Siyasa

SDP Gombe ta ƙaryata naɗin bogi, ta zargi maƙarƙashiya don haddasa rikici

SDP Gombe ta ƙaryata naɗin bogi, ta zargi maƙarƙashiya don haddasa rikici

Daga ABUBAKAR A BOLARI a Gombe Jam’iyyar Social Democratic Party (SDP) reshen Jihar Gombe ta fito fili ta karyata ikirarin wani naɗin shugabanci bogi da ake dangantawa da ita, tare da gargadi kan wani taron sirri da ake zargin an shirya domin kawo rarrabuwar kawuna a jam’iyyar. A wata sanarwa da Ambasada Injiniya M. Abdulkadir Kumo, mai ba da shawara na musamman kan harkokin watsa labarai ga shugaban jam’iyyar na jiha ya fitar, jam’iyyar ta bayyana cewa ba ta taba amincewa da naɗin Dokta Sadiƙ Abubakar Gombe a matsayin Mataimakin Shugaban Jam’iyyar na ƙasa (Arewa) ba, tana kira ga jama’a…
Read More
Sanatocin PDP na Osun sun nuna goyon baya ga Tinubu a 2027

Sanatocin PDP na Osun sun nuna goyon baya ga Tinubu a 2027

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Sanatocin da aka zaɓa ƙarƙashin jam’iyyar PDP a jihar Osun sun bayyana goyon bayansu ga Shugaba Bola Tinubu a gabanin zaben shugaban ƙasa na 2027. Sanatocin — Kamarudeen Oyewumi (Osun ta yamma), Olubiyi Ajagunla (Osun ta tsakiya), da Francis Fadahunsi (Osun ta gabas) — sun bayyana matsayinsu ne a wata sanarwa da suka fitar tare a ranar Laraba. Goyon bayan ya biyo bayan wata ganawa da suka yi a ranar Talata. ‘Yan majalisar sun bayyana goyon bayansu ga shugabancin Tinubu, suna ambato tarihin sa wajen jagoranci, sauye-sauyen tattalin arziki da kuma ci gaban ababen…
Read More
PDP za ta zama gawa nan da ƙarshen 2025 – Ganduje

PDP za ta zama gawa nan da ƙarshen 2025 – Ganduje

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja  Abdullahi Umar Ganduje, shugaban jam’iyyar APC na ƙasa, ya bayyana cewa jam’iyyar PDP na kan hanyarta ta rushewa gaba ɗaya. Ganduje ya mayar da martani ne ga kalaman tsohon gwamnan jihar Jigawa, Sule Lamido, wanda ya ce APC za ta watse nan ba da daɗewa ba, kuma tsofaffin 'yan PDP da suka hada da Ganduje za su koma jam’iyyar adawa. A cikin wata sanarwa da mai taimaka masa na musamman kan harkokin yaɗa labarai, Edwin Olofu, ya fitar a ranar Lahadi, Ganduje ya bayyana wadannan kalaman da “marasa tushe kuma marasa ma’ana.” Ya ce…
Read More
PDP ta kafa kwamitin sulhu ƙarƙashin Saraki

PDP ta kafa kwamitin sulhu ƙarƙashin Saraki

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Kwamitin Amintattun babbar jam'iyyar adawa a Nijeriya wato PDP ta rantsar da kwamitin sulhu mai ɗauke da mutum 20 a wani mataki na ƙara haɗa kan 'yan jam''iyyar a matakai daban-daban na ƙasar. Shugaban kwamitin amintattun PDP, Adolpus Wabara ya ce nan ba da jimawa ba jam'iyyar za ta kawo ƙarshen ka-ce-na-cen da ya dabaibaye ta tsawon lokaci, tare da ɗaukar matakai kan masu yi wa jam'iyyar zagon ƙasa.Ya ce wannan matakin zai ƙara tabbatar da cewa "waɗanda ke ficewa daga jam'iyyar da ma su ne matsalar jam'iyyar," inda ya ƙara da cewa yanzu…
Read More
Karrama Kwankwaso da Jami’ar Ɗangote ta yi da digirin girmamawa an yi abin da ya kamata – Hon. Nura Dala 

Karrama Kwankwaso da Jami’ar Ɗangote ta yi da digirin girmamawa an yi abin da ya kamata – Hon. Nura Dala 

Daga IBRAHIM MUHAMMAD a Kano Babban hadimi na musamman ga Sanatan Kano ta Tsakiya, Hon. Nura Maiƙarfi Dala ya bayyana karramawar da jami'ar kimiyya da fasaha ta Aliko ɗangote ta yi wa jagoran kwankwasiyya  Sanata Dakta Rabiu Musa Kwankwaso da digirin girmamawa da cewa  an yi abinda ya kamata. Ya ce ba shi digirin girmamawar tabbas an ajiye kwarya a gurbinta ne, idan aka yi la'akari da irin gudummuwa da ya bai wa jihar Kano musamman a harkar ilimi. Hon. Nura Maiƙarfi Dala ya yi nuni da cewa su ma waɗanda jami'ar ta karrama da suka haɗa da shugaban kamfanin…
Read More
Tsarin jam’iyya ɗaya a Nijeriya ba zai haifar da ɗa mai ido ba, inji Jonathan 

