Siyasa

Da Ɗumi-ɗumi: APC ta zaɓi Ganduje a matsayin shugaban jam’iyya na ƙasa

Da Ɗumi-ɗumi: APC ta zaɓi Ganduje a matsayin shugaban jam’iyya na ƙasa

Daga BASHIR ISAH Kwamitin Shugabanni na Ƙasa (NEC) na Jam'iyyar APC, ta zaɓi tsohon Gwamnan Kano, Abdullahi Ganduje, a matsayin sabon shugaban jam'iyyar na ƙasa. Kazalika, jam'iyyar ta zaɓi tsohon mai magana davyawun Shugaban Majalisar Dattawa, Ajibola Basiru, a matsayin sakatarenta na ƙasa. Kwamitin (NEC) ya yi wannan zaɓen ne yayin zamansa karo na 12 da ya gudanar ranar Alhamis Transcorp Hilton da ke Abuja. Mahalarta taron sun haɗa da Shugaban Ƙasa Bola Tinubu, Mataimakin Shugaban Ƙasa Kashim Shettima, gwamnonin APC da sauransu. Sai dai, tsohon Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari da tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa Yemi Osinbajo na daga cikin…
Read More
Shugabancin APC: NPCF ta yi na’am da naɗin Ganduje

Shugabancin APC: NPCF ta yi na’am da naɗin Ganduje

Daga BASHIR ISAH Kwamitin gudanarwa na ƙasa na ƙungiyar kansilolin jam'iyyar APC (NPCF) ya amince da naɗin tsohon Gwamnan Jihar Kano, Dokta Abdullahi Umar Ganduje, a matsayin sabon Shugaban Jam'iyyar APC na ƙasa. Ƙungiyar ƙarƙashin jagorancin Hon Muslihu Yusuf Ali, ta bayyana haka ne cikin sanarwar manema labarai da ta fitar mai ɗauke da sa hannnun Sakataren Ƙungiyar na Ƙasa, Hon Abayomi A. Kazeem da kwanan wata 29 ga Yuli, 2023. A cewar ƙungiyar, bai wa Ganduje shugabancin jam'iyyar ya yi daidai kasancewar gogaggen ɗan siyasa, ƙwararre wanda ya samar da ɗimbin cigaba a Jihar Kano a zamanin gwamnatinsa. Daga…
Read More
Sanatan Kano ta Tsakiya: Kotu ta tabbatar da nasarar Hanga

Sanatan Kano ta Tsakiya: Kotu ta tabbatar da nasarar Hanga

Daga BASHIR ISAH Kotun sauraren ƙararrakin zaɓe mai zamanta a Kano, ta tabbatar da sanar da Sanata Rufa’i Hanga ya samu a zaɓen da ya gabata a matsayin mai wakiltar Kano ta Tsakiya a Majalisar Dattawa. Majiyarmu ta ruwaito cewa ɗan takarar Jam'iyyar APC na sanatan Kano ta Tsakiya a zaɓen da aka gudanar 25 ga Fabrairun da ya gabata, Abdulsalam Abdulkarim Zaura, shi ne ya shigar da ƙara kotu inda ya ƙalubalanci ayyana ɗan takarar jam'iyyar NNPP, Rufa'i Hanga, da hukumar zaɓe INEC ta yi a matsayin wanda ya lashe zaɓen. Zaura, ta hannun lauyansa, Ishaka Dikko (SAN), ya…
Read More
An samu game da shugabancin Majalisar Nasarawa

An samu game da shugabancin Majalisar Nasarawa

Daga BASHIR ISAH 'Yan Majalisar Dokokin Jihar Nasarawa sun zaɓi Rt. Hon Ibrahim Balarabe Abdullahi (APC- Umaisha/Ugya) a matsayin Shugaban Majalisar jihar ta bakwai. Kazalika, 'yan majalisar sun sun zaɓi Hon Abel Yakubu Bala (PDP- Nassarawa Eggon ta Yamma) a matsayin Mataimakin Shugaban Majalisar. Muƙaddashin akawun majalisar, Hon Ibrahim Musa, shi ne ya sanar da hakan yayin rantsar da mambobin majalisar ta bakwai a Lafia, babban birnin jihar. Akawun majalisar ya ce an rantsar da mambobin majalisar ne daidai da damar da Gwamnan Abdullahi Sule na jihar ya bayar wanda ya yi daidai da kundin tsarin mulkin ƙasa.
Read More
Yan Nijeriya za zu yi murna idan aka rushe zaɓen Tinubu – PDP

Yan Nijeriya za zu yi murna idan aka rushe zaɓen Tinubu – PDP

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Jam'iyyar PDP ta ce 'yan Nijeriya za su fito kan tituna suna murna idan har aka soke ayyana Bola Tinubu a matsayin Shugaban Ƙasa. Sai dai a martanin da ta mayar cikin gaggawa, jam’iyyar mai mulkin ƙasar ta ce PDP na rugujewa ne kawai, inda ta dage cewa Shugaba Tinubu na da hurumin ‘yan Nijeriya kuma zai yi aiki a kan haka kamar yadda kundin tsarin mulkin ƙasar ya tanada. Pedro Obaseki, Daraktan Dabaru da Bincike na Kwamitin Yaƙin Neman Zaɓen Shugaban Ƙasa na PDP (PCC) wanda ya yi wa manema labarai jawabi gabanin…
Read More
An tashi baram-baram a zaman sulhu kan rigimar kujerar Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Nasarawa

