Siyasa

PDP ta zargi gwamnatin Kebbi da almubazzarancin Biliyan N20 cikin kwana 100

PDP ta zargi gwamnatin Kebbi da almubazzarancin Biliyan N20 cikin kwana 100

Daga JAMIL GULMA a Kebbi  Jam'iyyar PDP ta adawa a Jihar Kebbi ta zargi gwamnatin jihar ta Kebbi da almubazzaranci da zunzurutun kuɗi har Naira billiyan ashirin a cikin kwanaki 100 kacal. Alhaji Usman Bello Suru shugaban jam'iyyar PDP ne ya bayyana haka a wata zantawa da manema labarai a garin Birnin Kebbi, yayin da gwamnatin ke gudanar da bikin cika kwanaki 100 da gwamnatin APC ta yi a kan mulki. Ya ce ta yaya gwamanti za ta kashe har Naira billiyan 20 wajen gyaran babban birnin jihar kaɗai ba tare da la'akari da irin yadda yanayin al'umma ya ke…
Read More
Kotu ta ƙwace kujerar ɗan majalisa daga hannun NNPP ta bai wa APC a Kano

Kotu ta ƙwace kujerar ɗan majalisa daga hannun NNPP ta bai wa APC a Kano

Kotun Sauraren Ƙararrakin Zaɓe a Jihar Kano ta tsige Yusuf Umar Datti na Jam'iyyar NNPP a matsayin zaɓaɓɓen ɗan Majalisar Wakilai mai wakiltar Kura/Madobi/Garun Malam a jihar. Bayan tsige Datti daga kujerar ɗan majalisa tmda ta yi, kotun ta ayya abokin hamayyarsa na jam'iyyar APC, Musa Ilyasu Kwankwaso, a matsayin wanda ya lashe zaɓe. Kotun ta yanke wannan hukuncin ne bayan da ta kama Datti da laifin ƙin ajiye aikin gwamnati a tsakanin kwana 30 kafin shiga zaɓe kamara yadda doka ta tanada. Kafin shiga zaɓen, ɗan siyasar ma'aikaci ne a Jami'ar Bayero ta Kano. Kazalika, Alƙali Azingbe ya ce…
Read More
Dangantaka na ƙara tsami tsakanin Gwamna Obaseki da mataimakin sa

Dangantaka na ƙara tsami tsakanin Gwamna Obaseki da mataimakin sa

Ana yunƙurin fitar da ofishin mataimakin daga fadar gwamnati Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Rikicin da ke tsakanin Gwamnan Jihar Edo, Godwin Obaseki da mataimakinsa, Philip Shaibu na ci gaba da ruruwa yayin da ake shirin mayar da mataimakinsa wani gini da ke wajen gidan gwamnati. Ginin da ke lamba 7, Dennis Osadebey Avenue, kusa da gidan gwamnati, wanda shine ofishin hukumar saye da sayarwa ta jihar Edo, an gyara shi domin ya zama ofishin mataimakin. Tsohon gwamnan jihar, Adams Oshiomhole ne ya qaddamar da ginin a ranar 16 ga watan Disamba, 2014. Sai dai kuma da aka tuntuɓi…
Read More
Kotu ta kori ƙarar su Atiku kan Tinubu

Kotu ta kori ƙarar su Atiku kan Tinubu

Kotun Sauraren Ƙararrakin Zaɓe mai zamanta a Abuja ta kori ƙarar da Jam'iyyar PDP da ɗan takararta na shugabancin ƙasa, Atiku Abubakar suka shigar inda suke ƙalubalantar nasarar da Shugaba Bola Tinubu ya samu a babban zaɓen da ya gabata. Kotu ta yi watsi da ƙarar ne a zaman shari'a da ta yi ranar Laraba. Yayin zamanta, kotun ta soke wasu sakin layi a ƙorafin da aka shigar da suke nuni da Shugaba Bola Tinubu bai cancanci shiga zaɓen da ya gudana ranar 25 ga Fabrairun da ya gabata ba. Ta ce masu ƙarar sun gagara gabatar wa kotun cancantar…
Read More
Shari’ar zaɓen shugaban ƙasa: Jam’iyyar Labour ta yi watsi da hukuncin kotu

