Siyasa

Ba ni ba sake fitowa takara bayan na kammala wa’adina na biyu, inji Gwamna Abdullahi Sule

Ba ni ba sake fitowa takara bayan na kammala wa’adina na biyu, inji Gwamna Abdullahi Sule

Daga JOHN D. WADA a Lafiya Gwamnan Jihar Nasarawa Injiniya Abdullahi Sule, ya ce da zarar ya kammala wa’adinsa na biyu a matsayin gwamnan jihar, ba zai sake fitowa takarar kujerar siyasa ba har ƙarshen rayuwarsa. Gwamnan ya sanar da haka ne a lokacin da yake karɓar baƙuncin ‘ya’yan ƙungiyar masu aiko da rahoto wato Correspondents Chapel a turance na ƙasa reshen jihar ta Nasarawa waɗanda suka kai masa ziyarar taya shi murnar bikin ƙaramar Sallah da aka gudanar kwanan nan a gidansa dake garin Gudi dake yankin Ƙaramar Hukumar Akwanga a jihar. Ya ce a yanzu Alhamdu lillah da…
Read More
Sauraren Ƙararrakin Zaɓe: Atiku Abubakar ya halarci zaman kotu

Sauraren Ƙararrakin Zaɓe: Atiku Abubakar ya halarci zaman kotu

Ɗan takarar Shugaban Ƙasa ƙarƙashin Jam'iyyar PDP, Atiku Abubakar, ya halarci zaman shari'ar da Kotun Sauraren Ƙararrakin Zaɓe ki yi a Abuja a wannan Alhamis ɗin. Atiku ya halarci Kotun ne domin jin yadda za ta kaya kan ƙarar da ya shigar inda yake ƙalubalantar nasarar da ɗan takarar shugabancin ƙasa na Jam'iyyar APC, Bola Tinubu, ya samu a babban zaɓen da ya gudana. Tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasar shi ne ya zo na biyu a babban zaɓen da aka yi ran 25 ga Fabrairu, yayin da Peter Obi na Jam'iyyar Labour ya zo na uku. Atiku yana zargin an tafka…
Read More
Da Ɗumi-ɗumi: Kotun Ƙoli ta tabbatar da Adeleke a matsayin Gwamnan Osun

Da Ɗumi-ɗumi: Kotun Ƙoli ta tabbatar da Adeleke a matsayin Gwamnan Osun

Kotun Ƙoli ta yi watsi da ƙarar da Adegboyega Oyetola na Jam'iyyar APC ya ɗaukaka inda yake ƙalubalantar nasarar da Ademola Adeleke na Jam'iyyar PDP ya samu a matsayin Gwamnan Jihar Osun. Da yake karanto hukuncin yayin zaman kotun a ranar Talata, Mai Shari'a Emmanuel Agim ya tabbatar da hukuncin da Kotun Ɗaukaka Ƙara ta yanke na cewa Adeleke shi ne wanda ya yi nasara a zaɓen na Osun. Kotun Ƙolin ta ce mai ƙara ya gaza gabatar wa kotun gamsassun hujjoji kan zargin da ya yi cewa an zuba ƙuri'a wuce kima a zaɓen gwamnan jihar Osun da ya…
Read More
APC ta yi ra’ayin Akpabio da Barau su jaigoranci Majalisar Ƙasa

APC ta yi ra’ayin Akpabio da Barau su jaigoranci Majalisar Ƙasa

Kwamitin Gudanarwa na Ƙasa na Jam'iyyar APC (NWC) ya sannar da bin tsarin karɓa-karɓa dangane da shugabancin Majalisar Taraya zubi na 10. A cewar sanarwar da jam'iyyar ta fitar a ranar Litinin ta bakin Sakataren Yaɗa Labarai na Ƙasa, Felix Morka, tsarin karɓa-karɓar da jami'yyar ta shirya yin amfani da shi ya ƙunshi: Shugaban Majalisar Dattawa - Kudu maso Kudu - Sanata Godswill Akpabio (Akwa Ibom), Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa – Arewa maso Yamma - Sanata Barau Jubrin (Kano). Sauran su ne; Shugaban Majalisar Wakilai, Arewa maso Yamma – Hon. Abass Tajudeen (Kaduna), Mataimakin Shugaban Majalisar Wakilai Deputy Kudu maso…
Read More
Nasarar da Lawan Dare ya samu a Gwamnan Zamfara ba tirsasa wa al’umma aka yi ba – Mai-Nasiha

Nasarar da Lawan Dare ya samu a Gwamnan Zamfara ba tirsasa wa al’umma aka yi ba – Mai-Nasiha

Daga IBRAHIM MUHAMMAD a Kano An ƙalubalanci maganar da Gwamnan Jihar Zamfara ya yi na zargin cewa an yi amfani da wasu jami'an tsaro, sojoji da 'yan sanda sun tursasa wa mutane, su zaɓi Jam'iyyar PDP ba jam'iyyarsa ta APC ba, da cewa wannan magana da ya yi ba haka ba ne, kuma babu ƙamshin gaskiya a cikinta.  Jigo a Jam'iyyar PDP a Jihar Kano kuma masoyi, hadimi ga zaɓaɓɓen gwamnan jihar Zamfara Alhaji Dauda Lawan Dare, Malam Salmanu Mai Nasiha ne ya yi wannan ƙalubalen da yake mai da martani ga maganganun Gwamnan Zamfara Matawalle da ya ke zantawa…
Read More
‘Yan sanda sun cika hannu da korarren Kwamishinan Zaɓen Adamawa, Yunusa-Ari

