20
Sep
Ɗan takarar shugabancin ƙasa na jam'iyyar PDP a babban zaɓen 2023, Abubakar Atiku, ya garzaya Kotun Ƙoli don kotun ta yi watsi da hukuncin da Kotun Sauraren Ƙararrakin Zaɓen Shugaban Ƙasa ta yanke a ranar 6 ga Satumba. A hukuncin da ta yanke, Kotun Sauraren Ƙararrakin Zaɓen ta ce Bola Ahmed Tinubu shi ne wanda ya lashe zaɓen shugaban ƙasa a babban zaɓen da ya gabata. Sai dai, Atiku ya ce kotun ta tafka kuskure a hukuncin da ta yanke ranar Talata ƙarƙashin jagorancin Mai Shari'a Haruna Simon Tsammani. Ƙarar da Atiku ya ɗaukaka ta hannun babban lauyansa, Chief Chris…