Shari’ar zaɓen shugaban ƙasa: Jam’iyyar Labour ta yi watsi da hukuncin kotu

Jam'iyyar Labour Party ta yi watsi da hukuncin da Kotun Sauraren Ƙararrakin Zaɓen Shugaban Ƙasa kan ƙarar da ta shigar tana ƙalubalantar nasarar da Shugaba Tinubu ya samu a babban zaɓen da ya gabata a watan Fabrairu, 2023. Cikin sanarwar da ta fitar bayan hukuncin da kotun ta yanke a ranar Laraba, Sakataren jam'iyyar na ƙasa, Obiora Ifoh, ya ce ba a yi wa LP adalci ba kan ƙarar da ta shigar kan jam'iyyar APC da Tinubu. Ya ce jam'iyyar tasu za ta ɗauki mataki na gaba bayan tuntuɓar lauyoyinta bayan kuma ta amshi takardar shaidar hukuncin da kotun ta…
Read More
APC ta musanta saka sunan Wike a kwamitin yaƙin neman zaɓen Gwamnan Bayelsa

APC ta musanta saka sunan Wike a kwamitin yaƙin neman zaɓen Gwamnan Bayelsa

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Jam’iyyar All Progressives Congress (APC), ta yi kira ga jama’a da su yi watsi da jerin sunayen yaqin neman zaɓen da za a gudanar a ranar 11 ga watan Nuwamba a jihohin Imo, Kogi, da Bayelsa. A wani saƙo da ya wallafa a dandalin X (wanda aka fi sani da Tiwita) a ranar Talata, Muhammad Argungu, sakataren tsare-tsare na jam’iyyar APC, ya ce Abdullahi Ganduje, shugaban jam’iyyar na ƙasa, ya amince da kundin tsarin mulkin kwamitin yaqin neman zave tare da tuntuvar Kwamitin Ayyuka na Ƙasa (NWC). A cikin jerin sunayen da aka soke…
Read More
APC a Zamfara ta nesanta kanta da zargin yunƙurin hamɓarar da Gwamna Dauda

APC a Zamfara ta nesanta kanta da zargin yunƙurin hamɓarar da Gwamna Dauda

Daga SANUSI MUHAMMAD a Gusau Jam’iyyar All Progressives Congress APC a Zamfara ta nesanta kanta daga zargin kitsa yunƙurin hamɓarar da Gwamna Dauda Lawal kamar yadda jam’iyyar PDP mai mulki a jihar ta yi zargi. Sakataren Yaɗa Labarai na Jam’iyyar APC na jihar, Yusuf Idris ne ya bayyana hakan yayin da yake mayar da martani kan zargin da jam’iyyar PDP ta yi wa APC a wata sanarwa da ya fitar ga manema labarai a Gusau. A cewar sanarwar, zargin da jam'iyyar PDP ta yi wani shiri ne da jam’iyyar ta PDP ke yi ta hanyar amfani da tsohon aminin Gwamna…
Read More
NNPP ta dakatar da Kwankwaso bisa zargin yi wa jam’iyya zagon-ƙasa

NNPP ta dakatar da Kwankwaso bisa zargin yi wa jam’iyya zagon-ƙasa

Kwamitin Amintattu (BoT) na Jam'iyyar NNPP ya dakatar da ɗan takarar shugabancin ƙasa na jam'iyyar a babban zaɓen da ya gabata, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso, bisa zargin yi wa jam'iyyar zagon-ƙasa. Kazalika, Kwamitin (BoT) ya dakatar da Kwamitin Gudanarwa na Ƙasa (NWC) na jam'iyyar. Har wa yau, Kwamitin ya naɗa shugabannin jam'iyyar a matakin ƙasa ƙarƙashin jagorancin Dr Agbo Major a matsayin shugaban riƙo na ƙasa da kuma Mr Ogini Olaposi a matsayin muƙaddashin Sakatsren jam'iyya na ƙasa tare da wasu mutum 18. Jaridar News Point Nigeria ta kalato cewar, dakatarwar ta wata shida ne. Majiyarmu ta ce an cim…
Read More
Rundunar ‘yan sanda ta haramta zanga-zanga a Kano gabanin yanke hukuncin zaɓen gwamna

Rundunar ‘yan sanda ta haramta zanga-zanga a Kano gabanin yanke hukuncin zaɓen gwamna

Rundunar 'Yan Sandan Nijeriya reshen Jihar Kano ta haramta kowane irin nau'i na zanga-zanga a faɗin jihar. Da yake sanar da wannan doka a jihar a ranar Litinin, Kwamishinan 'Yan Sandan Jihar Kano, Husaini Gumel, ya ce dokar ta fara aiki nan take. A cewar Kwamishinan, bayanan sirri sun nuna jam'iyyun NNPP da APC a jihar na shirin gudanar da zanga-zanga dangane da zaman kotun sauraron ƙararrakin zaɓe a jihar. Idan ba a manta ba, Jam'iyyar APC a Kano ta shigar da ƙara kotu inda take ƙalubalantar bayyana NNPP da hukumar zaɓe INEC ta yi a matsayin wadda ta lashe…
Read More