Siyasa

Ƙungiyar matasan APC ta yi raddi kan zarge-zargen da Hon. Jaji ya yiwa Matawalle

Ƙungiyar matasan APC ta yi raddi kan zarge-zargen da Hon. Jaji ya yiwa Matawalle

Daga SANUSI MUHAMMAD a Gusau Ƙungiyar jajirtattun matasan jam'iyyar APC ta ƙasa, National Youths ɓanguard of APC ta sa ƙafa ta shure ɗaukacin zarge-zargen da Hon. Aminu Sani Jaji ya yi wa Ministan ƙasa a ma'aikatar tsaron Nijeriya, Dr Bello Muhammed Matawalle, cewa yana kitsa zarge-zargen ayyukan cin amanar jam’iyya a kansa. A cikin wata sanarwa da ta fitar, Sakataren yaɗa labaran ƙungiyar na ƙasa Dr Adeniyi Wale, ya bayyana zarge-zargen Hon. Jaji a matsayin “maras tushe,” yana mai cewa hakan wata hanya ce ta karkatar da hankalin jama’a daga abubuwan da yake kullawa a siyasa. “Jaji ya jima yana…
Read More
Kotun zaɓen Edo ta kori ƙarar da aka shigar kan Okpebolo da APC

Kotun zaɓen Edo ta kori ƙarar da aka shigar kan Okpebolo da APC

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Kotun sauraron ƙararrakin zaben gwamnan jihar Edo da ke zamanta a Abuja, ta yi watsi da ƙarar da Jam'iyyar Action Alliance (AA) da wani Adekunle Omoaje suka shigar a kan Gwamna Monday Okpebholo da jam’iyyar All Progressiɓes Congress (APC), saboda rashin cancanta da kuma rashin cancanta. Kotun ta ce Adekunle Omoaje, wanda ya shigar da ƙara na haɗin guiwa, ba shi da hurumin yin shari’ar. Daga cikin sauran, kotun ta ce Omoaje bai shiga zaɓen gwamna ba, don haka ba shi da hurumin kokwanto kan sahihancin zaɓen. Kotun ta kuma ce abin da Omoaje…
Read More
Gwamnan Edo: PDP ta yi watsi da hukuncin kotun zaɓe, ta ɗaukaka ƙara

Gwamnan Edo: PDP ta yi watsi da hukuncin kotun zaɓe, ta ɗaukaka ƙara

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Jam’iyyar PDP a Jihar Edo ta yi watsi da hukuncin da kotun sauraron ƙararrakin zaɓe ta yanke. Kotun sauraron kararrakin zaben Edo da ke zamanta a Abuja ranar Laraba, ta amince da zaben Gwamna Okpebolo tare da yin watsi da karar da PDP da Asue Ighodalo suka shigar. A wata sanarwa a Benin, Dr Tony Aziegbemi, shugaban kwamitin riƙo na jam’iyyar PDP, ya ce mafi yawan masu kaɗa ƙuri’a ne suka zaɓi ɗan takararsu a zaɓen gwamna da aka yi a ranar 21 ga Satumba, 2024. Mista Aziegbemi ya ce PDP na da tabbacin…
Read More
Akwai alamun PDP a Katsina tsagin Mustapha Inuwa na shirin ficewa daga jam’iyyar

Akwai alamun PDP a Katsina tsagin Mustapha Inuwa na shirin ficewa daga jam’iyyar

Alamu na nuna cewa ƴaƴan jam'iyyar PDP tsagin Mustapha Inuwa na shirin ficewa daga jam'iyyar nan bada jimawa ba. A wani taron gaggawa da suka yi a Katsina ƙarƙashin jagorancin tsohon sakataren gwamnatin Katsina Mustapha Inuwa ya faɗa wa taron cewa nan bada dadewa zasu san matsayin su a jam'iyyar. "Muna ta tuntuɓar mutanen mu da wasu ya'yan wasu jam'iyu a jihar da ƙasa baki ɗaya ƙarƙashin tsohon mataimakin shugaban ƙasa Atiku Abubakar madugu a tafiyar kafin mu fidda matsaya"inji Mustapha Inuwa. PDP a Katsina ta rabu gida biyu ne, akwai ɓangaren sanata Yakubu Lado Ɗanmarke da ɓangaren Mustapha Inuwa,sai…
Read More
Ba za mu yi haɗaka da kowa ba – SDP

Ba za mu yi haɗaka da kowa ba – SDP

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Jam'iyyar SDP a Nijeriya ta yi watsi da yunƙurin haɗaka tsakaninta da sauran jam'iyyun adawa da nufin tunkarar zaɓen 2027. Wannan na zuwa yayin da ake ganin tagomashin jam'iyyar ta SDP ya ƙaru sakamakon sauya sheƙar da wasu manya 'yan siyasa a ƙasar ke yi zuwa cikinta. A makon da ya gabata ne wasu jagororin adawa ƙarƙashin jagorancin tsohon mataimakin shugaban ƙasa Alhaji Atiku Abubakar na babbar jam'iyyar hamayya ta PDP suka sanar da cewa suna wani yunƙuri na ƙulla haɗaka domin kawar da APC a zaɓen 2027. Sai dai shugaban jam'iyyar na ƙasa…
Read More
Zamfara: Ƙungiyar Marafa ta nemi ɗanfulani ya yi murabus daga shugabancin APC

