Siyasa

Atiku ya ɗaukaka ƙara kan hukuncin Kotun Sauraren Ƙararrakin Zaɓe

Atiku ya ɗaukaka ƙara kan hukuncin Kotun Sauraren Ƙararrakin Zaɓe

Ɗan takarar shugabancin ƙasa na jam'iyyar PDP a babban zaɓen 2023, Abubakar Atiku, ya garzaya Kotun Ƙoli don kotun ta yi watsi da hukuncin da Kotun Sauraren Ƙararrakin Zaɓen Shugaban Ƙasa ta yanke a ranar 6 ga Satumba. A hukuncin da ta yanke, Kotun Sauraren Ƙararrakin Zaɓen ta ce Bola Ahmed Tinubu shi ne wanda ya lashe zaɓen shugaban ƙasa a babban zaɓen da ya gabata. Sai dai, Atiku ya ce kotun ta tafka kuskure a hukuncin da ta yanke ranar Talata ƙarƙashin jagorancin Mai Shari'a Haruna Simon Tsammani. Ƙarar da Atiku ya ɗaukaka ta hannun babban lauyansa, Chief Chris…
Read More
Shari’ar Gwamnan Kano: Kotu ta ayyana ranar da za ta yanke hukunci

Shari’ar Gwamnan Kano: Kotu ta ayyana ranar da za ta yanke hukunci

Kotun Sauraren Ƙararrakin Zaɓen Gwamnan Kano ta ayyana ranar Laraba ta wannan mako a matsayin ranar da za ta yanke hukunci kan shari'ar da ke gabanta inda Jam'iyyar APC ke ƙalubalantar nasarar da Gwamna Abba Kabir Yusuf na Jam'iyyar NNPP ya samu a zaɓen gwamnan jihar da ya gabata. A ranar Litinin da ta gabata Kotun ta sanar da ranar da za ta yanke hukuncin cikin sanarwar da ta aike wa ɓangarorin da shari'ar ta shafa. Sakataren lauyoyin NNPP, Barrister Bashir T/Wurzici, ya tabbatar wa Jaidar Daily Trust da hakan, yana mai cewa lallai an miƙa wa tawagar lauyoyi takardar…
Read More
Kotu ta tabbatar da nasarar zaɓen Gwamnan Zamfara

Kotu ta tabbatar da nasarar zaɓen Gwamnan Zamfara

Kotun Sauraren Ƙararrakin Zaɓen Jihar Zamfara, ta tabbatar da nasarar da Gwamnan Jihar, Dauda Lawal ya samu a babban zaɓen da ya gabata. Mai magana da yawun Gwamnan, Sulaiman Bala Idris ne ya bayyana haka cikin sanarwar da ya fitar ranar Litinin. Bala Idris ya bayyana hukuncin da kotun ta yanke a matsayin tabbatar da zaɓin al'ummar jihar ta Zamfara. Dauda Lawal ya zama gwamnan Zamfara ne biyo bayan nasarar da ya samu a zaɓen gwamnan jihar da ya gudana a watan Maris da ya gabata, inda ya ɗaɗa gwamana mai ci na wancan lokaci da ƙasa. “Ba da jimawa…
Read More
NNPP ta buƙaci INEC ta dakatar da shirin Kwankwasiyya na yi wa jam’iyyar kwaskwarima

NNPP ta buƙaci INEC ta dakatar da shirin Kwankwasiyya na yi wa jam’iyyar kwaskwarima

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Jam’iyyar NNPP ta rubutawa Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Ƙasa (INEC), inda ta buƙaci hukumar ta dakatar da shirin da wasu ƙungiyoyi ke yi na sauya tambarin jam’iyyar. Jam’iyyar ta kuma rubuta wa Sanata Rabiu Kwankwaso, ɗan takararta na shugaban ƙasa a 2023, domin ya kawo ƙarshen yarjejeniyar da ta shigar da ƙungiyar Kwankwasiyya cikin al'amuran jam'iyyar a zaɓen 2023. Wasiqun da Peter Ogah, lauyan jam’iyyar ne ya rubuta wa INEC da Kwankwaso ya sanya wa hannu kuma aka miƙa wa manema labarai ranar Laraba a Legas. Wasiƙar zuwa ga INEC tana ɗauke da taken:…
Read More
PDP ta zargi gwamnatin Kebbi da almubazzarancin Biliyan N20 cikin kwana 100