Tsarin jam’iyya ɗaya a Nijeriya ba zai haifar da ɗa mai ido ba, inji Jonathan 

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Tsohon Shugaban ƙasar Nijeriya, Goodluck Jonathan ya ce ƙoƙarin komawa tsarin jam'iyya ɗaya ta hanyar “ƙarfa-ƙarfar ar siyasa” zai jefa ƙasar cikin rikici. Manhaja ta rawaito cewa Jonathan ya yi wannan furuci ne a ranar Laraba a wajen bikin tunawa da kuma gabatar da jawabin girmamawa ga Marigayi Edwin Clark, fitaccen shugaba daga yankin Ijaw. An gudanar da taron ne a Abuja, inda manyan ’yan siyasa suka halarta. Tsohon shugaban ƙasar ya ce batun mayar da Nijeriya ƙasa mai jam’iyya ɗaya yana tayar da ƙura a kafafen sada zumunta. Jonathan ya ce ko da…
Read More
Kotu ta dakatar da taron Jam’iyyar PDP na Ekiti

Kotu ta dakatar da taron Jam’iyyar PDP na Ekiti

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja A ranar Laraba ne wata babbar kotun jihar Ekiti da ke Ado-Ekiti ta bayar da umarnin dakatar da gudanar da taron Jam’iyyar PDP a jihar. Justice E.B. Omotoso ya bayar da umarnin ne a lokacin da yake yanke hukunci kan karar da Afolabi Adedeji ya shigar mai lamba HAD/424M/2025. An shigar da ƙarar ne a kan jam’iyyar PDP, muƙaddashin shugaban jam’iyyar na ƙasa, Umar Damagun; Sakataren jam'iyyar na ƙasa, Umar Bature; Shugaban riƙo na jam'iyyar a jihar Ekiti, Dare Adeleke da kuma hukumar zaɓe mai zaman kanta ta ƙasa INEC. Kotun ta ba da…
Read More
’Yan PDP shida a Majalisar Wakilai daga Delta sun koma APC

’Yan PDP shida a Majalisar Wakilai daga Delta sun koma APC

Daga MAHDI MUSA MUHAMMAD Mambobin Jam’iyyar PDP shida a Majlisar Wakilai daga Jihar Delta sun sauya sheƙa zuwa Jam’iyya APC. Hakazalika, wasu biyu daga Jihar Enugu sun sauya sheƙa daga Jam’iyyar adawa ta LP zuwa PDP. Shugaban Majalisar Wakiliai, Abbas Tajuddeen, ne ya sanar da hakan bayan dawowar majalisar daga hutu a ranar Talata. Shugaban Majalisar ya bayyana cewa ’yan majalisar sun yanke shawarar sauya sheƙar ne sakamakon rikicin cikin gida da ya dabaibaye jam’iyyun nasu a matakin jiha da kuma ƙasa. Waɗanda sauka sauya sheaa zuwa APC su ne: ɓictor Nwokolo, Julius Pondi, Thomas Ereyitomi, Nicholas Mutu, Okodiko Jonathan, da kuma…
Read More
Babu hamayya a siyasar Nijeriya yanzu – Bafarawa

Babu hamayya a siyasar Nijeriya yanzu – Bafarawa

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Tsohon gwamnan jihar Sokoto, Alhaji Attahiru ɗalhatu Bafarawa, ya ce a yanzu babu wata hamayya da ta rage a fagen siyasar Nijeriya. A tattaunawarsa da BBC ya ce 'yan siyasar ƙasar su ne ke hamayya da kansu da cutar juna game da neman muƙamai ba tare da sun anfana wa talakawa wani abu ba. Bafarawa ya bayyana hakan ne ganin yadda wasu jiga-jigan jam'iyyun hamayya na ƙasar ke tururuwa suna komawa jam'iyya mai mulki ta APC a wannan tsakanin yayin da ya rage wajen shekara biyu a yi babban zaɓe na gaba, a 2027.…
Read More
Ba mu damu da manyan ‘yan siyasa a SDP ba, mun fi buƙatar ‘yan dangwale – El-Rufai 

Ba mu damu da manyan ‘yan siyasa a SDP ba, mun fi buƙatar ‘yan dangwale – El-Rufai 

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja  Tsohon gwamnan jihar Kaduna, Nasir El-Rufai ya ce sabuwar jam'iyyar da ya koma, SDP, ta fi buƙatar ta tara mambobi daga tushe ba wai manyan 'yan siyasa ba. El-Rufai, wanda ya fice da ga jam'iyyar APC a watannin baya, ya bayyana hakan ne bayan wani taron masu ruwa da tsaki da ya gudanar a jihar Kano a ranar Litinin. A cewarsa, SDP jam'iyya ce da ke rajin farfaɗo da dimokuraɗiyya tun daga tushe domin gyaran Nijeriya. "Mu ba mu damu da tara manyan 'yan siyasa a SDP ba. Mun fi son mu ga kamar…
Read More