Siyasa

Yadda zazzafar taƙaddama ta kaure tsakanin El-Rufai da Uba Sani

Yadda zazzafar taƙaddama ta kaure tsakanin El-Rufai da Uba Sani

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Rashin jituwa da ake zargi tsakanin tsohon gwamnan jihar Kaduna, Nasir El-Rufa'i da gwamna mai ci a Kaduna, Sanata Uba Sani ya fito fili, bayan tsohon gwamna ya yi kakausan martani kan kalaman gwamna mai ci. Wannan sabuwar taƙaddama da ta kunno kai na da nasaba da kalaman da gwamna Uba Sani ya furta a lokacin wata hira da kafar talabijin ta TɓC a Nijeriya, wadda ba ta yi wa tsohon gwamna El-Rufa'i daɗi ba. Mutanen biyu waɗanda a baya aminan juna ne a fagen siyasa, abubuwa sun sauya tun bayan sauyin gwamnati da…
Read More
Kotu ta ɗaure Farfesa shekara uku kan aikata maguɗin zaɓe

Kotu ta ɗaure Farfesa shekara uku kan aikata maguɗin zaɓe

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Wata Babbar Kotu a Jihar Akwa Ibom, ta yanke wa Farfesa Ignatius Uduk hukuncin ɗaurin shekaru uku a gidan yari kan laifin sauya sakamakon zaɓe. An gurfanar da Farfesan kan tuhume-tuhume uku da suka haɗa da gazawa wajen aiwatar da aikinsa, sauya sakamakon zaɓe, da kuma yin rantsuwar ƙarya a gaban kotun sauraron ƙorafe-ƙorafen zaɓe. Lamarin ya shafi zaɓen ‘yan majalisar jiha da aka gudanar a Essien Udim a shekarar 2019. A ranar Laraba ne, Mai shari’a Bassey Nkanang ya same shi da laifin sauya sakamakon zaɓe da yin rantsuwa bisa ƙarya. Hakan ya…
Read More
Masari ya buƙaci ‘yan Nijeriya su ƙara haƙuri da gwamnatin APC

Masari ya buƙaci ‘yan Nijeriya su ƙara haƙuri da gwamnatin APC

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Tsohon Gwamnan Jihar Katsina, Alhaji Aminu Masari, ya buƙaci ‘yan Nijeriya su nuna ƙarin haƙuri da gwamnatin Jam'iyyar All Progressiɓes Congress (APC), yana mai cewa matsalolin tattalin arzikin da ake fuskanta na daga cikin al'amuran duniya ne kuma ba na musamman a Nijeriya ba. Masari ya bayyana wannan jawabi ne a ranar Lahadi a ƙafur, ƙaramar Hukumar ƙafur, a lokacin ƙaddamar da yaƙin neman zaɓen ƙananan hukumomi da za a gudanar ranar 15 ga Fabrairu. Ya yi magana ne game da rahotanni da suka bayyana a shafukan sada zumunta cewa wasu 'yan siyasa suna…
Read More
Ba za mu yi wani juyayin ba kan sauya sheƙar Aregbesola da magoya bayansa a Osun – APC 

Ba za mu yi wani juyayin ba kan sauya sheƙar Aregbesola da magoya bayansa a Osun – APC 

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Jam’iyyar All Progressives Congress (APC) reshen jihar Osun ta ce ba za ta yi kewa da juyayin ficewar Omoluabi Rauf Aregbesola daga jam'iyyar All Progressiɓes Congress APC. Kungiyar ta sanar da sauya sheƙar ta ne a ranar Lahadi a yayin wani taron masu ruwa da tsaki a garin Ilesa na jihar Osun. Taron ya samu halartar Aregbesola da sauran ‘ya’yan jam’iyyar APC na gundumomi 332 na Osun. An ƙaddamar da ƙungiyar siyasa a watan Agusta 2023. Aregbesola ya yi gwamnan Osun daga 2010 zuwa 2018, da kuma ministan harkokin cikin gida daga 2019 zuwa…
Read More
Yadda rikicin shugabancin Jam’iyyar NNPP a Kano ya ɗauki zafi

Yadda rikicin shugabancin Jam’iyyar NNPP a Kano ya ɗauki zafi

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Wata sabuwar dambarwa da zaman rashin tabbas na ci gaba da addabar jam'iyyar adawa ta NNPP da ke mulki a jihar Kano, kan shugabancin jam'iyyar. Wannan dambarwa ta ja-ni-in-ja-ka game da halastaccen shugabancin jam'yyar a tsakanin masu biyayya ga Kwankwaso da waɗanda suka raba tafiya da shi. ɓangarori biyu ne ke jayayya kan shugabancin jam'iyyar ta NNPP; a tsakanin masu alamar kwando da kayan marmari da masu alamar littafi da hula da alƙalami. Shugabancin Sanata Mas'ud El-Jibrin Doguwa da Hashim Sulaiman Dogurawa ne ke ta kokawar ganin cewar kowannensu shi ne zai ja ragamar…
Read More
Ko Peter Obi na son yi wa masu da’awar maja a zaɓen 2027 tutsu ne? 

