da cewar…
Read More
PRP za ta yi aiki tuƙuru don kawar da mulkin zalunci da ake a ƙasar nan – Abba Namatazu

PRP za ta yi aiki tuƙuru don kawar da mulkin zalunci da ake a ƙasar nan – Abba Namatazu

Daga IBRAHIM MUHAMMAD a Kano An bayyana cewa a tsarin ƙasar nan tun 1999 kusan tafiyar jam'iyyar ɗaya ake sai dai idan lokaci ya zo sun fahimci mutane sun gane abinda ake nufi sai a sauya mata suna ta ƙarfafa wata jam'iyyar.  Injiniya Abba Sule Namatazu mataimakin shugaban jam'iyyar PRP na ƙasa mai kula da shiryar Arewa maso yamma ne ya bayyana hakan a taron da jam'iyyar ta gudanar a ranar Asabar a ɗakin taro na gidan Mumbayya. Ya ce a baya sunan jam'iyyar dake mulkin ƙasa ita ce PDP sai aka yi bula-bula ta koma APC, mun ce jam'iyya…
Read More
SDP ba ta sayarwa ko jinginarwa ba ce, jam’iyyar ta faɗa wa haɗakar su Atiku 

SDP ba ta sayarwa ko jinginarwa ba ce, jam’iyyar ta faɗa wa haɗakar su Atiku 

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Jam’iyyar Social Democratic Party (SDP) ƙarƙashin jagorancin Wole Adesina ta bayyana da kakkausar murya cewa jam’iyyar ba ta sayarwa ba ce kuma ba ta haya ba ce ga wani ƙawance ko motsi na siyasa. A wata sanarwa da ya fitar ranar Litinin a Abuja, sakataren yaɗa labaran jam’iyyar na ƙasa, Barista Alfa Mohammed, ya jaddada cewa ba za a yi amfani da jam’iyyar SDP a matsayin wata kafa ta ƙaddamar da hare-hare kan shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ba ko kuma inganta duk wani ƙawancen da ba shi da wata manufa mai inganci don…
Read More
Yadda rikicin PDP ya ƙara ta’azzara bayan da alaƙa ta yi tsami tsakanin Wike da Makinde 

Yadda rikicin PDP ya ƙara ta’azzara bayan da alaƙa ta yi tsami tsakanin Wike da Makinde 

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Da alama jam'iyyar hamayya ta PDP na ƙara tsunduma cikin rikicin da ka iya yi mata illa a shirinta na tunkarar zaɓe mai zuwa a 2027, inda 'ya'yan jam'iyyar guda biyu Nyesom Wike, ministan babban birnin Nijeriya da Seyi Makinde, gwamnan jihar Oyo suka sanya zare. Nyesom Wike dai ya zargi Seyi Makinde da "lalata jam'iyyar" inda ya ce bai mutunta duk wasu yarjeniyoyin aka yi ba dangane da yadda za a warware taƙaddamar da jam'iyyar ke fama da ita a tsawon lokaci. Nyesom Wike da Seyi Makinde sun kasance abokan tafiya a jam'iyyar…
Read More
Ba zan sake halartar taron PDP ba har sai an kori Wike da Ortom – Sule Lamido 

Ba zan sake halartar taron PDP ba har sai an kori Wike da Ortom – Sule Lamido 

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Tsohon Gwamnan Jihar Jigawa, Sule Lamido, ya bayyana Ministan Babban Birnin Tarayya Abuja, Nyesom Wike, a matsayin annoba da ya kamata a kore shi daga jam’iyyar PDP. Lamido ya bayyana haka ne a wata tattaunawa ta wayar tarho da aka yi da shi a Abuja a jiya Talata. Ya bayyana cewa ko da yake har yanzu yana cikin jam’iyyar PDP, wacce ya taimaka wajen kafuwa ya yanke shawarar dakatar da halartar tarukan shugabanci na jam’iyyar – duk da zafin hakan – matuƙar Wike da tsohon Gwamnan Jihar Benue, Samuel Ortom, na ci gaba da…
Read More
Ba dole sai na zama shugaban Nijeriya ba — Peter Obi

