12
May
Daga JOHN D. WADA a Lafiya Gwamnan Jihar Nasarawa Injiniya Abdullahi Sule, ya ce da zarar ya kammala wa’adinsa na biyu a matsayin gwamnan jihar, ba zai sake fitowa takarar kujerar siyasa ba har ƙarshen rayuwarsa. Gwamnan ya sanar da haka ne a lokacin da yake karɓar baƙuncin ‘ya’yan ƙungiyar masu aiko da rahoto wato Correspondents Chapel a turance na ƙasa reshen jihar ta Nasarawa waɗanda suka kai masa ziyarar taya shi murnar bikin ƙaramar Sallah da aka gudanar kwanan nan a gidansa dake garin Gudi dake yankin Ƙaramar Hukumar Akwanga a jihar. Ya ce a yanzu Alhamdu lillah da…