15
Sep
Daga JAMIL GULMA a Kebbi Jam'iyyar PDP ta adawa a Jihar Kebbi ta zargi gwamnatin jihar ta Kebbi da almubazzaranci da zunzurutun kuɗi har Naira billiyan ashirin a cikin kwanaki 100 kacal. Alhaji Usman Bello Suru shugaban jam'iyyar PDP ne ya bayyana haka a wata zantawa da manema labarai a garin Birnin Kebbi, yayin da gwamnatin ke gudanar da bikin cika kwanaki 100 da gwamnatin APC ta yi a kan mulki. Ya ce ta yaya gwamanti za ta kashe har Naira billiyan 20 wajen gyaran babban birnin jihar kaɗai ba tare da la'akari da irin yadda yanayin al'umma ya ke…