An tashi baram-baram a zaman sulhu kan rigimar kujerar Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Nasarawa

Daga JOHN D. WADA a Lafiya Idan ba a manta ba jaridar Blueprint Manhaja a kwanan nan ne ta kawo muku labarin rigimar da ta ɓarke akan zaɓen sabon shugabancin majalisar dokokin jihar ta Nasarawa karo na 7, inda a ƙarshe aka samu ɓangarori 2 wato ɓangaren Honorabul Oga Ogazi da na shugaban majalisar dokokin dake neman zarcewa wato Honorabul Balarabe Ibrahim Abdullahi. Kasancewa rigimar ya ƙi ci ya kuma qi cinyewa ne sai wasu masu ruwa da tsakin jihar dake faɗa aji da sarakunan gargajiyan jihar da sauran su ciki har da gwamnan jihar Injiniya Abdullahi Sule suka ɗauki…
Read More
Shugabancin APC: Kyari ya maye gurbin Adamu

Shugabancin APC: Kyari ya maye gurbin Adamu

Daga BASHIR ISAH Mataimakin Shuagaban Jam'iyyar APC na ƙasa da daga shiyyar Arewa, Abubakar Kyari, ya maye gurbin Sanata Abdullahi Adamu a matsayin sabon shugaban jam'iyyar na ƙasa biyo bayan murabus da Adamu ɗin ya yi. Wannan sauyin da jam'iyyar ta APC ta samu ya yi daidai da tanadin kundin dokokin jam'iyyar, wanda ya nuna cewa idan shugaban jam'iyyar na ƙasa ya yi murabus mataimakinsa ya maye gurbinsa a matsayin riƙon ƙwarya. An ga Kyari ya jagoranci mambobin Kwamitin Gudanarwa na Ƙasa (NWC) na jam'iyyar wajen yin taro a sakatariyar jam'iyyar da ke Abuja cikin tsattsauran tsaro a ranar Litinin.…
Read More
Adamu ya yi murabus daga shugabancin Jam’iyyar APC

Adamu ya yi murabus daga shugabancin Jam’iyyar APC

Daga BASHIR ISAH Sbugaban Jam'iyyar APC na Ƙasa, Sanata Abdullahi Adamu, ya miƙa wasiƙar yin murabus daga kujerarsa ta shugabancin jam'iyyar kamar yadda Jaridar News Point Nigeria ta rawaito. Majiyar News Point Nigeria ta bayya cewar, Sanata Adamu wanda ya zama shugaban APC a watan Maris, 2022, ya miƙa wasiƙar murabus daga muƙaminsa ga Fadar Shugaban Ƙasa gabanin dawowar Shugaba Bola Ahmed Tinubu daga taron Ƙungiyar Ƙasashen Afirka (AU) da ya halarta a ƙasar Kenya. Majiyar jaridar ta ce, Adamu ya aike da wasiƙar tasa ce ga Shugaban Ma'aikatan Fadar Shugaban Ƙasa, Femi Gbajabiamila, da misalin ƙarfe 4 na yammacin…
Read More
Ɗan takarar Gwamna ya je Kotun Sauraron Ƙararrakin Zaɓe da shaidu 8,000

Ɗan takarar Gwamna ya je Kotun Sauraron Ƙararrakin Zaɓe da shaidu 8,000

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Mutumin da ya yi wa Jam’iyyar PDP takara a zaɓen Gwamnan Jihar Ogun na 2023, Ladi Adebutu, a ranar Talata ya isa kotun sauraron kararrakin zaɓen jihar da shaidu har guda 8,000. Ɗan takarar dai na ƙalubalantar nasarar da Dapo Abiodun ya samu a zaɓen Gwamnan Jihar da aka gudanar ranar 18 ga watan Maris ɗin da ya gabata. A kwafin ƙarar tasa mai lamba EPT/OG/GOV/03/2023, ɗan takarar ya ce ya shigar da ƙarar ce saboda yana zargin ba a bi Dokar Zaɓe ta Nijeriya ba a yayin zaɓen. Alqalai uku ne dai suke…
Read More
APC ta nesanta kanta da batun manyan muƙaman da aka naɗa a Majalisar Tarayya

APC ta nesanta kanta da batun manyan muƙaman da aka naɗa a Majalisar Tarayya

Daga BASHIR ISAH Shugaban Jam'iyyar APC na Ƙasa, Sanata Abdullahi Adamu, ya nesanta jam'iyyar da batun manyan muƙaman da aka naɗa a Majalisar Tarayya kamar yadda shugabancin majalisar dattawa da ta wakilai suka sanar a ranar Talata. Yayin taro da Kwamitin Gudanawar na Ƙasa na jam'iyyar da ƙungiyar gwamnonin APC a Abuja, Adamu ya ce Majalisar Tarayya ta saɓa ƙa'ida wajen sanar da manyan jami'an da aka naɗa ba tare da sanin jam'iyyar ba kamar yadda tashar AIT ta rawaito. A zaman da majalisun suka yi a ranar Talata aka jiyo Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Godswill Akpabio da Shugaban Majalisar…
Read More