Ko Peter Obi na son yi wa masu da’awar maja a zaɓen 2027 tutsu ne? 

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja A daidai lokacin da wasu ke hanƙoron ganin jam'iyyun adawa a Nijeriya sun haɗe domin kafa jam'iyya mai ƙarfi da za ta ƙalubalanci jam'iyyar APC mai mulki a zaɓen shekarar 2027, da alama akwai jan aiki a gaba. ɗaya daga cikin waɗanda ake tunanin yana cikin na gaba-gaba wajen haɗakar, wato tsohon ɗan takarar shugaban ƙasa a Jam'iyyar Labour, Peter Obi, wanda ya zo na uku a zaɓen shugaban ƙasa da aka yi na 2023 ne ya fara nuna kamar zai yi tutsu, inda ya nesanta kansa daga duk wani yunƙurin da ake yi…
Read More
Dole mu ba matasa dama a siyasar 2027 – Bafarawa

Dole mu ba matasa dama a siyasar 2027 – Bafarawa

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja  Tsohon Gwamnan Jihar Sokoto Alhaji Attahiru Bafarawa, wanda a kwanakin baya ya bayyana ficewarsa daga jam'iyyar PDP, ya ce dole tsofaffin 'yan siyasa tsararrakinsa su kauce, su ba matasa wuri a siyasar 2027. A wata tattaunawa da ya yi da jaridar Blueprint, Bafarawa ya ce, "ba rikici nake yi da PDP ba. Mutane suna kuskuren tunanin dole ɗan siyasa ya nemi takarar zama zaɓaɓɓe, amma siyasa ta wuce haka, siyasa magana ce da hidimtawa al'umma. "Na yi kusan shekara 48 a siyasa, amma yanzu na kai shekara 70 a duniya. Aikin da ke gabana…
Read More
Salon mulki da tsare-tsaren Tinubu za su kai mu tudun mun tsira – Uba Sani

Salon mulki da tsare-tsaren Tinubu za su kai mu tudun mun tsira – Uba Sani

Daga SANI HAMAD GIWA a Abuja Gwamnan Kaduna, Uba Sani, ya ce, Shugaba Tinubu ya shirya tsaf domin sake fasalin Nijeriya da kuma ɗora ta kan gwadaben cigaba mai ɗorewa. Gwamnan ya ce, idan aka yi la’akari da manufofin shugaban ƙasa da ke cike da ƙarfin guiwa za a ga sun ɗan haifar da ƙalubale da tsanani, amma komai zai wuce, domin tsananin na ɗan wani lokaci ne. Gwamna Uba Sani ya yi waɗannan kalamai ne a yayin wani taron lakca na kwana ɗaya da Arewa Think Tank ta shirya a ranar Talata inda a cikin jawabinsa na maraba, yake…
Read More
Gwamnan Kaduna ya maida wani sarki da gwamnatin El-Rufa’i ta sauke

Gwamnan Kaduna ya maida wani sarki da gwamnatin El-Rufa’i ta sauke

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Gwamnan Jihar Kaduna, Sanata Uba Sani, ya mayar da Jonathan Paragua Zamuna, babban Sarkin Piriga da ke ƙaramar Hukumar Lere, bisa bin umarnin kotu. Jaridar Manhaja ta ruwaito cewa kotun masana'antu ta ƙasa da ke Kaduna ta soke tsige Cif Zamuna tare da tsige shi a ranar 14 ga watan Yuni 2024. Da yake magana da taron sarakunan gargajiya a ranar Alhamis, 5 ga watan Yuli, 2024, Gwamna Sani ya tabbatar da aniyarsa ta aiwatar da hukuncin da kotun ta yanke, wanda ya kawar da tsige shi. Nasir El-Rufai, wanda Uba Sani ya gada,…
Read More
Ayyukan raya jiha: Gwamnan Jihar Yobe, Mala Buni ya ciri tuta – Hon. Dala Buni

Ayyukan raya jiha: Gwamnan Jihar Yobe, Mala Buni ya ciri tuta – Hon. Dala Buni

Daga GAMBO ISA Shugaban ƙaramar Hukumar Gujba a Jihar Yobe, Honorabul Alhaji Dala Mala Buni ya yaba wa Gwamna Mai Mala Buni bisa ayyukan raya ƙasa a jihar. Dala ya bayyana haka ne a cikin makon nan yayin wata tattaunawa da wakilinmu a Abuja, inda ya zayyana wasu daga nasarorin da gwamnan ya samu a fannin jin daɗi da walwalar al'umma ta fuskar kayayyakin more rayuwa, noma, ilimi, kiwon lafiya, gina manyan kasuwanni na zamani da sauransu. Honorabul Dala Buni ya lissafo nasarorin da suka haɗa da, shirye-shiryen da suka shafi al'ummar jihar kaitsaye, kamar gina manyan kasuwannin zamani a…
Read More