‘Yan sanda sun cika hannu da korarren Kwamishinan Zaɓen Adamawa, Yunusa-Ari

'Yan sanda sun damƙe korarren Kwamishinan Zaɓe na Jihar Adamawa, Hudu Yunusa-Ari, kan abin da ya aikata yayain zaɓen gwamna a jihar. Kakakin 'yan sanda, Muyiwa Adejobi, ya bayyana a cikin sanarwar da ya fitar ranar Talata cewa, yanzu haka 'yan sanda na tsare da Yunusa-Ari. Sanarwar ta ce 'yan sanda sun cika hannu da Arin ne a Abuja, inda yake ci gaba da amsa tambaya kan dalilin da ya sa ya yi riga malam masallaci wajen bayyana sakamakon zaɓe alhali ana tsaka da tattara sakamakon zaɓen yayin zaɓen cike giɓi na gwamnan jihar da ya gudana kwanan baya. Ari…
Read More
Mun zo aikin ceto ne, cewar Zaɓaɓɓen Gwamnan Zamfara

Mun zo aikin ceto ne, cewar Zaɓaɓɓen Gwamnan Zamfara

Zaɓaɓɓen Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, a'ya ƙaddamar da kwamitin karɓar mulki a ranar Talata a Gusau, babban birnin jihar. Yayin ƙaddamar da kwamitin mai membobi 60, Dauda Lawal ya jaddada cewa ya zo aikin ceto ne tare da sake gina Jihar Zamfara. Sanarwar da ofishin zaɓaɓɓen gwamnan ya fitar mai ɗauke da sa hannun Sulaiman Bala Idris ta nunar cewa, an kafa kwamitin karɓar mulkin ne a ƙarƙashin jagorancin tsohon Sufeto Janar na ‘yan sanda, M.D Abubakar. Da yake jawabi a wajen ƙaddamar da kwamitin, mai girma Dauda Lawal, ya ce nauyin da ya rataya a kan kwamitin shi…
Read More
Ƙungiyoyi sun bayyana shiyyar da ya dace ta fitar da Shugaban Majalisar Dattawa

Ƙungiyoyi sun bayyana shiyyar da ya dace ta fitar da Shugaban Majalisar Dattawa

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Gamayyar ƙungiyoyin da ke sha'awar tsoma baqi a harkokin siyasa a arewa maso yamma, 'Rescue North West APC Group' ta ce, ta raba gardama kan kujerar Shugaban Majalisar Dattawa. An ruwaito gamayyar ƙungiyoyin na cewa shiyyar arewa maso yammacin Nijeriya ce ta cancanta ta samu kujerar shugaban majalisar dattawa ta 10 da za a kafa. A cewarsu, ya kamata a baiwa shiyyar wannan kujera saboda ta ba da gudummuwar tulin ƙuri'u, waɗanda suka taimaki Zaɓaɓɓen Shugaban Ƙasa, Bola Tinubu, ya kai ga nasara a zaɓen 2023. Bayan taron da ƙungiyoyin suka gudanar a jihohin Katsina, Kaduna,…
Read More
Tinubu, Shugaban APC na Ƙasa, Adamu da wasu sun yi ganawar sirri

Tinubu, Shugaban APC na Ƙasa, Adamu da wasu sun yi ganawar sirri

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Zaɓaɓɓen Shugaban Ƙasa, Sanata Bola Tinubu ya gana da Shugaban Jam’iyyar APC na Ƙasa, Sanata Abdullahi Adamu a gidan tsaro da ke Abuja. A wajen taron da aka gudanar a sirrance akwai Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Ahmad Lawan; Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Ovie Omo-Agege; Sakataren Yaɗa Labarai na Jam’iyyar APC na Ƙasa, Sanata Iyiola Omisore da tsohon Sakataren Kwamitin Yaƙin Neman Zaɓen Shugabancin Jam’iyyar APC, Hon James Faleke. A ƙarshen taron, Shugaban Jam’iyyar APC na Ƙasa ya ce taron wani aiki ne na yau da kullum. Ya ƙi bayyana batutuwan da aka tattauna…
Read More
Kansiloli sun tsige Mataimakin Shugaban Ƙaramar Hukuma a Katsina

Kansiloli sun tsige Mataimakin Shugaban Ƙaramar Hukuma a Katsina

Daga UMAR GARBA a Katsina Kansilolin Ƙaramar Hukumar Malumfashi guda 9 cikin 12 sun gudanar da wani zama na musamman tare da tsige Shugaban Majalisar, Hon. Abdullahi Rabi'u mai wakiltar mazaɓar Yaba da mataimakin shi, Hon Mustapha Ma'azu mai wakiltar mazaɓar Gorar-Dansaka. Haka zalika kamar yadda ɗaya daga cikin kansilolin ya shaida wa Blueprint Manhaja, kansiloli sun kuma tsige Mataimakin Shugaban Ƙaramar Hukumar ta Malumfashi, Hon Abdulrazak Tukur Maifada bisa zarge-zargen aikata ba daidai ba. Daga bisani kansilolin sun naɗa sababbin shuwagabannin kamar haka:- Hon. Salmanu Saminu a matsayin Shugaban Majalisar; Hon. Ibrahim Muhammed Rahimi (Yammama Ward) a matsayin Mataimakin…
Read More