Siyasa

Gwamnan Kaduna ya maida wani sarki da gwamnatin El-Rufa’i ta sauke

Gwamnan Kaduna ya maida wani sarki da gwamnatin El-Rufa’i ta sauke

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Gwamnan Jihar Kaduna, Sanata Uba Sani, ya mayar da Jonathan Paragua Zamuna, babban Sarkin Piriga da ke ƙaramar Hukumar Lere, bisa bin umarnin kotu. Jaridar Manhaja ta ruwaito cewa kotun masana'antu ta ƙasa da ke Kaduna ta soke tsige Cif Zamuna tare da tsige shi a ranar 14 ga watan Yuni 2024. Da yake magana da taron sarakunan gargajiya a ranar Alhamis, 5 ga watan Yuli, 2024, Gwamna Sani ya tabbatar da aniyarsa ta aiwatar da hukuncin da kotun ta yanke, wanda ya kawar da tsige shi. Nasir El-Rufai, wanda Uba Sani ya gada,…
Read More
Ayyukan raya jiha: Gwamnan Jihar Yobe, Mala Buni ya ciri tuta – Hon. Dala Buni

Ayyukan raya jiha: Gwamnan Jihar Yobe, Mala Buni ya ciri tuta – Hon. Dala Buni

Daga GAMBO ISA Shugaban ƙaramar Hukumar Gujba a Jihar Yobe, Honorabul Alhaji Dala Mala Buni ya yaba wa Gwamna Mai Mala Buni bisa ayyukan raya ƙasa a jihar. Dala ya bayyana haka ne a cikin makon nan yayin wata tattaunawa da wakilinmu a Abuja, inda ya zayyana wasu daga nasarorin da gwamnan ya samu a fannin jin daɗi da walwalar al'umma ta fuskar kayayyakin more rayuwa, noma, ilimi, kiwon lafiya, gina manyan kasuwanni na zamani da sauransu. Honorabul Dala Buni ya lissafo nasarorin da suka haɗa da, shirye-shiryen da suka shafi al'ummar jihar kaitsaye, kamar gina manyan kasuwannin zamani a…
Read More
Tsohon kwamishinan Gwamna Abba ya bar jam’iyyar NNPP

Tsohon kwamishinan Gwamna Abba ya bar jam’iyyar NNPP

Daga USMAN KAROFI Hon. Abbas, wanda ya riƙe muƙamin kwamishinan raya karkara da cigaban al’umma har zuwa watan da ya gabata, ya bayyana ficewarsa daga NNPP ne yayin ziyarar da ya kai gidan mataimakin shugaban majalisar dattawa, Sanata Barau Jibrin, a daren Juma’a. Wannan sauyin sheƙa na Hon. Abbas ya kasance ci gaba da “Barau Tsunami” da ake kira, wanda ya jawo ɗaruruwan shugabannin NNPP tare da dubban magoya bayansu sun sauya sheƙa zuwa APC. A cikin jawabinsa, Hon. Abbas ya bayyana cikakken goyon bayansa ga jam’iyyar APC tare da alƙawarin yin aiki don samun nasarar jam’iyyar a jihar Kano…
Read More
Dalilin da ya sa gwamnonin APC ba za su iya taimaka wa El-Rufa’i ba – Gwamna Sule

Dalilin da ya sa gwamnonin APC ba za su iya taimaka wa El-Rufa’i ba – Gwamna Sule

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Gwamnan Jihar Nasarawa, Abdullahi Sule, ya ce ƙungiyar Progressive Governors’ Forum (PGF) ba za ta iya taɓuka komai ba game da batun tantance tsohon gwamnan jihar Kaduna, Nasir El-Rufai a matsayin minista. Sule, wanda ɗan ƙungiyar gwamnonin jam’iyyar APC ne wato PGF, ya kuma ce El-Rufai bai bar jam’iyya mai mulki ba duk da ƙin amincewa da shi a matsayin wanda majalisar wakilai ta tsayar a matsayin minista a watan Agustan 2023. “El-Rufai bai bar jam’iyyar mu ba; har yanzu yana cikin jam’iyyarmu,” inji Sule a cikin shirin siyasar gidan Talabijin na Channels na…
Read More
Ya kamata APC ta nemi afuwa kan barazana ga rayuwar Obi – Atiku

Ya kamata APC ta nemi afuwa kan barazana ga rayuwar Obi – Atiku

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Tsohon ɗan takarar shugabancin Nijeriya a Jam'iyyar PDP, Atiku Abubakar ya soki jam'iyyar APC bisa kalaman da sakataren watsa labaranta na ƙasa, Feliɗ Morka ya yi game da bayanin sabuwar shekara na tsohon ɗantakarar jam'iyyar LP, Peter Obi, inda Obi ya ce kalaman tamkar barazana ce ga rayuwarsa. Atiku ya bayyana haka ne a shafukansa na sada zumunta, inda ya ce, "Wannan barazanar, da cigaba da riƙe ɗan gwagwarmaya Mahdi Shehu, abin takaici ne, kuma tamkar kama hanyar mulkin kama-karya ne, inda ake shaƙe 'yan hamayya." Ya ce kalaman sakataren watsa labaran na APC…
Read More
Rikicin siyasa tsakanin Kwankwaso, Shekarau da Ganduje na hana Kano cigaba – Garo