PDP ta zargi gwamnatin Kebbi da almubazzarancin Biliyan N20 cikin kwana 100

Daga JAMIL GULMA a Kebbi  Jam'iyyar PDP ta adawa a Jihar Kebbi ta zargi gwamnatin jihar ta Kebbi da almubazzaranci da zunzurutun kuɗi har Naira billiyan ashirin a cikin kwanaki 100 kacal. Alhaji Usman Bello Suru shugaban jam'iyyar PDP ne ya bayyana haka a wata zantawa da manema labarai a garin Birnin Kebbi, yayin da gwamnatin ke gudanar da bikin cika kwanaki 100 da gwamnatin APC ta yi a kan mulki. Ya ce ta yaya gwamanti za ta kashe har Naira billiyan 20 wajen gyaran babban birnin jihar kaɗai ba tare da la'akari da irin yadda yanayin al'umma ya ke…
Read More
Kotu ta ƙwace kujerar ɗan majalisa daga hannun NNPP ta bai wa APC a Kano

Kotu ta ƙwace kujerar ɗan majalisa daga hannun NNPP ta bai wa APC a Kano

Kotun Sauraren Ƙararrakin Zaɓe a Jihar Kano ta tsige Yusuf Umar Datti na Jam'iyyar NNPP a matsayin zaɓaɓɓen ɗan Majalisar Wakilai mai wakiltar Kura/Madobi/Garun Malam a jihar. Bayan tsige Datti daga kujerar ɗan majalisa tmda ta yi, kotun ta ayya abokin hamayyarsa na jam'iyyar APC, Musa Ilyasu Kwankwaso, a matsayin wanda ya lashe zaɓe. Kotun ta yanke wannan hukuncin ne bayan da ta kama Datti da laifin ƙin ajiye aikin gwamnati a tsakanin kwana 30 kafin shiga zaɓe kamara yadda doka ta tanada. Kafin shiga zaɓen, ɗan siyasar ma'aikaci ne a Jami'ar Bayero ta Kano. Kazalika, Alƙali Azingbe ya ce…
Read More
Dangantaka na ƙara tsami tsakanin Gwamna Obaseki da mataimakin sa

Dangantaka na ƙara tsami tsakanin Gwamna Obaseki da mataimakin sa

Ana yunƙurin fitar da ofishin mataimakin daga fadar gwamnati Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Rikicin da ke tsakanin Gwamnan Jihar Edo, Godwin Obaseki da mataimakinsa, Philip Shaibu na ci gaba da ruruwa yayin da ake shirin mayar da mataimakinsa wani gini da ke wajen gidan gwamnati. Ginin da ke lamba 7, Dennis Osadebey Avenue, kusa da gidan gwamnati, wanda shine ofishin hukumar saye da sayarwa ta jihar Edo, an gyara shi domin ya zama ofishin mataimakin. Tsohon gwamnan jihar, Adams Oshiomhole ne ya qaddamar da ginin a ranar 16 ga watan Disamba, 2014. Sai dai kuma da aka tuntuɓi…
Read More
Kotu ta kori ƙarar su Atiku kan Tinubu

Kotu ta kori ƙarar su Atiku kan Tinubu

Kotun Sauraren Ƙararrakin Zaɓe mai zamanta a Abuja ta kori ƙarar da Jam'iyyar PDP da ɗan takararta na shugabancin ƙasa, Atiku Abubakar suka shigar inda suke ƙalubalantar nasarar da Shugaba Bola Tinubu ya samu a babban zaɓen da ya gabata. Kotu ta yi watsi da ƙarar ne a zaman shari'a da ta yi ranar Laraba. Yayin zamanta, kotun ta soke wasu sakin layi a ƙorafin da aka shigar da suke nuni da Shugaba Bola Tinubu bai cancanci shiga zaɓen da ya gudana ranar 25 ga Fabrairun da ya gabata ba. Ta ce masu ƙarar sun gagara gabatar wa kotun cancantar…
Read More
Shari’ar zaɓen shugaban ƙasa: Jam’iyyar Labour ta yi watsi da hukuncin kotu

Shari’ar zaɓen shugaban ƙasa: Jam’iyyar Labour ta yi watsi da hukuncin kotu

Jam'iyyar Labour Party ta yi watsi da hukuncin da Kotun Sauraren Ƙararrakin Zaɓen Shugaban Ƙasa kan ƙarar da ta shigar tana ƙalubalantar nasarar da Shugaba Tinubu ya samu a babban zaɓen da ya gabata a watan Fabrairu, 2023. Cikin sanarwar da ta fitar bayan hukuncin da kotun ta yanke a ranar Laraba, Sakataren jam'iyyar na ƙasa, Obiora Ifoh, ya ce ba a yi wa LP adalci ba kan ƙarar da ta shigar kan jam'iyyar APC da Tinubu. Ya ce jam'iyyar tasu za ta ɗauki mataki na gaba bayan tuntuɓar lauyoyinta bayan kuma ta amshi takardar shaidar hukuncin da kotun ta…
Read More