Zamfara: Ƙungiyar Marafa ta nemi ɗanfulani ya yi murabus daga shugabancin APC

Daga SANUSI MUHAMMAD a Gusau Alhaji Surajo Garba Maikatako, Shugaban ƙungiyar goyon bayan Jam'iyyar APC ɓangaren Sanata Kabiru Garba Marafa a Jihar Zamfara ya yi kira ga shugaban jam’iyyar APC na jihar, Hon Tukur ɗanfulani da ya yi murabus daga muƙaminsa domin samun zaman lafiya da cigaban jam’iyyar APC a jihar. Surajo Maikatako ya yi wannan kiran ne a wata sanarwa da ya raba wa manema labarai a Gusau ranar Alhamis.  Maikatako ya ƙalubalanci Hon ɗanfulani da mayar da Sanata Marafa saniyar ware tare da nuna wariya ga Sanata Marafa da magoya bayansa a jihar. A cewarsa, za a iya…
Read More
Zamfara: Sanata Marafa ya musanta sauya sheƙa zuwa SDP daga APC

Zamfara: Sanata Marafa ya musanta sauya sheƙa zuwa SDP daga APC

Daga SANUSI MUHAMMAD a Gusau Tsohon sanata mai wakiltar Zamfara ta tsakiya a Majalisar Dattawa ta ƙasa, Sanata Kabiru Garba Marafa ya ƙaryata raɗe-raɗin da ake yaɗawa na cewa yana shirin ficewa daga jam'iyyar sa ta APC ya koma Social Democratic Party SDP. Shugaban kwamitin amintattu na jam'iyyar APC ta ɓangaren Sanata Kabiru Garba Marafa a Jihar Zamfara, Alh. Surajo Maikatako ya bayyana haka a lokacin da yake amsa tambayoyi daga manema labarai a Gusau yau Laraba. Maikatako ya bayyana jita-jitar da akewa Sanata Kabiru Garba Marafa na shirin sauya sheka zuwa SDP a matsayin sharri, mara tushe kuma mara…
Read More
Ni gwamnan Kano nake son zama ba shugaban jam’iyyar APC ba – Abbas

Ni gwamnan Kano nake son zama ba shugaban jam’iyyar APC ba – Abbas

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Shugaban Jam'iyyar APC na jihar Kano Abdullahi Abbas ya ce shi burinsa ya zama gwamnan Kano ba sake zama shugaban jam'iyyar APC ba a jihar ta Kano. Abdullahi Abbas ya shaida wa BBC hakan ne yayin mayar da martani ga ministan ma'aikatar gidaje na Nijeriya, Yusuf Abdullahi Ata kan kalamansa na baya-bayan nan inda ya yi barazanar ficewa daga jam'iyyar. Ministan ya yi barazanar ficewa daga jam'iyyar APC muddun aka sake zaɓen shugaban jam'iyyar na Kano, Abdullahi Abbas a matsayin shugaban jam'iyyar na jihar a karo na huɗu. A yanzu haka zafafan kalaman ministan…
Read More
An rantsar da Aiyedatiwa a matsayin gwamnan Ondo

An rantsar da Aiyedatiwa a matsayin gwamnan Ondo

A ranar Litinin, Lucky Aiyedatiwa ya karɓi rantsuwar kama aiki a matsayin gwamnan Jihar Ondo na bakwai, a wani biki da aka gudanar a filin wasan Ondo da ke Akure, babban birnin jihar. Aiyedatiwa, wanda ya lashe zaɓen gwamna da jam’iyyar APC ta tsayar a watan Disamba 2024, ya yi rantsuwar ofis ne bayan mataimakinsa, Olayide Adelami. Manyan mutane daga faɗin ƙasar, ciki har da Shugaban APC na ƙasa, Abdullahi Ganduje, da gwamnonin jihohi irin su Babajide Sanwo-Olu na Legas da Biodun Oyebanji na Ekiti, sun halarci bikin. Aiyedatiwa ya samu nasara ne bayan kayar da abokin hamayyarsa, Agboola Ajayi,…
Read More
Malaman addini sun yi wa ’yan siyasa juyin mulki — Sule Lamiɗo

Malaman addini sun yi wa ’yan siyasa juyin mulki — Sule Lamiɗo

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Tsohon Gwamnan Jihar Jigawa Sule Lamiɗo, ya zargi malaman addini da neman ƙwace lamurran siyasar Nijeriya daga hannun ’yan siyasa. Sule Lamiɗo ya nuna damuwa bisa yadda malaman addini ke ƙara shiga harkokin siyasa, inda ya ce, a halin yanzu malaman suna yin tasiri sosai a yanayin tafiyar siyasa da kuma jefa ƙuri’a. Ya bayyana haka ne a yayin da ya kai ziyarar ta’aziyya ga fitaccen malamin Musulunci, Sheikh Yusuf Sambo Rigachikum, bisa rasuwar babban ɗansa a Jihar Kaduna. A cikin bidiyon ta’aziyyar, an ji Sule Lamiɗo, yana cewa, malaman addini sun yi wa…
Read More