Rikicin siyasa tsakanin Kwankwaso, Shekarau da Ganduje na hana Kano cigaba – Garo

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Tsohon ɗan Takarar Mataimakin Gwamna na Jam’iyyar APC a 2023, Murtala Sule Garo, ya yi kira ga tsofaffin gwamnonin Jihar Kano, da su manta da banbance-banbancen siyasa su haɗa kai domin ci gaban jihar. Wannan na cikin wani bidiyo wanda ɗan siyasar ya yi kira ga tsofaffn gwamnoni da su haɗa kai don ciyar da jihar gaba. Garo ya nuna damuwa kan rashin jituwa tsakanin Rabiu Kwankwaso, Malam Ibrahim Shekarau, da Abdullahi Ganduje, wanda a cewarsa hakan na haifar da cikas ga ci gaban Kano. Ya ce, “Abin takaici ne ganin jihohi kamar Zamfara,…
Read More
Shugabannin Arewa na haifar da rabuwar kai wajen zaɓen ’yan takara – Kwankwaso

Shugabannin Arewa na haifar da rabuwar kai wajen zaɓen ’yan takara – Kwankwaso

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Jagoran ɗariƙar Kwankwasiyya, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso, ya yi kira ga shugabannin Arewa da su daina tsoma baki wajen zaɓen ’yan takarar shugaban ƙasa a Nijeriya. Kwankwaso ya ce shugabannin na amfani da sunan yankin wajen ƙirƙiro matsaloli kawai. Kwankwaso, ya bayyana cewa irin wannan tsoma bakin yana raba kan al’umma, kuma yana haifar da zaɓen shugabannin da ba su cancanta ba. Yayin wata hira da BBC, ya shawarci waɗannan shugabanni da su daina tursasa wa al’umma ra’ayinsu kuma su yi koyi da darusan da suka samu daga zaɓukan da suka gabata. “Irin wannan…
Read More
Ciyaman ɗin ƙaramar hukuma a Kano ya naɗa hadimai 60

Ciyaman ɗin ƙaramar hukuma a Kano ya naɗa hadimai 60

Daga IBRAHIM HAMISU a Kano Shugaban ƙaramar Hukumar Nasarawa a jihar Kano, Yusuf Imam, wanda aka fi sani da ‘Ogan ɓoye’ ya amince da naɗin mataimaka na musamman guda 60 da za su yi aiki a ɓangarori daban-daban a ƙaramar hukumar.   A cewar takardar amincewa da sakataren ƙaramar hukumar, Ado Muhd Hotoro ya sanya wa hannu, naɗin na ɗaya daga cikin ƙoƙarin da shugaban ƙaramar hukumar ya ke yi na bunƙasa da ayyuka don ci gaban ƙananan hukumomi. Jerin sunayen waɗanda aka naɗa sun haɗa da masu bayar da rahoto na musamman guda 18 da aka ba su don kula…
Read More
Yadda Saraki ya ci amanata a majalisa — Ndume

Yadda Saraki ya ci amanata a majalisa — Ndume

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja  Sanata Mohammed Ali Ndume, mai wakiltar Kudancin Borno, ya ce Tsohon Shugaban Majalisar Dattawa, Bukola Saraki, ya ci amanarsa duk da ƙoƙarin da ya yi na ganin ya zama shugaban majalisar. Da yake magana da sashen Hausa na Deutsche Welle (DW), Ndume, ya bayyana yadda tsohon Shugaban Majalisar Dattawa, Saraki, ya juya masa baya duk da goyon bayan da ya bashi wajen zama Shugaban Majalisar Dattawa ta 8. “An tsige daga matsayin Shugaban Majalisar Dattawa sannan aka dakatar da ni na tsawon wata takwas ba tare da albashi ba. “Wannan ya baƙanta min rai…
Read More
’Yan sanda sun kama ƙusa a NNPP bisa zargin sukar Gwamna Zulum

’Yan sanda sun kama ƙusa a NNPP bisa zargin sukar Gwamna Zulum

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Rundunar ‘Yan Sandan Jihar Borno ta kama wani jigo a jam’iyyar NNPP, Atom Magira, bisa zargin sukar Gwamna Babagana Zulum. Hadimin Mr. Magira, Mohammed Yahaya, ya bayyana cewa jami’an rundunar sun ɗauke shi ne a daren Lahadi. Manhaja ta rawaito cewa Magira, wanda ya taɓa neman takarar gwamna a ƙarƙashin jam’iyyar APC a zaɓen 2019, yana daga cikin manyan ‘yan adawa a jihar. Ya kasance mai magana sosai kan wasu manufofin Gwamna Babagana Zulum. Wasu majiyoyi sun shaida wa wakilinmu cewa an kama Mr. Magira ne saboda wani allon talla da magoya bayan “YES…
Read More