29
Dec
Daga IBRAHIM MUHAMMAD a Kano An bayyana ɗaukar nauyin duba masu larurar idanu kyauta da ba su magani da shugaban ƙaramar hukumar Nasarawa ya yi da aka gudanar a Asibitin Gwagwarwa da cewa koyi ne da yake da Gwamnan jihar Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf na baza ayyuka a ko'ina. Alhaji Yahuza Adamu 'Yankaba shugaban jam'iyyar NNPP na ƙaramar hukumar Nasarawa ne ya bayyana hakan. Ya ƙara da cewa shi kuma shugaban ƙaramar hukumar Nasarawa Ogan ɓoye ya yi amfani da wannan dama ya na ɗaukar marasa lafiya da basu tallafi kamar yanzu yadda ya ɗauki masu larurar ciwon ido…