Ba dole sai na zama shugaban Nijeriya ba — Peter Obi

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja  Tsohon ɗan takarar shugaban Nijeriya a ƙarƙashin jam’iyyar Labour a Zaɓen 2023, Peter Obi, ya ce ba dole ba ne sai ya zama shugaban ƙasar nan ba. Sai dai Peter Obi ya ce yana so ya ga ƙasar tana aiki yadda ya kamata a ƙarƙashin jagoranci nagari. Gidan Talabijin na Channels ya ruwaito Obi yana bayyana haka ne lokacin bikin murnar cika shekara biyu kan mulki na Gwamnan Abia, Aleɗ Otti. Ya ce ya kamata a samu shugabanni waɗanda mutane za su yi alfahari da su. Ya ƙara da cewa haƙƙin shugaba ne ya…
Read More
Gwamnonin PDP sun zargi Gwamnatin Tarayya da amfani da dabarun tsoratarwa

Gwamnonin PDP sun zargi Gwamnatin Tarayya da amfani da dabarun tsoratarwa

Daga MAHDI MUSA MUHAMMAD Gwamnonin jam’iyyar PDP sun zargi Gwamnatin Tarayya da amfani da dabarun tsoratarwa tare da maida su saniyar ware. Gwamnonin na PDP sun sha alwashin ain yarda da irin waɗannan matakai tare da jajircewa wajen ci gaba da gudanar da mulki na gari. Sun bayyana hakan ne yayin taron kwamitin zartaswa na ƙasa (NEC) karo na 99 na jam’iyyar PDP da aka gudanar a ranar Talata a birnin tarayya Abuja. Shugaban ƙungiyar Gwamnonin PDP, kuma gwamnan jihar Bauchi, Sanata Bala Mohammed, wanda ya yi jawabi a wajen taron, ya bayyana irin ƙalubalen da jam’iyyar da mambobinta ke…
Read More
Na fi tsofaffin kansiloli 3,000 da Gwamna Abba ya biya haƙƙoƙinsu murna – Hon. Nagoda

Na fi tsofaffin kansiloli 3,000 da Gwamna Abba ya biya haƙƙoƙinsu murna – Hon. Nagoda

Daga MUHAMMADU MUJITABA a Kano Hon. Alhajiji Nagoda mai bai wa gwamnan Kano shawara kan harkar yaɗa labarai kuma wanda  ya wakilci Hon. Abdullahi Ibrahim Wayya, Kwamishinan yaɗa labarai na Kano ya bayyana cewa shi da abokin aikinsa Hon. Zawa'i da suka kawo wa gwamna labarin halin da tsofaffin kansiloli tun daga na 2014 zuwa 2024 suke ciki, gwamnan Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf kuma suka ba shi shawara kan ya biya su kuma ya yarda ya biya su su kimmanin 3000 ba tare da la'akari da yadda wasu suka nuna masa hamayya da adawa kasancewa ba jam'iyyarsu ɗaya ba…
Read More
2027: Za mu maida Tinubu Legas – El-Rufai ya tabbatar da haɗakar Atiku da Obi

2027: Za mu maida Tinubu Legas – El-Rufai ya tabbatar da haɗakar Atiku da Obi

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Tsohon gwamnan jihar Kaduna, Malam Nasir El-Rufai, ya tabbatar da haɗakar da ta haɗa da tsohon mataimakin shugaban ƙasa Atiku Abubakar da ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar Labour a 2023, Peter Obi, da nufin kawar da shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu a 2027. El-Rufai ya tabbatar da hakan ne yayin da yake jawabi a ranar Laraba a taron Arewa TechFest a Katsina. Ya ce, "Jiya da ƙarfe 8 na dare, an yi wani muhimmin taro na haɗin gwiwa da muke haɗawa domin tabbatar da cewa Shugaba Tinubu ya koma Legas." Manhaja ta ruwaito…
Read More
2027: Dukkan gwamnonin yankin Kudu maso Gabas Tinubu za su yi – Umahi

2027: Dukkan gwamnonin yankin Kudu maso Gabas Tinubu za su yi – Umahi

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja  Ministan ayyuka Dave Umahi ya ce dukkan gwamnonin yankin Kudu maso gabas suna goyon bayan shugaba Tinubu inda ya buƙaci waɗanda ba su yanke shawara ba kamar Peter Obi da su bi sahun sauran gwamnonin. Sannan ya ce an kusa kammala aikin titin Lahadi zuwa Calabar kuma daga watan Disamba masu amfani da hanyar za su riƙa biyan haraji. Mista Umahi ya bayyana hakan ne a wata hira da aka yi da shi a yayin shirye-shiryen murnar cika shekaru biyu da hawan mulkin shugaba Tinubu. Ya ce dukkan gwamnonin yankin Kudu maso gabas suna…
Read More